< 2 Sama’ila 16 >
1 Sa’ad da Dawuda ya yi ɗan nesa da ƙwanƙolin, sai ga Ziba mai hidimar Mefiboshet, yana jira yă tarye shi. Yana da jerin jakuna da sirdi suna ɗauke da dunƙulen burodi ɗari biyu, da ƙosai busasshen inabi ɗari ɗaya, da kosan’ya’yan itace ɓaure guda ɗari, da salka ruwan inabi.
Quand David eut passé un peu au delà du sommet [de la montagne], voici Tsiba, serviteur de Méphiboseth, vint au devant de lui, avec deux ânes bâtés, sur lesquels il y avait deux cents pains, et cent paquets de raisins secs, et cent [autres paquets] de [fruits] d'Eté, et un baril de vin.
2 Sarki ya ce wa Ziba, “Me ya sa ka kawo waɗannan?” Ziba ya ce, “Jakuna domin iyalin gidan sarki su hau ne, burodi da’ya’yan itace domin mutane su ci, ruwan inabi kuma domin waɗanda suka gaji a hamada.”
Et le Roi dit à Tsiba: Que veux-tu faire de cela? Et Tsiba répondit: Les ânes sont pour la famille du Roi, afin qu'ils montent dessus; et le pain, et les autres fruits d'Eté à manger, sont pour les jeunes gens, et il y a du vin pour boire, afin que ceux qui se trouveront fatigués au désert, en boivent.
3 Sai sarki ya ce, “Ina jikar maigidanka?” Ziba ya ce, “Yana zaune a Urushalima gama yana tsammani cewa, ‘Yau gidan Isra’ila za su mayar mini da sarautar kakana.’”
Et le Roi lui dit: Mais où est le fils de ton Maître? Et Tsiba répondit au Roi: Voilà, il est demeuré à Jérusalem; car il a dit: Aujourd'hui la maison d'Israël me rendra le Royaume de mon père.
4 Sai sarki ya ce wa Ziba, “Duk abin da yake na Mefiboshet, ya zama naka.” Ziba ya rusuna ya ce, “Bari in dinga samun tagomashi a gabanka ranka yă daɗe.”
Alors le Roi dit à Tsiba: Voilà, tout ce qui est à Méphiboseth, [est à toi]. Et Tsiba dit: Je me prosterne devant toi, je trouve grâce devant toi, ô Roi mon Seigneur!
5 Yayinda Sarki Dawuda ya kusato Bahurim, sai ga wani mutumin dangin Shawulu ya fito daga can, sunansa Shimeyi ɗan Gera. Ya fito yana ta la’anta yayinda yake fitowa.
Et le Roi David vint jusqu'à Bahurim; et voici il sortit de là un homme de la famille de la maison de Saül, nommé Simhi fils de Guéra, qui étant sorti avec impétuosité, faisait des imprécations.
6 Ya jajjefi Dawuda da dukan fadawan sarki da duwatsu, ko da yake sojoji da masu gadin sarki na musamman suna kewaye da sarki dama da hagu.
Et jetait des pierres contre David, et contre tous les serviteurs du Roi David, et tout le peuple, et tous les hommes forts étaient à la droite et à la gauche du Roi.
7 Yayinda yake la’antar, Shimeyi ya ce, “Tafi daga nan, tafi daga nan, mai kisankai, mutumin banza kawai!
Or Simhi parlait ainsi en le maudissant: Sors, sors, homme de sang, et méchant homme.
8 Ubangiji ya kama ka saboda alhakin jinin gidan Shawulu, wanda kake sarauta a maimakonsa. Ubangiji ya ba da masarautar ga ɗanka Absalom. Hallaka ta zo maka domin kai mai kisankai ne!”
L'Eternel a fait retomber sur toi tout le sang de la maison de Saül, en la place duquel tu as régné, et l'Eternel a mis le royaume entre les mains de ton fils Absalom, et voilà, [tu souffres] le mal [que tu as fait], parce que tu es un homme de sang.
9 Sai Abishai ɗan Zeruhiya ya ce wa sarki, “Ranka yă daɗe, don me wannan mataccen kare yake la’antarka? Bari in je in datse kansa.”
Alors Abisaï, fils de Tséruja, dit au Roi: Comment ce chien mort maudit-il le Roi mon Seigneur? que je passe, je te prie, et que je lui ôte la tête.
10 Amma sarki ya ce, “Ba ruwana da ku, ku’ya’yan Zeruhiya. Idan yana la’ana ne domin Ubangiji ya ce masa, ‘La’anci Dawuda,’ wa zai ce, ‘Don me kake haka?’”
Mais le Roi répondit: Qu'ai-je à faire avec vous, fils de Tséruja? Qu'il [me] maudisse; car l'Eternel lui a dit: Maudis David; qui donc lui dira: Pourquoi l'as-tu fait?
11 Sa’an nan Dawuda ya ce wa Abishai da dukan fadawansa, “Ɗana, na cikina, yana ƙoƙari yă kashe ni. Balle wannan mutumin Benyamin! Ku ƙyale shi, yă yi ta zargi, Ubangiji ne ya ce masa yă yi haka.
David dit aussi à Abisaï, et à tous ses serviteurs: Voici, mon propre fils qui est sorti de mes entrailles, cherche ma vie, et combien plus maintenant un fils de Jémini? Laissez-le, et qu'il [me] maudisse; car l'Eternel le lui a dit.
12 Mai yiwuwa Ubangiji yă ga azabata, yă sāka mini da alheri saboda la’anar da nake sha a yau.”
Peut-être l'Eternel regardera mon affliction, l'Eternel me rendra le bien au lieu des malédictions que celui-ci me donne aujourd'hui.
13 Saboda haka Dawuda da mutanensa suka ci gaba da tafiyarsu yayinda Shimeyi yana tafiya ɗaura da shi a gefen tudu, yana zagi, yana jifansa da duwatsu, yana tayar masa da ƙura.
David donc avec ses gens continuait son chemin, et Simhi allait à côté de la montagne, vis-à-vis de lui, continuant à maudire, jetant des pierres contre lui, et de la poudre en l'air.
14 Sarki da dukan mutanen da suke tare da shi suka isa masauƙinsu a gajiye. A can fa ya huta.
Ainsi le Roi David, et tout le peuple qui était avec lui, étant fatigués, vinrent, et se rafraîchirent là.
15 Ana cikin haka, Absalom da dukan Isra’ila suka iso Urushalima, Ahitofel kuwa yana tare da shi.
Or Absalom et tout le peuple, [savoir] les hommes d'Israël, entrèrent dans Jérusalem; et Achithophel était avec lui.
16 Sai Hushai mutumin Arkitawa, abokin Dawuda ya je wurin Absalom ya ce masa, “Ran sarki yă daɗe! Ran sarki yă daɗe!”
Or il arriva que quand Cusaï Arkite, l'intime ami de David, fut venu vers Absalom, il dit à Absalom: Vive le Roi, vive le Roi.
17 Absalom ya ce wa Hushai, “Ƙaunar da kake nuna wa abokinka ke nan? Me ya sa ba ka tafi tare da abokinka ba?”
Et Absalom dit à Cusaï: Est-ce donc là l'affection que tu as pour ton intime ami? pourquoi n'es-tu point allé avec ton intime ami?
18 Hushai ya ce wa Absalom, “A’a, ai, wanda Ubangiji ya zaɓa ta wurin waɗannan mutane, da kuma ta wurin dukan mutane Isra’ila, shi zan zama nasa, zan kuma kasance tare da shi.
Mais Cusaï répondit à Absalom: Non; mais je serai à celui que l'Eternel a choisi, et que ce peuple, et tous les hommes d'Israël [ont aussi choisi], et je demeurerai avec lui.
19 Ban da haka ma, wane ne zan bauta wa? Ashe, ba ɗan ne zan bauta wa ba? Kamar dai yadda na bauta wa mahaifinka, haka zan bauta maka.”
Et de plus, qui servirai-je? ne sera-ce pas son fils? Je serai ton serviteur, comme j'ai été le serviteur de ton père.
20 Absalom ya ce wa Ahitofel, “Ba mu shawararka. Me za mu yi?”
Alors Absalom dit à Achithophel: Consultez ensemble [pour voir] ce que nous avons à faire.
21 Ahitofel ya ce wa Absalom, “Je ka kwana da ƙwarƙwaran mahaifinka waɗanda ya bari su lura da fada. Ta haka dukan Isra’ila za su ji cewa ka mai da kanka abin wari a hancin mahaifinka, dukan hannuwan waɗanda suke tare da kai kuwa za su sami ƙarfi.”
Et Achithophel dit à Absalom: Va vers les concubines de ton père, qu'il a laissées pour garder la maison, afin que quand tout Israël saura que tu te seras mis en mauvaise odeur auprès de ton père, les mains de tous ceux qui sont avec toi, soient fortifiées.
22 Saboda haka suka kafa wa Absalom tenti a bisa rufin ɗaki, a can ya kwana da ƙwarƙwaran mahaifinsa a gaban dukan Isra’ila.
On dressa donc un pavillon à Absalom sur le toit de la maison: et Absalom vint vers les concubines de son père, à la vue de tout Israël.
23 To, a kwanakin nan shawarar da Ahitofel yakan bayar takan zama kamar wadda aka nemi daga Allah ne. Haka Dawuda da Absalom duk suke ɗaukan dukan shawarar Ahitofel.
Or le conseil que donnait Achithophel en ce temps-là était autant estimé, que si quelqu'un eût demandé le conseil de Dieu. C'est ainsi qu'on considérait tous les conseils qu'Achithophel donnait, tant à David qu'à Absalom.