< 2 Sama’ila 15 >

1 Ana nan sai Absalom ya samo wa kansa wata keken yaƙi da dawakai tare da mutum hamsin da za su sha gabansa.
Bundan sonra Avşalom kendisine bir savaş arabası, atlar ve önünde koşacak elli kişi hazırladı.
2 Absalom yakan tashi da sassafe yă tsaya a gefen hanyar shigar ƙofar birni. Duk sa’ad da wani ya zo da ƙara don a kai gaban sarki yă yi shari’a, Absalom yakan kira shi yă ce, “Daga wane gari ka fito?” Sai mutumin yă amsa yă ce, “Bawanka ya fito a ɗaya daga cikin kabilan Isra’ila.”
Sabah erkenden kalkıp kent kapısına giden yolun kenarında dururdu. Davasına baktırmak için krala gelen herkese seslenip, “Nerelisin?” diye sorardı. Adam hangi İsrail oymağından geldiğini söylerdi.
3 Sai Absalom yă ce masa, “Ga shi, ƙararka daidai ne, tana kuma da gaskiya, sai dai ba wakilin sarkin da zai ji ka.”
Avşalom ona şöyle derdi: “Bak, ileri sürdüğün savlar doğru ve haklı. Ne var ki, kral adına seni dinleyecek kimse yok.”
4 Absalom kuwa yakan ƙara da cewa, “Da a ce an naɗa ni alƙali a ƙasar mana! Da duk mai ƙara, ko kuka wanda zai zo wurina, zan in tabbatar an yi masa adalci.”
Sonra konuşmasını şöyle sürdürürdü: “Keşke kral beni ülkeye yargıç atasa! Davası ya da sorunu olan herkes bana gelse, ben de ona hakkını versem!”
5 Kuma duk sa’ad da wani ya zo wurin Absalom ya rusuna don yă gaishe shi, sai Absalom yă sa hannunsa yă ta da shi, yă kuma rungume shi.
Biri önünde yüzüstü yere kapanmak üzere yaklaştı mı, Avşalom elini uzatıp adamı tutar, öperdi.
6 Absalom ya yi ta yin haka ga dukan Isra’ilawan da suka zo wurin sarki don neman adalci, ta haka kuwa ya saci zukatan mutanen Isra’ila.
Davasına baktırmak için krala gelen İsrailliler'in hepsine böyle davrandı. Böylelikle İsrailliler'in gönlünü çeldi.
7 A ƙarshen shekara huɗu, Absalom ya ce wa sarki, “Bari in tafi Hebron in cika alkawarin da na yi wa Ubangiji.
Dört yıl sonra Avşalom krala, “İzin ver de Hevron'a gidip RAB'be adağımı yerine getireyim” dedi,
8 Yayinda bawanka yake zama a Geshur, a Aram, na yi wannan alkawari, na ce, ‘In Ubangiji ya komo da ni Urushalima, zan yi wa Ubangiji sujada a Hebron.’”
“Çünkü ben kulun Aram'ın Geşur Kenti'nde yaşarken, ‘RAB beni Yeruşalim'e geri getirirse, O'na Hevron'da tapınacağım’ diye adak adamıştım.”
9 Sarki ya ce, “Ka sauka lafiya.” Sai ya tafi Hebron.
Kral, “Esenlikle git” dedi. Ne var ki, Hevron'a giden Avşalom bütün İsrail oymaklarına gizlice ulaklar göndererek şöyle dedi: “Boru sesini duyar duymaz, ‘Avşalom Hevron'da kral oldu’ diyeceksiniz.”
10 Sai Absalom ya aiki manzanni a asirce cikin dukan kabilan Isra’ila, ya ce musu su ce, “Da zarar kuka ji an busa ƙaho, sai ku ce, ‘Absalom sarki ne a Hebron.’”
11 Mutum ɗari biyu daga Urushalima suka raka Absalom. An gayyace su a matsayin baƙi, suka kuwa tafi cikin rashin sani, ba su san wani abu game da al’amarin ba.
Yeruşalim'den çağrılan iki yüz kişi olup bitenden haberleri olmaksızın, iyi niyetle Avşalom'la birlikte gittiler.
12 Yayinda Absalom yake miƙa hadaya, ya aika a kira Ahitofel mutumin Gilo, mai ba wa Dawuda shawara, yă zo daga Gilo garinsa. Ta haka makircin ya ƙara ƙarfi, masu bin Absalom kuma suka yi ta ƙaruwa.
Avşalom kurbanları keserken, Davut'un danışmanı Gilolu Ahitofel'i de Gilo Kenti'nden getirtti. Böylece ayaklanma güç kazandı. Çünkü Avşalom'u izleyen halkın sayısı giderek çoğalıyordu.
13 Wani manzo ya zo wurin Dawuda ya ce masa, “Zukatan mutanen Isra’ila sun koma wajen Absalom.”
Bir ulak gelip Davut'a, “İsrailliler Avşalom'a yürekten bağlandı” dedi.
14 Sai Dawuda ya ce wa dukan fadawansa da suke tare da shi a Urushalima, “Ku zo! Mu gudu, in ba haka ba, babu wanda zai tsira daga hannun Absalom. Dole mu bar nan, nan da nan, in ba haka ba zai tashi da sauri yă fāɗa mana, yă kuma hallaka garin da takobi.”
Bunun üzerine Davut Yeruşalim'de kendisiyle birlikte olan bütün görevlilerine şöyle dedi: “Haydi kaçalım! Yoksa Avşalom'dan kaçıp kurtulamayacağız. Hemen gidelim! Yoksa Avşalom ardımızdan çabucak yetişip bizi yıkıma uğratır. Kenti de kılıçtan geçirir.”
15 Sai fadawan sarki suka ce masa, “Barorinka suna a shirye su yi duk abin da ranka yă daɗe, ya zaɓa.”
Kralın görevlileri, “Efendimiz kral ne karar verirse yapmaya hazırız” diye yanıtladılar.
16 Sarki ya kama hanya, dukan gidansa kuwa suna biye da shi; amma ya bar ƙwarƙwarai goma su lura da fada.
Böylece kral ardısıra gelen bütün ev halkıyla birlikte yola koyuldu. Ancak saraya baksınlar diye on cariyesini orada bıraktı.
17 Ta haka sarki ya kama hanya da dukan mutane suna biye da shi, suka yi sansani a wani wuri mai ɗan nisa da Urushalima.
Kralla yanındakiler kentin en son evinde durdular.
18 Dukan mutanensa suka wuce gabansa, tare da dukan Keretawa da Feletiyawa; da dukan mutane ɗari shida na Gittiyawan da suka raka shi daga Gat, suka wuce gaban sarki.
Bütün kulları, Keretliler'le Peletliler kralın yanından geçtiler. Gat'tan ardısıra gelmiş olan altı yüz Gatlı asker de kralın önünden geçti.
19 Sarki ya ce wa Ittai mutumin Gat, “Don me za ka zo tare da mu? Ka koma ka zauna tare da Sarki Absalom. Kai baƙo ne, ɗan gudun hijira daga garinka.
Kral Gatlı İttay'a, “Neden sen de bizimle geliyorsun?” dedi, “Geri dön ve yeni kralla kal. Çünkü sen yurdundan sürülmüş bir yabancısın.
20 Jiya-jiya ka zo. Yau kuma in sa ka yi ta yawo tare da mu, ga shi ban ma san inda za ni ba? Koma, ka tafi da’yan’uwanka. Bari alheri da amincin Ubangiji su kasance tare da kai.”
Daha dün geldin. Bugün nereye gideceğimi kendim bilmezken, seni de bizimle birlikte mi dolaştırayım? Kardeşlerinle birlikte geri dön. Tanrı'nın sevgisi ve sadakati üzerinde olsun!”
21 Amma Ittai ya ce wa sarki, “Muddin Ubangiji yana a raye kuma muddin ranka yă daɗe yana a raye, duk inda ranka yă daɗe sarki zai kasance, ko a yi rai ko a mutu, a can bawanka zai kasance.”
Ama İttay şöyle yanıtladı: “Efendim kral, yaşayan RAB'bin adıyla ve yaşamın hakkı için derim ki, ister yaşam, ister ölüm için olsun, sen neredeysen kulun ben de orada olacağım.”
22 Dawuda ya ce wa Ittai, “Wuce gaba, taka mu je.” Sai Ittai mutumin Gat ya shiga layi tare da dukan mutanensa da iyalan da suke tare da shi.
Davut İttay'a, “Yürü, geç!” dedi. Böylece Gatlı İttay yanındaki bütün adamları ve çocuklarıyla birlikte geçti.
23 Dukan ƙauyuka suka yi ta kururuwa yayinda mutanen suke wucewa. Sarki shi ma ya haye ta Kwarin Kidron, mutane kuma suka ci gaba da tafiya zuwa wajen hamada.
Halk geçerken, bütün yöre halkı hıçkıra hıçkıra ağlıyordu. Kral Kidron Vadisi'ni geçti. Halk da kırlara doğru ilerledi.
24 Zadok yana nan tare da su, kuma dukan Lawiyawan da suke tare da shi kuwa suna ɗauke da akwatin alkawarin Allah. Suka sauke akwatin alkawarin Allah, Abiyatar ya miƙa hadaya sai da mutane suka gama fita daga birnin.
Kâhin Sadok'la Tanrı'nın Antlaşma Sandığı'nı taşıyan Levililer de oradaydı. Tanrı'nın Sandığı'nı yere koydular. Bütün halk kentten çıkana dek Aviyatar sunular sundu.
25 Sa’an nan sarki ya ce wa Zadok, “Ka komar da akwatin alkawarin Allah cikin birnin. Idan na sami tagomashi a idon Ubangiji, zai dawo da ni, yă kuma sa in sāke gan shi a mazauninsa.
Sonra kral, Sadok'a, “Tanrı'nın Sandığı'nı kente geri götür” dedi, “RAB benden hoşnut kalırsa, beni geri getirir, sandığı ve konduğu yeri bana gösterir.
26 Amma in ya ce, ‘Ina baƙin ciki da kai,’ to, ina a shirye; bari yă yi abin da ya fi masa.”
Ama, ‘Senden hoşnut değilim’ derse, işte buradayım, bana uygun gördüğünü yapsın.”
27 Sarki ya kuma ce wa Zadok firist, “Ashe, kai ba mai duba ba ne? Ka koma cikin birnin lafiya, tare da ɗanka Ahimawaz, da kuma Yonatan ɗan Abiyatar. Kai da Abiyatar ku tafi da’ya’yanku biyu.
Kral Kâhin Sadok'la konuşmasını şöyle sürdürdü: “Sen bilici değil misin? Oğlun Ahimaas'ı ve Aviyatar oğlu Yonatan'ı yanına al; Aviyatar'la birlikte esenlikle kente dönün.
28 Zan kuwa jira a mashigai a hamada, sai na ji daga gare ku.”
Sizden aydınlatıcı bir haber alana dek ben kırda, ırmağın sığ yerinde bekleyeceğim.”
29 Saboda haka Zadok da Abiyatar suka ɗauki akwatin alkawarin Allah suka komar da shi Urushalima, suka zauna a can.
Böylece Sadok'la Aviyatar Tanrı'nın Sandığı'nı Yeruşalim'e geri götürüp orada kaldılar.
30 Amma Dawuda ya ci gaba yana hawan Dutsen Zaitun, yana kuka yayinda yake tafiya; kansa a rufe, kuma babu takalma a ƙafafunsa. Dukan mutanen da suke tare da shi suka rufe kawunansu suna ta kuka yayinda suke haurawa.
Davut ağlaya ağlaya Zeytin Dağı'na çıkıyordu. Başı örtülüydü, yalınayak yürüyordu. Yanındaki herkesin başı örtülüydü ve ağlayarak dağa çıkıyorlardı.
31 To, an gaya wa Dawuda cewa, “Ahitofel yana cikin waɗanda suka hadasa maƙarƙashiya tare da Absalom.” Saboda haka Dawuda ya yi addu’a ya ce, “Ya Ubangiji ka mai da shawarar Ahitofel ta zama shiririta.”
O sırada biri Davut'a, “Ahitofel Avşalom'dan yana olan suikastçıların arasında” diye bildirdi. Bunun üzerine Davut, “Ya RAB, Ahitofel'in öğüdünü boşa çıkar” diye dua etti.
32 Da Dawuda ya isa ƙwanƙoli, inda mutane sun saba yi wa Allah sujada, Hushai, mutumin Arkitawa kuwa yana can don yă tarye shi, taguwarsa a yage, ga kuma ƙura a kansa.
Davut Tanrı'ya tapılan tepenin doruğuna varınca, Arklı Huşay giysisi yırtılmış, başı toz toprak içinde onu karşıladı.
33 Sai Dawuda ya ce masa, “In ka tafi tare da ni, za ka zama mini kaya.
Davut ona, “Benimle birlikte gelirsen, bana yük olursun” dedi,
34 Amma in ka koma birni, ka gaya wa Absalom, ‘Zan zama bawanka, ya sarki; dā ni bawan mahaifinka ne, amma yanzu zan zama bawanka,’ ta haka za ka watsar da shawarar Ahitofel.
“Ama kente döner ve Avşalom'a, ‘Ey kral, senin kulun olacağım; geçmişte babana nasıl kulluk ettiysem, şimdi de sana öyle kulluk edeceğim’ dersen, Ahitofel'in öğüdünü benim için boşa çıkarırsın.
35 Ba Zadok da Abiyatar firistocin nan suna nan tare da kai ba? Ka gaya musu duk abin da ka ji a fadan sarki.
Kâhin Sadok ile Kâhin Aviyatar orada seninle birlikte olacaklar. Kralın sarayında duyduğun her şeyi onlara bildir.
36 ’Ya’yansu biyu maza, Ahimawaz ɗan Zadok, da kuma Yonatan ɗan Abiyatar, suna can tare da su. Ka aike su wurina da duk abin da ka ji.”
Sadok oğlu Ahimaas ile Aviyatar oğlu Yonatan da oradalar. Bütün duyduklarınızı onların aracılığıyla bana iletebilirsiniz.”
37 Saboda haka Hushai abokin Dawuda ya isa Urushalima yayinda Absalom yake shigowa birnin.
Böylece Davut'un dostu Huşay Yeruşalim'e gitti. Tam o sırada Avşalom da kente giriyordu.

< 2 Sama’ila 15 >