< 2 Sama’ila 15 >

1 Ana nan sai Absalom ya samo wa kansa wata keken yaƙi da dawakai tare da mutum hamsin da za su sha gabansa.
Et il arriva, après cela, qu’Absalom se procura des chars et des chevaux, et 50 hommes qui couraient devant lui.
2 Absalom yakan tashi da sassafe yă tsaya a gefen hanyar shigar ƙofar birni. Duk sa’ad da wani ya zo da ƙara don a kai gaban sarki yă yi shari’a, Absalom yakan kira shi yă ce, “Daga wane gari ka fito?” Sai mutumin yă amsa yă ce, “Bawanka ya fito a ɗaya daga cikin kabilan Isra’ila.”
Et Absalom se levait de bonne heure, et se tenait à côté du chemin de la porte; et tout homme qui avait une cause qui l’oblige d’aller vers le roi pour un jugement, Absalom l’appelait, et disait: De quelle ville es-tu? Et il disait: Ton serviteur est de l’une des tribus d’Israël.
3 Sai Absalom yă ce masa, “Ga shi, ƙararka daidai ne, tana kuma da gaskiya, sai dai ba wakilin sarkin da zai ji ka.”
Et Absalom lui disait: Vois, tes affaires sont bonnes et justes, mais tu n’as personne pour les entendre de la part du roi.
4 Absalom kuwa yakan ƙara da cewa, “Da a ce an naɗa ni alƙali a ƙasar mana! Da duk mai ƙara, ko kuka wanda zai zo wurina, zan in tabbatar an yi masa adalci.”
Et Absalom disait: Que ne m’établit-on juge dans le pays! alors tout homme qui aurait une cause ou un procès viendrait vers moi, et je lui ferais justice.
5 Kuma duk sa’ad da wani ya zo wurin Absalom ya rusuna don yă gaishe shi, sai Absalom yă sa hannunsa yă ta da shi, yă kuma rungume shi.
Et s’il arrivait qu’un homme s’approche pour se prosterner devant lui, il lui tendait la main, et le prenait, et l’embrassait.
6 Absalom ya yi ta yin haka ga dukan Isra’ilawan da suka zo wurin sarki don neman adalci, ta haka kuwa ya saci zukatan mutanen Isra’ila.
Et Absalom agissait de cette manière envers tous ceux d’Israël qui venaient vers le roi pour un jugement; et Absalom dérobait les cœurs des hommes d’Israël.
7 A ƙarshen shekara huɗu, Absalom ya ce wa sarki, “Bari in tafi Hebron in cika alkawarin da na yi wa Ubangiji.
Et il arriva au bout de 40 ans, qu’Absalom dit au roi: Je te prie, que je m’en aille et que j’acquitte à Hébron mon vœu que j’ai voué à l’Éternel.
8 Yayinda bawanka yake zama a Geshur, a Aram, na yi wannan alkawari, na ce, ‘In Ubangiji ya komo da ni Urushalima, zan yi wa Ubangiji sujada a Hebron.’”
Car ton serviteur voua un vœu, quand je demeurais à Gueshur, en Syrie, disant: Si l’Éternel me fait retourner à Jérusalem, je servirai l’Éternel.
9 Sarki ya ce, “Ka sauka lafiya.” Sai ya tafi Hebron.
Et le roi lui dit: Va en paix. Et il se leva, et s’en alla à Hébron.
10 Sai Absalom ya aiki manzanni a asirce cikin dukan kabilan Isra’ila, ya ce musu su ce, “Da zarar kuka ji an busa ƙaho, sai ku ce, ‘Absalom sarki ne a Hebron.’”
Et Absalom envoya des émissaires dans toutes les tribus d’Israël, disant: Quand vous entendrez le son de la trompette, dites: Absalom règne à Hébron.
11 Mutum ɗari biyu daga Urushalima suka raka Absalom. An gayyace su a matsayin baƙi, suka kuwa tafi cikin rashin sani, ba su san wani abu game da al’amarin ba.
Et 200 hommes qui avaient été invités, s’en allèrent de Jérusalem avec Absalom, et ils allaient dans leur simplicité, et ne savaient rien de l’affaire.
12 Yayinda Absalom yake miƙa hadaya, ya aika a kira Ahitofel mutumin Gilo, mai ba wa Dawuda shawara, yă zo daga Gilo garinsa. Ta haka makircin ya ƙara ƙarfi, masu bin Absalom kuma suka yi ta ƙaruwa.
Et Absalom envoya [appeler] Akhitophel, le Guilonite, le conseiller de David, de sa ville de Guilo, pendant qu’il offrait les sacrifices; et la conjuration devint puissante, et le peuple allait croissant auprès d’Absalom.
13 Wani manzo ya zo wurin Dawuda ya ce masa, “Zukatan mutanen Isra’ila sun koma wajen Absalom.”
Et il vint à David quelqu’un qui lui rapporta, disant: Les cœurs des hommes d’Israël suivent Absalom.
14 Sai Dawuda ya ce wa dukan fadawansa da suke tare da shi a Urushalima, “Ku zo! Mu gudu, in ba haka ba, babu wanda zai tsira daga hannun Absalom. Dole mu bar nan, nan da nan, in ba haka ba zai tashi da sauri yă fāɗa mana, yă kuma hallaka garin da takobi.”
Et David dit à tous ses serviteurs qui étaient avec lui à Jérusalem: Levez-vous, et fuyons, car nous ne saurions échapper devant Absalom. Hâtez-vous de vous en aller, de peur qu’il ne se hâte, et ne nous atteigne, et ne fasse tomber le malheur sur nous, et ne frappe la ville par le tranchant de l’épée.
15 Sai fadawan sarki suka ce masa, “Barorinka suna a shirye su yi duk abin da ranka yă daɗe, ya zaɓa.”
Et les serviteurs du roi dirent au roi: Selon tout ce que choisira le roi, notre seigneur, voici tes serviteurs.
16 Sarki ya kama hanya, dukan gidansa kuwa suna biye da shi; amma ya bar ƙwarƙwarai goma su lura da fada.
Et le roi sortit, et toute sa maison à sa suite; et le roi laissa dix femmes concubines pour garder la maison.
17 Ta haka sarki ya kama hanya da dukan mutane suna biye da shi, suka yi sansani a wani wuri mai ɗan nisa da Urushalima.
Et le roi sortit, et tout le peuple à sa suite; et ils s’arrêtèrent à Beth-Merkhak.
18 Dukan mutanensa suka wuce gabansa, tare da dukan Keretawa da Feletiyawa; da dukan mutane ɗari shida na Gittiyawan da suka raka shi daga Gat, suka wuce gaban sarki.
Et tous ses serviteurs marchaient à ses côtés; et tous les Keréthiens, et tous les Peléthiens, et tous les Guitthiens, 600 hommes qui étaient venus de Gath à sa suite, marchaient devant le roi.
19 Sarki ya ce wa Ittai mutumin Gat, “Don me za ka zo tare da mu? Ka koma ka zauna tare da Sarki Absalom. Kai baƙo ne, ɗan gudun hijira daga garinka.
Et le roi dit à Itthaï, le Guitthien: Pourquoi viendrais-tu, toi aussi, avec nous? Retourne-t’en, et demeure avec le roi; car tu es étranger, et de plus tu as émigré dans le lieu que tu habites.
20 Jiya-jiya ka zo. Yau kuma in sa ka yi ta yawo tare da mu, ga shi ban ma san inda za ni ba? Koma, ka tafi da’yan’uwanka. Bari alheri da amincin Ubangiji su kasance tare da kai.”
Tu es venu hier, et aujourd’hui je te ferais errer avec nous çà et là? Et quant à moi, je vais où je puis aller. Retourne-t’en, et emmène tes frères. Que la bonté et la vérité soient avec toi!
21 Amma Ittai ya ce wa sarki, “Muddin Ubangiji yana a raye kuma muddin ranka yă daɗe yana a raye, duk inda ranka yă daɗe sarki zai kasance, ko a yi rai ko a mutu, a can bawanka zai kasance.”
Mais Itthaï répondit au roi, et dit: L’Éternel est vivant, et le roi, mon seigneur, est vivant, que dans le lieu où sera le roi, mon seigneur, soit pour la mort, soit pour la vie, là aussi sera ton serviteur!
22 Dawuda ya ce wa Ittai, “Wuce gaba, taka mu je.” Sai Ittai mutumin Gat ya shiga layi tare da dukan mutanensa da iyalan da suke tare da shi.
Et David dit à Itthaï: Va, et passe! Alors Itthaï, le Guitthien, passa avec tous ses hommes et tous les enfants qui étaient avec lui.
23 Dukan ƙauyuka suka yi ta kururuwa yayinda mutanen suke wucewa. Sarki shi ma ya haye ta Kwarin Kidron, mutane kuma suka ci gaba da tafiya zuwa wajen hamada.
Et tout le pays pleurait à haute voix, et tout le peuple passait; et le roi passa le torrent du Cédron, et tout le peuple passa en face du chemin du désert.
24 Zadok yana nan tare da su, kuma dukan Lawiyawan da suke tare da shi kuwa suna ɗauke da akwatin alkawarin Allah. Suka sauke akwatin alkawarin Allah, Abiyatar ya miƙa hadaya sai da mutane suka gama fita daga birnin.
Et voici Tsadok aussi, et tous les Lévites avec lui, portant l’arche de l’alliance de Dieu, et ils posèrent l’arche de Dieu, et Abiathar monta, jusqu’à ce que tout le peuple ait achevé de passer hors de la ville.
25 Sa’an nan sarki ya ce wa Zadok, “Ka komar da akwatin alkawarin Allah cikin birnin. Idan na sami tagomashi a idon Ubangiji, zai dawo da ni, yă kuma sa in sāke gan shi a mazauninsa.
Et le roi dit à Tsadok: Reporte l’arche de Dieu dans la ville; si je trouve grâce aux yeux de l’Éternel, alors il me ramènera, et me la fera voir, elle et sa demeure.
26 Amma in ya ce, ‘Ina baƙin ciki da kai,’ to, ina a shirye; bari yă yi abin da ya fi masa.”
Et s’il dit ainsi: Je ne prends point de plaisir en toi; – me voici, qu’il fasse de moi ce qui sera bon à ses yeux.
27 Sarki ya kuma ce wa Zadok firist, “Ashe, kai ba mai duba ba ne? Ka koma cikin birnin lafiya, tare da ɗanka Ahimawaz, da kuma Yonatan ɗan Abiyatar. Kai da Abiyatar ku tafi da’ya’yanku biyu.
Et le roi dit à Tsadok, le sacrificateur: N’es-tu pas le voyant? Retourne-t’en en paix à la ville, et Akhimaats, ton fils, et Jonathan, fils d’Abiathar, vos deux fils, avec vous.
28 Zan kuwa jira a mashigai a hamada, sai na ji daga gare ku.”
Voyez, j’attendrai dans les plaines du désert, jusqu’à ce que vienne de votre part une parole pour m’apporter des nouvelles.
29 Saboda haka Zadok da Abiyatar suka ɗauki akwatin alkawarin Allah suka komar da shi Urushalima, suka zauna a can.
Et Tsadok et Abiathar reportèrent l’arche de Dieu à Jérusalem, et y demeurèrent.
30 Amma Dawuda ya ci gaba yana hawan Dutsen Zaitun, yana kuka yayinda yake tafiya; kansa a rufe, kuma babu takalma a ƙafafunsa. Dukan mutanen da suke tare da shi suka rufe kawunansu suna ta kuka yayinda suke haurawa.
Et David monta par la montée des Oliviers, montant et pleurant; et il avait la tête couverte et marchait nu-pieds, et tout le peuple qui était avec lui montait, chacun ayant sa tête couverte, et en montant ils pleuraient.
31 To, an gaya wa Dawuda cewa, “Ahitofel yana cikin waɗanda suka hadasa maƙarƙashiya tare da Absalom.” Saboda haka Dawuda ya yi addu’a ya ce, “Ya Ubangiji ka mai da shawarar Ahitofel ta zama shiririta.”
Et on rapporta à David, en disant: Akhitophel est parmi les conjurés avec Absalom. Et David dit: Éternel! je te prie, rends vain le conseil d’Akhitophel.
32 Da Dawuda ya isa ƙwanƙoli, inda mutane sun saba yi wa Allah sujada, Hushai, mutumin Arkitawa kuwa yana can don yă tarye shi, taguwarsa a yage, ga kuma ƙura a kansa.
Et David, étant parvenu au sommet où il se prosterna devant Dieu, il arriva que voici, Hushaï, l’Arkite, vint au-devant de lui, sa tunique déchirée et de la terre sur sa tête.
33 Sai Dawuda ya ce masa, “In ka tafi tare da ni, za ka zama mini kaya.
Et David lui dit: Si tu passes avec moi, tu me seras à charge.
34 Amma in ka koma birni, ka gaya wa Absalom, ‘Zan zama bawanka, ya sarki; dā ni bawan mahaifinka ne, amma yanzu zan zama bawanka,’ ta haka za ka watsar da shawarar Ahitofel.
Mais si tu retournes à la ville, et que tu dises à Absalom: Ô roi! je serai ton serviteur; comme j’ai été autrefois serviteur de ton père, maintenant aussi je serai ton serviteur, – alors tu annuleras pour moi le conseil d’Akhitophel.
35 Ba Zadok da Abiyatar firistocin nan suna nan tare da kai ba? Ka gaya musu duk abin da ka ji a fadan sarki.
Et les sacrificateurs Tsadok et Abiathar ne sont-ils pas là avec toi? Et il arrivera que tout ce que tu entendras de la maison du roi, tu le rapporteras à Tsadok et à Abiathar, les sacrificateurs.
36 ’Ya’yansu biyu maza, Ahimawaz ɗan Zadok, da kuma Yonatan ɗan Abiyatar, suna can tare da su. Ka aike su wurina da duk abin da ka ji.”
Voici, leurs deux fils, Akhimaats, [fils] de Tsadok, et Jonathan, [fils] d’Abiathar, sont là avec eux; et vous me ferez savoir par eux tout ce que vous aurez entendu.
37 Saboda haka Hushai abokin Dawuda ya isa Urushalima yayinda Absalom yake shigowa birnin.
Et Hushaï, l’ami de David, vint dans la ville; et Absalom entra à Jérusalem.

< 2 Sama’ila 15 >