< 2 Sama’ila 12 >

1 Ubangiji ya aiki Natan wurin Dawuda. Da ya tafi wajensa, sai ya ce, “An yi waɗansu mutum biyu a wani gari, ɗaya mai arziki, ɗayan kuma matalauci.
Et l'Éternel envoya Nathan vers David; et il vint à lui et lui dit: Il y avait deux hommes dans une ville, l'un riche et l'autre pauvre.
2 Mai arzikin yana da babban garken tumaki, da kuma shanu,
Le riche avait du gros et du menu bétail en fort grande abondance.
3 amma matalauci ba shi da kome sai’yar tunkiyar da ya sayo. Ya yi kiwonta, ta kuwa yi girma tare shi da yaransa. Takan ci tare da shi ta sha ruwa a kwaf nasa, har ma ta kwanta a ƙirjinsa. Ta ma zama kamar’ya a gare shi.
Mais le pauvre n'avait rien du tout, qu'une petite brebis qu'il avait achetée et nourrie, et qui avait grandi chez lui et avec ses enfants, mangeant de ses morceaux, buvant de sa coupe et dormant dans son sein; et elle était comme sa fille.
4 “To, sai ga wani baƙo ya zo wurin mai arzikin nan, amma mai arzikin ya ƙi yă kama tunkiyarsa, ko saniyarsa yă yanka don yă shirya wa baƙon da ya zo abinci. A maimako, sai ya je ya kama’yar tunkiyan nan ta matalaucin ya yanka ya shirya wa mutumin da ya zo masa.”
Mais un voyageur étant venu chez cet homme riche, il a épargné son gros et son menu bétail, et n'en a point apprêté au passant qui était venu chez lui; mais il a pris la brebis de l'homme pauvre, et l'a apprêtée pour l'homme qui était venu chez lui.
5 Dawuda ya husata ƙwarai da mutumin, ya ce wa Natan, “Muddin Ubangiji yana a raye, mutumin da ya yi wannan ya cancanci yă mutu!
Alors la colère de David s'embrasa fort contre cet homme; et il dit à Nathan: L'Éternel est vivant! l'homme qui a fait cela est digne de mort.
6 Dole yă biya diyyar tunkiyan nan sau huɗu, domin ya aikata haka ba tausayi.”
Et pour cette brebis il en rendra quatre, puisqu'il a fait cela et qu'il a été sans pitié.
7 Sai Natan ya ce wa Dawuda, “Kai ne mutumin! Ga abin da Ubangiji, Allah ya ce, ‘Na naɗa ka sarki bisa Isra’ila, na kuma cece ka daga hannun Shawulu.
Alors Nathan dit à David: Tu es cet homme-là! Ainsi dit l'Éternel, le Dieu d'Israël: Je t'ai oint pour roi sur Israël, et je t'ai délivré de la main de Saül;
8 Na ba ka gidan maigidanka, da matan maigidanka duka. Na ba ka gidan Isra’ila da Yahuda. Da a ce dukan waɗannan sun kāsa maka, ai, da na ƙara maka.
Je t'ai même donné la maison de ton seigneur, et les femmes de ton seigneur dans ton sein, et je t'ai donné la maison d'Israël et de Juda, et si c'était peu, je t'eusse ajouté telle et telle chose.
9 Me ya sa ka rena maganar Ubangiji ta wurin yin mugunta haka a idonsa? Ka kashe Uriya mutumin Hitti da takobi, ka kuma ɗauki matarsa tă zama matarka. Ka kashe shi da takobin Ammonawa.
Pourquoi donc as-tu méprisé la parole de l'Éternel, en faisant ce qui lui déplaît? Tu as frappé de l'épée Urie, le Héthien; tu as pris sa femme pour en faire ta femme, et lui, tu l'as tué par l'épée des enfants d'Ammon.
10 To, fa, takobi ba zai taɓa rabu da gidanka ba, domin ka rena ni, ka kuma ƙwace matar Uriya mutumin Hitti ta zama matarka.’
Et maintenant, l'épée ne s'éloignera jamais de ta maison, parce que tu m'as méprisé, et que tu as enlevé la femme d'Urie, le Héthien, afin qu'elle fût ta femme.
11 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Daga cikin iyalinka zan kawo masifa a kanka. A idanunka zan ɗauki matanka in ba wa wani da yake kusa da kai, zai kuwa kwana da su da rana tsaka.
Ainsi dit l'Éternel: Voici, je vais faire sortir de ta propre maison le malheur contre toi; je prendrai tes femmes sous tes yeux, et je les donnerai à un de tes proches, et il couchera avec tes femmes, à la vue de ce soleil.
12 Ka aikata wannan a ɓoye, amma zan aikata wannan da rana tsaka, a gaban dukan Isra’ila.’”
Car tu l'as fait en secret; mais moi je le ferai en présence de tout Israël et à la face du soleil.
13 Sai Dawuda ya ce wa Natan, “Na yi wa Ubangiji zunubi.” Natan ya ce, “Ubangiji ya yafe maka zunubin. Ba za ka mutu ba.
Alors David dit à Nathan: J'ai péché contre l'Éternel! Et Nathan dit à David: Aussi l'Éternel a fait passer ton péché; tu ne mourras point;
14 Amma saboda ka yi haka ka sa abokan gāba suka rena Ubangiji, yaron da aka haifa maka zai mutu.”
Toutefois, parce qu'en cela tu as donné occasion aux ennemis de l'Éternel de blasphémer, le fils qui t'est né mourra certainement.
15 Bayan Natan ya tafi gida, sai Ubangiji ya bugi yaron da matar Uriya ta haifa wa Dawuda, ya kuwa kamu da ciwo.
Et Nathan retourna dans sa maison. Et l'Éternel frappa l'enfant que la femme d'Urie avait enfanté à David, et il devint fort malade;
16 Dawuda ya roƙi Allah saboda yaron. Ya yi azumi, ya kuma shiga gidansa ya kwana kwance a ƙasa.
Et David pria Dieu pour l'enfant, et David jeûna; puis il rentra et passa la nuit couché sur la terre.
17 Dattawan iyalinsa suka tsaya kusa da shi don su ɗaga shi daga ƙasa, amma ya ƙi, bai kuwa ci wani abu tare da su ba.
Et les anciens de sa maison se levèrent et vinrent vers lui pour le faire lever de terre; mais il ne le voulut point, et ne mangea point avec eux.
18 A rana ta bakwai sai yaron ya rasu. Barorin Dawuda suka ji tsoro su gaya masa cewa yaron ya mutu, gama sun yi tunani cewa, “Yayinda yaron yake da rai, mun yi magana da Dawuda bai ji mu ba. Yaya za mu gaya masa yaron ya mutu? Ai, zai yi wa kansa ɓarna.”
Et le septième jour l'enfant mourut, et les serviteurs de David craignaient de lui faire savoir que l'enfant était mort; car ils disaient: Quand l'enfant était en vie, nous lui avons parlé, et il n'a point écouté notre voix; comment donc lui dirions-nous que l'enfant est mort? Il ferait bien pis encore.
19 Dawuda ya gane bayinsa suna wa juna raɗan wani abu, sai ya gane yaron ya mutu. Sai ya ce, “Yaron ya rasu ko?” Suka ce, “I, ya rasu.”
Mais David aperçut que ses serviteurs parlaient tout bas, et il comprit que l'enfant était mort; et David dit à ses serviteurs: L'enfant est-il mort? Ils répondirent: Il est mort.
20 Sa’an nan Dawuda ya tashi daga ƙasa. Bayan ya yi wanka, ya shafa mai, ya kuma canja rigunarsa, sa’an nan ya shiga gidan Ubangiji ya yi sujada. Sai ya tafi gidansa, ya nemi a ba shi abinci, aka ba shi, ya kuwa ci.
Alors David se leva de terre, se lava, s'oignit, et changea de vêtements; et il entra dans la maison de l'Éternel, et se prosterna. Puis il revint dans sa maison; il demanda de la nourriture qu'on lui présenta, et il mangea.
21 Barorinsa suka ce masa, “Me ya sa kake yin haka? Yayinda yaron yake da rai, ka yi azumi, ka kuma yi kuka, amma yanzu da yaron ya mutu, ka tashi, ka kuma ci abinci!”
Et ses serviteurs lui dirent: Qu'est-ce donc que tu fais? Tu as jeûné et pleuré pour l'enfant, lorsqu'il était encore en vie; et quand l'enfant est mort, tu te lèves, et tu prends de la nourriture?
22 Ya ce musu, “Yayinda yaron yake da rai, na yi azumi, na kuma yi kuka. Na yi tunani na ce, ‘Wa ya sani? Ko Ubangiji zai yi mini alheri yă bar yaron yă rayu.’
Mais il dit: Quand l'enfant était encore en vie, j'ai jeûné et j'ai pleuré; car je disais: Qui sait si l'Éternel n'aura point pitié de moi, et si l'enfant ne vivra point?
23 Amma yanzu da ya mutu, me zai sa in yi azumi? Zan iya dawo da shi ne? Ni zan je wajensa, ba shi zai dawo wurina ba.”
Mais maintenant qu'il est mort, pourquoi jeûnerais-je? Pourrais-je le faire revenir? Je m'en irai vers lui, mais lui ne reviendra pas vers moi.
24 Sai Dawuda ya yi wa matarsa Batsheba ta’aziyya, ya kuma tafi wurinta ya kwana da ita. Ta kuma haifi ɗa, suka ba shi suna Solomon. Ubangiji ya ƙaunace shi;
Et David consola sa femme Bath-Shéba; et il vint vers elle, et coucha avec elle; et elle enfanta un fils qu'il nomma Salomon.
25 kuma saboda Ubangiji ya ƙaunace shi, sai ya aika da saƙo ta wurin annabi Natan yă ba shi suna Yedidiya.
Et l'Éternel l'aima; et il envoya Nathan, le prophète, qui lui donna le nom de Jédidia (aimé de l'Éternel), à cause de l'Éternel.
26 Ana cikin haka, sai Yowab ya yi yaƙi da Rabba na Ammonawa, ya kuma ƙwace babban birnin.
Or Joab faisait la guerre contre Rabba des enfants d'Ammon, et il prit la ville royale.
27 Sa’an nan Yowab ya aika manzanni wurin Dawuda yana cewa, “Na yaƙi Rabba na kuma ƙwace hanyar samun ruwanta.
Alors Joab envoya des messagers vers David, pour lui dire: J'ai attaqué Rabba, et même j'ai pris la ville des eaux.
28 Yanzu fa ka tattara saura rundunoni ka fāɗa wa birnin ka ci shi. In ba haka ba zan karɓe birnin, a kuma kira shi da sunana.”
Maintenant donc assemble le reste du peuple, et campe contre la ville et prends-la, de peur que je ne prenne la ville et qu'on ne l'appelle de mon nom.
29 Saboda haka Dawuda ya tattara sauran rundunar sojojin suka tafi Rabba suka fāɗa masa suka kuma ci shi.
David assembla donc tout le peuple; il marcha contre Rabba, combattit contre elle et la prit.
30 Ya ɗauke rawanin daga kan sarkinsu, nauyinsa ya kai talenti, na zinariya, an kuma yi masa ado da duwatsu masu daraja, aka aza shi a kan Dawuda. Ya kuma kwashe ganima mai yawa daga garin.
Et il enleva la couronne de leur roi de dessus sa tête; elle était d'or avec des pierres précieuses, et pesait un talent; et on la mit sur la tête de David. Il emmena aussi de la ville un fort grand butin.
31 Ya fito da mutanen da suke a can, ya sa su su yi aiki da zarto, da diga, da kuma gatari, ya kuma sa su bugan bulok. Haka ya yi wa dukan garuruwan Ammonawa. Sa’an nan Dawuda da dukan sojoji suka koma Urushalima.
Et il fit sortir le peuple qui y était, et le mit sous des scies, sous des herses de fer et sous des haches de fer, et les fit passer par un four à briques; il en fit ainsi à toutes les villes des enfants d'Ammon. Puis David s'en retourna à Jérusalem avec tout le peuple.

< 2 Sama’ila 12 >