< 2 Sarakuna 9 >
1 Sai Elisha ya kira wani daga cikin ƙungiyar annabawa, ya ce masa, “Ka sha ɗamara, ka ɗauki wannan kwalabar mai ka je Ramot Gileyad.
Then Elisha the Prophet called one of ye children of the Prophets, and sayde vnto him, Gird thy loynes and take this boxe of oyle in thine hand and get thee to Ramoth Gilead.
2 Da ka isa can, ka nemi Yehu ɗan Yehoshafat, ɗan Nimshi. Ka je wurinsa, ka ja shi gefe daga abokansa, ka shiga da shi ɗaki na ciki.
And when thou commest thither, looke where is Iehu ye sonne of Iehoshaphat, the sonne of Nimshi, and go, and make him arise vp from among his brethren, and leade him to a secret chamber.
3 Sa’an nan ka ɗauki kwalabar man ka zuba a kansa, ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa, na naɗa ka sarkin Isra’ila.’ Sa’an nan ka buɗe ƙofa ka ruga a guje; kada ka ɓata lokaci!”
Then take the boxe of oyle and powre it on his head, and say, Thus sayth the Lord, I haue anointed thee for King ouer Israel. then open the doore, and flee without any tarying.
4 Sai saurayin nan, annabi, ya tafi Ramot Gileyad.
So the seruat of ye Prophet gate him to Ramoth Gilead.
5 Da ya isa can, sai ya tarar da hafsoshin soji zaune a wuri guda. Sai ya ce, “Ina da saƙo dominka komanda.” Sai Yehu ya ce, “Wanne a cikinmu?” Sai ce, “Dominka, komanda.”
And when he came in, behold, the captaines of the armie were sitting. And he sayde, I haue a message to thee, O captaine. And Iehu sayd, Vnto which of all vs? And he answered, To thee, O captaine.
6 Sai Yehu ya tashi ya shiga cikin gida. Sa’an nan annabin ya zuba wa Yehu mai a kā, ya ce, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na naɗa ka sarki a bisa jama’ar Ubangiji, wato, Isra’ila.
And he arose, and went into the house, and he powred the oyle on his head and sayde vnto him, Thus sayth the Lord God of Israel, I haue anointed thee for King ouer the people of the Lord, euen ouer Israel.
7 Za aka hallaka gidan Ahab maigidanka, zan kuma ɗauki fansar jinin bayina annabawa da kuma jinin dukan bayin Ubangiji da Yezebel ta zub da.
And thou shalt smite the house of Ahab thy master, that I may auenge the blood of my seruants the Prophets, and the blood of al the seruants of the Lord of the hand of Iezebel.
8 Dukan gidan Ahab zai hallaka. Zan kashe dukan’ya’yan Ahab maza a Isra’ila, bayi ko’yantattu.
For the whole house of Ahab shalbe destroied: and I will cut off from Ahab, him that maketh water against the wall, as well him that is shut vp, as him that is left in Israel.
9 Zan mai da gidan Ahab kamar gidan Yerobowam ɗan Nebat da kuma kamar gidan Ba’asha ɗan Ahiya.
And I will make the house of Ahab like the house of Ieroboam the sonne of Nebat, and like the house of Baasha the sonne of Ahiiah.
10 Game da Yezebel kuwa, karnuka za su cinye ta a fili a Yezireyel, ba kuwa wanda zai binne ta.’” Sa’an nan ya buɗe ƙofa ya ruga a guje.
And the dogges shall eate Iezebel in the fielde of Izreel, and there shalbe none to burie her. And he opened the doore, and fled.
11 Da Yehu ya koma wurin sauran hafsoshin sai ɗaya daga cikinsu ya tambaye shi, “Lafiya? Me ya kawo wannan mahaukaci a wurinka?” Sai Yehu ya ce, “Ka san mahaukacin nan da irin maganganunsa.”
Then Iehu came out to the seruants of his lord. And one sayd vnto him, Is all well? wherefore came this mad fellowe to thee? And hee sayde vnto them, Ye knowe the man, and what his talke was.
12 Suka ce masa, “Ba gaskiya ba ne, ka dai faɗa mana.” Yehu ya ce, “Ga abin da ya ce mini, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, na naɗa ka sarki a bisa Isra’ila.’”
And they sayde, It is false, tell vs it nowe. Then he sayd, Thus and thus spake he to me, saying, Thus saieth the Lord, I haue anointed thee for King ouer Israel.
13 Sai suka yi sauri suka ɗauki rigunansu suka shimfiɗa a ƙasa, suka busa kakaki, suka yi ihu, suka ce, “Yehu ne sarki.”
Then they made haste, and tooke euerie man his garment, and put it vnder him on the top of the staires, and blewe the trumpet, saying, Iehu is King.
14 Saboda haka, Yehu ɗan Yehoshafat, ɗan Nimshi, ya ƙulla wa Yoram maƙarƙashiya (To, Yoram da dukan Isra’ila suna kāre Ramot Gileyad daga Hazayel sarkin Aram,
So Iehu ye sonne of Iehoshaphat the sonne of Nimshi conspired against Ioram: (Now Ioram kept Ramoth Gilead, he and all Israel, because of Hazael King of Aram.
15 amma Sarki Yoram ya koma Yezireyel don yă farfaɗo daga raunukan da Arameyawa suka ji masa a wata gabzawar da ya yi da Hazayel sarkin Aram.) Yehu ya ce, “In haka kuke ji, kada ku bar wani yă sulluɓe daga birnin yă kai labarin Yezireyel.”
And King Ioram returned to bee healed in Izreel of the woundes, which the Aramites had giuen him, when hee fought with Hazael King of Aram) and Iehu sayde, If it be your mindes, let no man depart and escape out of the citie, to goe and tell in Izreel.
16 Sai ya tashi ya ɗauki keken yaƙinsa ya tafi Yezireyel gama Yoram yana hutawa a can. Ga kuma Ahaziya sarkin Yahuda ya je don yă gan shi.
So Iehu gate vp into a charet, and went to Izreel: for Ioram lay there, and Ahaziah King of Iudah was come downe to see Ioram.
17 Mai tsaro kuwa yana tsaye a kan hasumiya a Yezireyel, sai ya hangi rundunar Yehu sa’ad da yake zuwa. Ya ce, “Na ga wata runduna.” Sai Yoram ya umarta, “Nemi mahayin doki a aike shi yă tarye su, yă kuma tambaye su, ‘Lafiya?’”
And the watchman that stoode in the towre in Izreel spyed the companie of Iehu as hee came, and sayd, I see a companie. And Iehoram said, Take a horseman and send to meete them, that hee may say, Is it peace?
18 Sai mahayin dokin ya hau, ya ruga, ya taryi Yehu, ya ce, “Ga abin da sarki ya ce, ‘Lafiya?’” Sai Yehu ya ce masa, “Ina ruwanka da zancen lafiya? Ka shiga layi.” Sai mai tsaron ya ce wa sarki, “Ɗan saƙon ya kai wurinsu, amma ba ya dawowa.”
So there went one on horseback to meete him, and sayde, Thus sayth the King, Is it peace? And Iehu sayd, What hast thou to do with peace? Turne behinde me. And the watchman tolde, saying, The messenger came to them, but he commeth not againe.
19 Saboda haka sarki ya sāke aika mahayin doki na biyu. Sa’ad da ya isa wurinsu sai ya ce, “Ga abin da sarki ya ce, ‘Lafiya?’” Yehu ya ce, “Ina ruwanka da zancen lafiya? Ka shiga layi.”
Then hee sent out another on horsebacke, which came to them, and sayde, Thus sayth the King, Is it peace? And Iehu answered, What hast thou to doe with peace? turne behinde me.
20 Mai tsaro ya sāke cewa, “Ya kai wurinsu, amma shi ma ba ya dawowa. Ina ganin sukuwar kamar irin ta Yehu, jikan Nimshi, gama yakan yi sukuwa kamar mahaukaci.”
And the watchman tolde, saying, He came to them also, but commeth not againe, and the marching is like the marching of Iehu the sonne of Nimshi: for he marcheth furiously.
21 Yoram ya umarta, “Haɗa mini keken yaƙi!” Da aka haɗa, sai Yoram sarkin Isra’ila, da Ahaziya sarkin Yahuda, suka hau suka tafi, kowa a keken yaƙinsa, don su taryi Yehu. Suka sadu da shi a filin da yake na Nabot mutumin Yezireyel.
Then Iehoram sayd, Make ready: and his charet was made ready. And Iehoram King of Israel and Ahaziah King of Iudah went out eyther of them in his charet against Iehu, and met him in the fielde of Naboth the Izreelite.
22 Sa’ad da Yoram ya ga Yehu sai ya tambaye shi, “Lafiya kuwa ka zo, Yehu?” Yehu ya ce, “Ina kuwa lafiya, da yake dukan bautar gumaka da bokancin mahaifiyarka Yezebel sun bazu ko’ina?”
And when Iehoram sawe Iehu, he sayde, Is it peace, Iehu? And he answered, What peace? whiles the whoredomes of thy mother Iezebel, and her witchcraftes are yet in great nomber?
23 Yoram ya juya, ya gudu, yana ce wa Ahaziya, “Cin amana, Ahaziya!”
Then Iehoram turned his hand, and fled, and said to Ahaziah, O Ahaziah, there is treason.
24 Sai Yehu ya ja bakansa ya harbi Yoram a tsakanin kafaɗunsa. Kibiyar ta same shi a zuciyarsa sai ya fāɗi a cikin keken yaƙinsa.
But Iehu tooke a bowe in his hande, and smote Iehoram betweene the shoulders, that the arowe went through his heart: and he fell downe in his charet.
25 Yehu ya ce wa Bidkar, hafsan keken yaƙinsa, “Ka ɗauke shi ka jefar a filin da yake na Nabot mutumin Yezireyel. Ka tuna yadda ni da kai muke a kekunan yaƙi a bayan Ahab mahaifinsa sa’ad da Ubangiji ya yi wannan annabci game da shi,
Then said Iehu to Bidkar a captaine, Take, and cast him in some place of the fielde of Naboth the Izreelite: for I remember that when I and thou rode together after Ahab his father, the Lord layed this burden vpon him.
26 ‘Jiya na ga jinin Nabot da jinin’ya’yansa, in ji Ubangiji, kuma ba shakka zan ɗauki fansa a wannan fili, in ji Ubangiji.’ Saboda haka, ka ɗauke shi ka jefar da shi a bisa wannan fegi, bisa ga faɗin Ubangiji. Saboda haka, ka ɗauke shi ka jefar a filin, in ji Ubangiji.”
Surely I haue seene yesterday the blood of Naboth, and the blood of his sonnes, saide the Lord, and I will render it thee in this fielde, saith the Lord: nowe therefore take and cast him in the fielde, according to the word of the Lord.
27 Sa’ad da Ahaziya sarkin Yahuda ya ga abin da ya faru, sai ya haura hanyar Bet Haggan a guje. Yehu ya bi shi yana ihu, “A kashe shi, shi ma!” Suka ji masa rauni a keken yaƙinsa a hanya zuwa Gur, kusa da Ibileyam amma ya tsere zuwa Megiddo ya mutu a can.
But when Ahaziah the King of Iudah saw this, he fled by the way of the garden house: And Iehu pursued after him, and sayd, Smite him also in the charet: and they smote him in the going vp to Gur, which is by Ibleam. And hee fled to Megiddo, and there dyed.
28 Barorinsa suka ɗauke shi cikin keken yaƙi zuwa Urushalima suka binne shi a kabarinsa tare da kakanninsa a birnin Dawuda.
And his seruants caried him in a charet to Ierusalem, and buried him in his sepulchre with his fathers in the citie of Dauid.
29 (A shekara ta goma sha ɗaya ta Yoram ɗan Ahab, Ahaziya ya zama sarkin Yahuda.)
And in the eleuenth yere of Ioram the sonne of Ahab, began Ahaziah to reigne ouer Iudah.
30 Sa’an nan Yehu ya je Yezireyel. Sa’ad da Yezebel ta sami labari, sai ta sha kwalliya ta gyara gashin kanta, ta zauna tana kallo daga taga.
And when Iehu was come to Izreel, Iezebel heard of it, and painted her face, and tired her head, and looked out at a windowe.
31 Yayinda Yehu ya shiga ƙofa, sai ta ce, “Lafiya, kai Zimri, mai kashe maigidansa?”
And as Iehu entred at the gate, shee sayde, Had Zimri peace, which slewe his master?
32 Sai ya ɗaga ido ya dubi tagan ya ce, “Wa yake gefena? Wane ne?” Sai bābānni biyu ko uku suka leƙo suka dube shi.
And he lift vp his eyes to the windowe, and sayd, Who is on my side, who? Then two or three of her Eunuches looked vnto him.
33 Yehu ya ce musu, “Ku jefa ta ƙasa!” Sai suka jefar da ita, jininta ya fantsama a jikin bango da kuma a jikin dawakai yayinda suke tattaka ta.
And he sayde, Cast her downe: and they cast her downe, and hee sprinkled of her blood vpon the wall, and vpon the horses, and he trode her vnder foote.
34 Yehu ya shiga ya ci, ya kuma sha. Ya ce, “Ku san yadda za ku yi da la’ananniyan nan, ku binne ta, gama’yar sarki ce.”
And when he was come in, he did eate and drinke, and sayde, Visite now yonder cursed woman, and burie her: for she is a Kings daughter.
35 Amma sa’ad da suka je don su binne ta, ba su sami kome ba sai ƙoƙon kanta, ƙafafunta da kuma hannuwanta.
And they went to burie her, but they foud no more of her, then the skull and the feete, and the palmes of her handes.
36 Suka komo suka faɗa wa Yehu, wanda ya ce, “Wannan ita ce maganar da Ubangiji ya faɗa ta bakin bawansa Iliya mutumin Tishbe. A fili, a Yezireyel, karnuka za su cinye naman Yezebel.
Wherefore they came agayne and tolde him. And he said, This is the worde of the Lord, which he spake by his seruant Eliiah the Tishbite, saying, In the fielde of Izreel shall ye dogs eate the flesh of Iezebel.
37 Gawar Yezebel zai zama kamar juji a ƙasa, a fili, a Yezireyel, har ba wanda zai iya cewa, ‘Wannan Yezebel ce.’”
And the carkeis of Iezebel shalbe as doung vpon the ground in the field of Izreel, so that none shall say, This is Iezebel.