< 2 Sarakuna 5 >

1 Na’aman babban hafsan hafsoshin rundunar sarkin Aram ne, kuma ƙasaitaccen mutum ne mai martaba a idon maigidansa, domin ta wurinsa Ubangiji ya ba Aram nasara. Na’aman jarumi ne ƙwarai, amma yana da kuturta.
And Naaman, head of the host of the king of Aram, was a great man before his lord, and accepted of face, for YHWH had given salvation to Aram by him, and the man was mighty in valor, [but] leprous.
2 To, daga cikin hare haren da mutanen Aram suke kaiwa, sai suka kama wata yarinya daga ƙasar Isra’ila, aka sa ta zama mai yi wa matar Na’aman aiki.
And the Arameans have gone out [by] troops, and they take a little girl captive out of the land of Israel, and she is before the wife of Naaman,
3 Sai ta ce wa uwargijiyarta, “Da dai shugabana zai ga annabin da yake Samariya, da annabin zai warkar da shi daga kuturtarsa.”
and she says to her mistress, “O that my lord [were] before the prophet who [is] in Samaria; then he recovers him from his leprosy.”
4 Sai Na’aman ya je wurin maigidansa ya faɗa masa abin da yarinyan nan daga Isra’ila ta faɗa.
And [one] goes in and declares [it] to his lord, saying, “Thus and thus the girl who [is] from the land of Israel has spoken.”
5 Sarkin Aram ya ce, “Ko ta ƙaƙa, ka tafi, zan aika da wasiƙa ga sarkin Isra’ila.” Sai Na’aman ya tashi, ɗauke da talenti goma na azurfa, shekel dubu shida na zinariya, da tufafi kashi goma.
And the king of Aram says, “Go, enter, and I send a letter to the king of Israel”; and he goes and takes in his hand ten talents of silver, and six thousand [pieces] of gold, and ten changes of garments.
6 Wasiƙar da ya kai wa sarkin Isra’ila ta ce, “Da wannan wasiƙa ina aika Na’aman gare ka don ka warkar da kuturtarsa.”
And he brings in the letter to the king of Israel, saying, “And now, at the coming in of this letter to you, behold, I have sent my servant Naaman to you, and you have recovered him from his leprosy.”
7 Da sarkin Isra’ila ya karanta wasiƙar, sai ya yayyage tufafinsa, ya ce, “Ni Allah ne? Zan iya ɗauke rai ko in mai da shi? Me ya sa wannan mutum ya turo mini wannan mutum in warkar da kuturtarsa? Dubi fa yadda yake nemana da faɗa!”
And it comes to pass, at the king of Israel’s reading the letter, that he tears his garments and says, “Am I God, to put to death and to keep alive, that this [one] is sending to me to recover a man from his leprosy? For surely know now, and see, for he is presenting himself to me.”
8 Da Elisha mutumin Allah ya ji cewa sarkin Isra’ila ya yayyage tufafinsa, sai ya aika masa da wannan saƙo, “Don me za ka yayyage tufafinka? Ka sa mutumin yă zo wurina, zai kuwa san cewa akwai annabi a Isra’ila.”
And it comes to pass, at Elisha the man of God’s hearing that the king of Israel has torn his garments, that he sends to the king, saying, “Why have you torn your garments? Please let him come to me, and he knows that there is a prophet in Israel.”
9 Saboda haka Na’aman ya tafi da dawakansa da keken yaƙinsa, ya tsaya a ƙofar gidan Elisha.
And Naaman comes, with his horses and with his chariot, and stands at the opening of the house for Elisha;
10 Sai Elisha ya aika’yan saƙo su ce masa, “Je, ka nutse sau bakwai a Urdun, fatar jikinka za tă koma daidai, ka kuma tsarkaka.”
and Elisha sends a messenger to him, saying, “Go, and you have washed seven times in the Jordan, and your flesh turns back to you—and be clean.”
11 Amma Na’aman ya tashi daga can da fushi yana cewa, “Na yi tsammani zai fito ne wurina yă tsaya, yă yi kira bisa ga sunan Ubangiji Allahnsa, yă kaɗa hannunsa inda kuturtar take, yă warkar da ni.
And Naaman is angry, and goes on and says, “Behold, I said, He certainly comes out to me, and has stood and called in the Name of his God YHWH, and waved his hand over the place, and recovered the leper.
12 Ashe, Amana da Farfa, kogunan da suke Damaskus, ba su fi dukan ruwan da suke Isra’ila ba? Me zai sa ba zan nutse cikinsu in tsarkaka ba?” Sai ya juya ya yi tafiyarsa da fushi.
Are not Abana and Pharpar, rivers of Damascus, better than all the waters of Israel? Do I not wash in them and I have been clean?” And he turns and goes on in fury.
13 Sai bayin Na’aman suka je kusa da shi suka ce, “Baba, da a ce annabin ya ce ka yi wani abu mai wuya, da ba za ka yi ba? Balle fa cewa kawai ya yi, ‘Ka yi wanka ka kuma tsarkaka’!”
And his servants come near, and speak to him, and say, “My father, the prophet had spoken a great thing to you—do you not do [it]? And surely, when he has said to you, Wash, and be clean.”
14 Saboda haka Na’aman ya je ya nutse sau bakwai a Urdun, yadda mutumin Allah ya ce masa, sai fatarsa ta koma kamar ta ɗan yaro.
And he goes down and dips in the Jordan seven times, according to the word of the man of God, and his flesh turns back as the flesh of a little youth, and is clean.
15 Sai Na’aman da dukan masu hidimarsa suka koma wurin mutumin Allah. Na’aman ya tsaya a gaban mutumin Allah ya ce, “Yanzu na san cewa babu wani Allah a duk duniya sai a Isra’ila. Ina roƙonka ka karɓi kyauta daga hannun bawanka.”
And he turns back to the man of God, he and all his camp, and comes in, and stands before him, and says, “Now behold, I have known that there is not a God in all the earth except in Israel; and now, please take a blessing from your servant.”
16 Annabin ya amsa ya ce, “Muddin Ubangiji wanda nake bauta masa yana a raye, ba zan karɓi kome ba.” Ko da yake Na’aman ya yi ta roƙonsa, amma ya ƙi.
And he says, “YHWH lives, before whom I have stood—if I take [it]”; and he presses on him to take, and he refuses.
17 Sai Na’aman ya ce, “In ba za ka karɓa ba, ina roƙonka, bari a ba wa bawanka ƙasa gwargwadon abin da jakuna biyu za su iya ɗauka, gama bawanka ba zai sāke yin hadaya ta ƙonawa, ko wata hadaya ga wani allah ba, sai ga Ubangiji.
And Naaman says, “If not, please let a couple of mules’ burden of earth be given to your servant, for your servant makes no more burnt-offering and sacrifice to other gods, but [only sacrifices] to YHWH.
18 Amma ina fata Ubangiji zai gafarta wa bawanka saboda abu guda. Bari yă gafarta mini sa’ad da na raka sarkina zuwa haikalin Rimmon domin yă yi sujada, bari Ubangiji yă yi wa bawanka gafara saboda wannan.”
For in this thing may YHWH be propitious to your servant, in the coming in of my lord into the house of Rimmon to bow himself there, and he was supported by my hand, and I bowed myself [in] the house of Rimmon; for my bowing myself in the house of Rimmon, may YHWH now be propitious to your servant in this thing.”
19 Sai Elisha ya ce, “Ka sauka lafiya.” Bayan Na’aman ya yi ɗan nisa,
And he says to him, “Go in peace.” And he goes from him a distance of land,
20 sai Gehazi, bawan Elisha mutumin Allah, ya yi tunani a ransa ya ce, “Maigidana ya yi wa Na’aman mutumin Aram nan ƙaramci da bai karɓi duk abin da ya kawo ba. Muddin Ubangiji yana a raye, zan bi shi a guje in karɓi wani abu daga gare shi.”
and Gehazi, servant of Elisha the man of God, says, “Behold, my lord has spared this Aramean Naaman, not to receive from his hand that which he brought; for YHWH lives; if I have run after him, then I have taken something from him.”
21 Saboda haka Gehazi ya bi Na’aman a guje. Da Na’aman ya hango shi yana zuwa a guje, sai ya sauka daga keken yaƙinsa ya tarye shi ya ce, “Lafiya?”
And Gehazi pursues after Naaman, and Naaman sees one running after him, and comes down off the chariot to meet him, and says, “Is there peace?”
22 Gehazi ya amsa ya ce, “Lafiya ƙalau. Maigidana ne ya aiko ni cewa, ‘Samari biyu daga ƙungiyar annabawa sun ziyarce ni daga ƙasa mai duwatsu na yankin Efraim. Ina roƙonka ka ba su talenti na azurfa da tufafi kashi biyu.’”
And he says, “Peace; my lord has sent me, saying, Behold, now, this, two young men of the sons of the prophets have come to me from the hill-country of Ephraim; please give a talent of silver and two changes of garments to them.”
23 Na’aman ya ce, “Ba damuwa, karɓi talenti biyu.” Ya roƙi Gehazi yă karɓa, sa’an nan ya ƙunsa masa talentin biyu na azurfa ya sa masa a kan jakankuna biyu, ya haɗa da tufafi kashi biyu, ya ba bayinsa biyu suka ɗauka, ya ce su sha gaban Gehazi.
And Naaman says, “Be pleased, take two talents”; and he urges him, and binds two talents of silver in two purses, and two changes of garments, and gives [them] to two of his young men, and they carry [them] before him;
24 Da Gehazi ya isa wani tudu, sai ya karɓi kayan daga wurin bayin ya shiga da su a ɓoye a cikin gida. Sa’an nan ya sallami mutanen suka tafi.
and he comes to the high place, and takes [them] out of their hand, and lays [them] up in the house, and sends the men away, and they go.
25 Sa’an nan ya shiga ya tsaya a gaban maigidansa Elisha. Sai Elisha ya tambaye shi ya ce, “Ina ka je, Gehazi?” Sai Gehazi ya amsa ya ce, “Bawanka bai je ko’ina ba.”
And he has come in, and stands by his lord, and Elisha says to him, “From where—Gehazi?” And he says, “Your servant did not go here or there.”
26 Amma Elisha ya ce masa, “Ashe, ba ina tare da kai a ruhu ba sa’ad da mutumin ya sauko daga keken yaƙinsa ya tarye ka. Kana gani wannan lokaci ne da za a karɓi kuɗi, da riguna, da gonar inabi, da tumaki, da bijimai, da bayi maza da mata?
And he says to him, “My heart did not go when the man turned from off his chariot to meet you; is it a time to take silver, and to take garments, and olives, and vines, and flock, and herd, and menservants, and maidservants?
27 Kuturtar Na’aman zai manne maka da zuriyarka har abada.” Sai Gehazi ya fita daga gaban Elisha a kuturce, fari fat kamar dusar ƙanƙara.
Indeed, the leprosy of Naaman cleaves to you and to your seed for all time”; and he goes out from before him—leprous as snow.

< 2 Sarakuna 5 >