< 2 Sarakuna 20 >

1 A kwanakin nan sai Hezekiya ya kamu da rashin lafiya har ya kusa mutuwa. Sai annabi Ishaya ɗan Amoz ya zo wurinsa ya ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ka kintsa gidanka domin za ka mutu, ba za ka warke ba.”
In those days Hezekiah has been sick to death, and Isaiah son of Amoz the prophet comes to him and says to him, “Thus said YHWH: Give a charge to your house, for you are dying, and do not live.”
2 Hezekiya ya juya fuskarsa wajen bango ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce,
And he turns around his face to the wall, and prays to YHWH, saying,
3 “Ya Ubangiji, ka tuna yadda na yi tafiya a gabanka da aminci da zuciya ɗaya, na kuma aikata abin da yake daidai a gabanka.” Sai Hezekiya ya yi kuka mai zafi.
“Ah, now, O YHWH, please remember how I have habitually walked before You in truth and with a perfect heart, and I have done that which [is] good in Your eyes”; and Hezekiah weeps [with] a great weeping.
4 Kafin Ishaya yă bar tsakiyar filin gida, sai maganar Ubangiji ta zo masa cewa,
And it comes to pass, [when] Isaiah has not [yet] gone out to the middle court, that the word of YHWH has been to him, saying,
5 “Ka koma ka ce wa Hezekiya, shugaban mutanena, ‘Ga abin da Ubangiji Allah na mahaifinka Dawuda ya ce, na ji addu’arka na kuma ga hawayenka; zan warkar da kai. A rana ta uku daga yau za ka haura zuwa haikalin Ubangiji.
“Return, and you have said to Hezekiah, leader of My people, Thus said YHWH, God of your father David: I have heard your prayer, I have seen your tear, behold, I give healing to you. On the third day you go up to the house of YHWH;
6 Zan ƙara maka shekara goma sha biyar. Zan kuma cece ka daga hannun sarkin Assuriya. Zan kāre birnin nan saboda kaina da kuma bawana Dawuda.’”
and I have added fifteen years to your days, and I deliver you and this city out of the hand of the king of Asshur, and have covered over this city for My own sake, and for the sake of My servant David.”
7 Sai Ishaya ya ce, “A kwaɓa ɓaure.” Sai aka yi haka, aka shafa wa marurun, ya kuma warke.
And Isaiah says, “Take a cake of figs”; and they take and lay [it] on the boil, and he revives.
8 Hezekiya ya tambayi Ishaya, “Wace alama ce za tă nuna cewa Ubangiji zai warkar da ni, kuma cewa in tafi haikalin Ubangiji kwana uku daga yanzu?”
And Hezekiah says to Isaiah, “What [is] the sign that YHWH gives healing to me, that I have gone up to the house of YHWH on the third day?”
9 Sai Ishaya ya ce, “Ga alamar Ubangiji zuwa gare ka da za tă nuna cewa Ubangiji zai cika alkawarinsa. Kana so inuwa tă yi gaba da taki goma, ko tă koma baya da taki goma?”
And Isaiah says, “This [is] the sign to you from YHWH, that YHWH does the thing that He has spoken—[will] the shadow have gone on ten degrees, or does it turn back ten degrees?”
10 “Ai, abu mai sauƙi ne inuwa tă yi gaba da taki goma.” In ji Hezekiya, “Gwamma dai tă koma baya da taki goma.”
And Hezekiah says, “It has been light for the shadow to incline ten degrees; no, but let the shadow turn backward ten degrees.”
11 Sai annabi Ishaya ya roƙi Ubangiji, Ubangiji kuwa ya sa inuwa ta koma baya da taki goma bisa ga magwajin rana wanda Sarki Ahaz ya gina.
And Isaiah the prophet calls to YHWH, and He brings back the shadow by the degrees that it had gone down in the degrees of Ahaz—backward ten degrees.
12 A wannan lokaci, Merodak-Baladan ɗan Baladan sarkin Babilon ya aika wa Hezekiya wasiƙu tare da kyauta, domin ya sami labarin rashin lafiyar Hezekiya.
At that time Berodach-Baladan son of Baladan, king of Babylon, has sent letters and a present to Hezekiah, for he heard that Hezekiah had been sick;
13 Hezekiya ya karɓi jakadun, ya nuna musu dukan abin da yake a ɗakunan ajiyarsa, azurfa, zinariya, kayan ƙanshi da mai, wurin ajiye makamansa da kuma dukan abin da aka samu a ɗakin ajiyarsa. Babu wani abu a fadansa ko a dukan mulkinsa da Hezekiya bai nuna musu ba.
and Hezekiah listens to them, and shows them all the house of his treasury, the silver, and the gold, and the spices, and the good ointment, and all the house of his vessels, and all that has been found in his treasuries; there has not been a thing that Hezekiah has not showed them in his house and in all his dominion.
14 Sai annabi Ishaya ya tafi wurin Sarki Hezekiya ya tambaye shi ya ce, “Me mutanen nan suka ce, kuma daga ina suka fito?” Sai Hezekiya ya ce, “Daga ƙasa mai nisa. Daga Babilon.”
And Isaiah the prophet comes to King Hezekiah and says to him, “What did these men say? And from where do they come to you?” And Hezekiah says, “They have come from a far-off land—from Babylon.”
15 Annabin ya yi tambaya, “Me suka gani a fadanka?” Hezekiya ya ce, “Ba abin da yake a ma’ajina da ban nuna musu ba.”
And he says, “What did they see in your house?” And Hezekiah says, “They saw all that [is] in my house; there has not been a thing that I have not showed them among my treasures.”
16 Sai Ishaya ya ce wa Hezekiya, “Ka ji kalmar Ubangiji.
And Isaiah says to Hezekiah, “Hear a word of YHWH:
17 Lokaci yana zuwa da za a kwashe kome a fadanka da kuma dukan abubuwan da kakanninka suka tara har yă zuwa yau, a kai su Babilon. Ba abin da za a rage, in ji Ubangiji.
Behold, days are coming, and all that [is] in your house, and [all] that your father has treasured up until this day, has been carried to Babylon; there is not a thing left, said YHWH;
18 Za a kuma kwashe waɗansu daga cikin zuriyarka, na jiki da jininka waɗanda za a haifa maka, su zama bābānni a fadan sarkin Babilon.”
and of your sons who go out from you, whom you beget, they take away, and they have been eunuchs in the palace of the king of Babylon.”
19 Hezekiya ya ce, “Maganar Ubangiji da ka faɗa ta yi kyau.” Gama ya yi tunani cewa, “Ai, ba ni da damuwa, tun da yake za a yi zaman lafiya da salama a kwanakina.”
And Hezekiah says to Isaiah, “The word of YHWH that you have spoken [is] good”; and he says, “Why not, if there is peace and truth in my days?”
20 Game da sauran ayyukan mulkin Hezekiya, dukan nasarorinsa da yadda ya yi tafki da kuma bututun ruwa inda ya kawo ruwa cikin birni, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
And the rest of the matters of Hezekiah, and all his might, and how he made the pool, and the conduit, and brings in the waters to the city, are they not written on the scroll of the Chronicles of the Kings of Judah?
21 Hezekiya ya huta tare da kakanninsa. Manasse ɗansa kuma ya gāje shi.
And Hezekiah lies with his fathers, and his son Manasseh reigns in his stead.

< 2 Sarakuna 20 >