< 2 Sarakuna 11 >

1 Da Ataliya mahaifiyar Ahaziya ta ga ɗanta ya mutu, sai ta shiga hallaka dukan iyalin gidan sarauta.
Athalie, mère d'Ochozias, voyant que son fils était mort, se leva et fit périr toute la race royale.
2 Amma Yehosheba,’yar Sarki Yoram,’yar’uwar Ahaziya, ta ɗauki Yowash ɗan Ahaziya daga cikin’ya’yan sarkin da ake shiri a kashe, ta ɓoye. Ta ɓoye shi daga Ataliya a wurin mai lura da shi a ɗakin kwana; don kada a kashe shi.
Mais Josaba, fille du roi Joram et sœur d'Ochozias, prit Joas, fils d'Ochozias, et l'enleva du milieu des fils du roi que l'on massacrait; elle le mit avec sa nourrice dans la chambre des lits. On le déroba ainsi aux regards d'Athalie, et il ne fut pas mis à mort.
3 Ya kasance a ɓoye, shi da mai lura da shi, a haikalin Ubangiji shekara shida yayinda Ataliya take mulkin ƙasar.
Il resta six ans caché avec Joschéba dans la maison de Yahweh; et ce fut Athalie qui régna sur le pays.
4 A shekara ta bakwai sai Yehohiyada ya aika a kira komandodin sojoji ɗari-ɗari, da Keretawa, da matsara, ya sa aka kawo masa su a haikalin Ubangiji. Ya ƙulla yarjejjeniya da rantsuwa da su a haikalin Ubangiji, sa’an nan ya nuna musu ɗan sarki.
La septième année, Joïada envoya chercher les centurions des Cariens et des coureurs, et il les fit venir auprès de lui dans la maison de Yahweh. Il conclut une alliance avec eux et, après leur avoir fait prêter serment dans la maison de Yahweh, il leur montra le fils du roi.
5 Ya umarce su cewa, “Ga abin da za ku yi sa’ad da kuka zo aiki a Asabbaci, ku raba kanku kashi uku. Kashi ɗaya za su yi gadin gidan sarki,
Puis il leur donna ses ordres, en disant: « Voici ce que vous ferez: Le tiers d'entre vous qui entre en service le jour du sabbat, pour monter la garde à la maison du roi,
6 kashi ɗaya za su yi gadin Ƙofar Sur, kashi ɗaya kuma za su yi gadin ƙofar da take bayan’yan gadin fada. Dukan waɗannan ƙungiyoyi uku za su yi gadin fadan,
— le tiers à la porte de Sur, et le tiers à la porte des coureurs, — vous ferez la garde à la maison de Yahweh pour en interdire l'entrée.
7 ku kuma da kuke a sauran ƙungiyoyi biyu da kun saba hutu a Asabbaci, duk za ku yi gadin haikali don sarki.
Et vos deux autres divisions, tous ceux qui sortent de service le jour du sabbat, pour monter la garde à la maison de Yahweh auprès du roi,
8 Ku tsaya kewaye da sarki, kowane mutum da makaminsa a hannu. Duk wanda ya kusace ku, ku kashe shi. Ku manne wa sarki duk inda ya tafi.”
vous entourerez le roi de toutes parts, chacun les armes à la main; si quelqu'un entre dans les rangs, qu'on le mette à mort; et vous serez près du roi quand il sortira et quand il entrera. »
9 Komandodin sojoji suka yi yadda Yehohiyada firist ya umarta. Kowa ya ɗauki mutanensa, waɗanda za su kama aiki Asabbaci da waɗanda za su kama hutun Asabbaci, suka zo wurin Yehohiyada firist.
Les centurions agirent selon tout ce qu'avait ordonné le prêtre Joïada. Ayant pris chacun leurs gens, ceux qui entraient en service le jour du sabbat et ceux qui sortaient de service le jour du sabbat, ils se rendirent auprès du prêtre Joïada.
10 Sai ya ba komandodin māsu da garkuwoyi da dā suke na Dawuda, waɗanda suke a cikin haikalin Ubangiji.
Le prêtre remit aux centurions les lances et les boucliers qui avaient appartenu au roi David, et qui se trouvaient dans la maison de Yahweh.
11 Matsaran kuma kowa da makaminsa a hannu, suka tsaya kewaye da sarki, kusa da bagade da kuma haikali, daga gefen kudu zuwa gefen arewa na haikalin.
Les coureurs, chacun les armes à la main, se tinrent depuis le côté droit de la maison jusqu'au côté gauche de la maison, près de l'autel et près de la maison, de manière à entourer le roi.
12 Sai Yehohiyada ya fito da ɗan sarki ya sa masa rawani a kā; ya ba shi shafin alkawari, ya kuma furta shi sarki. Suka shafe shi da mai, mutane kuma suka yi ta tafi suka ihu, suna cewa, “Ran sarki yă daɗe.”
Et le prêtre fit avancer le fils du roi, et il mit sur lui le diadème et le témoignage. Ils l'établirent roi et l'oignirent, et, frappant des mains, ils dirent: « Vive le roi! »
13 Sa’ad da Ataliya ta ji surutun matsara da na mutane, sai ta tafi wurin mutanen a haikalin Ubangiji.
Lorsque Athalie entendit le bruit des coureurs et du peuple, elle vint vers le peuple, à la maison de Yahweh.
14 Da ta duba sai ga sarki, tsaye kusa da ginshiƙi, bisa ga al’ada. Hafsoshi da masu busa suna tsaye kusa da sarki, dukan mutanen ƙasar kuma suna farin ciki suna busa ƙahoni. Sai Ataliya ta keta tufafinta ta tā da murya tana cewa, “Kai! Wannan cin amana ne! Ai, wannan cin amana ne!”
Elle regarda, et voici que le roi se tenait sur l'estrade, selon l'usage; près du roi, étaient les chefs et les trompettes, et tout le peuple du pays était dans la joie, et l'on sonnait des trompettes. Athalie déchira ses vêtements et cria: « Conspiration! Conspiration! »
15 Yehohiyada ya umarci komandodin sojoji waɗanda suke lura da mayaƙa, ya ce, “Ku fitar da ita daga cikinku, ku kuma kashe duk wanda ya bi ta.” Gama firist ɗin ya ce, “Kada a kashe ta a cikin haikalin Ubangiji.”
Alors le prêtre Joïada donna un ordre aux centurions qui étaient à la tête de l'armée et leur dit: « Faites-la sortir de la maison entre les rangs, et tuez par l'épée quiconque la suivra. » Car le prêtre avait dit: « Qu'elle ne soit pas mise à mort dans la maison de Yahweh. »
16 Saboda haka suka kama ta yayinda ta kai inda dawakai sukan shiga filin fada, a can kuwa aka kashe ta.
On lui fit place des deux côtés, et elle se rendit par le chemin de l'entrée des chevaux, vers la maison du roi, et c'est là qu'elle fut tuée.
17 Sa’an nan Yehohiyada ya yi alkawari tsakanin Ubangiji da sarki da kuma mutane cewa za su zama mutanen Ubangiji. Ya kuma yi alkawari tsakanin sarki da mutane.
Joïada conclut, entre Yahweh, le roi et le peuple, l'alliance par laquelle ils devaient être le peuple de Yahweh; il fit aussi l'alliance entre le roi et le peuple.
18 Sai dukan mutanen ƙasar suka tafi haikalin Ba’al suka rushe shi. Suka farfasa bagadai da kuma gumaka, suka kuma kashe Mattan wanda yake firist na Ba’al a gaban bagade. Sa’an nan Yehohiyada firist ya sa matsara a haikalin Ubangiji.
Et tout le peuple du pays entra dans la maison de Baal, et ils la démolirent; ils brisèrent entièrement ses autels et ses images, et ils tuèrent devant les autels Mathan, prêtre de Baal. Après avoir mis des gardiens dans la maison de Yahweh,
19 Ya tafi tare da komandodin sojoji, Keretawa, matsara da kuma dukan mutanen ƙasar, tare kuwa suka kawo sarki daga haikalin Ubangiji zuwa cikin fada, ta ƙofar matsara. Sarki kuwa ya ɗauki mazauninsa a bisa kursiyin sarauta,
le prêtre Joïada prit les centurions, les Cariens et les coureurs, et tout le peuple du pays, et ils firent descendre le roi de la maison de Yahweh, et ils entrèrent dans la maison du roi par la porte des coureurs; et Joas s'assit sur le trône des rois.
20 dukan mutanen ƙasar suka yi murna. Birnin ya sami salama don an kashe Ataliya da takobi a fada.
Tout le peuple du pays se réjouit, et la ville fut tranquille; et l'on fit mourir Athalie par l'épée dans la maison du roi.
21 Yowash yana da shekara bakwai sa’ad da ya fara mulki.
Joas avait sept ans lorsqu'il devint roi.

< 2 Sarakuna 11 >