< 2 Korintiyawa 3 >

1 Yabon kanmu ne kuma muka fara yi? Ko kuwa muna bukatar wasiƙun yabo ne zuwa gare ku, ko daga gare ku, kamar yadda waɗansu suke yi?
Must we begin again to commend ourselves? or need we, as some, letters of recommendation to you, or letters of recommendation from you?
2 Ai, ku kanku ku ne wasiƙarmu, wadda aka rubuta a zukatanku, domin kowa yă santa, yă kuma karanta ta.
You are out letter, written on our hearts, known and read of all men.
3 Kun nuna cewa ku wasiƙa ce daga Kiristi, sakamakon hidimarmu, ba wadda aka rubuta da inki ba, sai dai da Ruhun Allah mai rai. Ba kuma a kan allunan dutse ba, sai dai a kan allunan zukatan mutane.
For you are plainly declared Christ's letter, ministered by us, written, not with ink, but with the Spirit of the living God; not on tables of stone, but on fleshly tables of the heart.
4 Amincewa kamar wannan shi ne namu ta wurin Kiristi a gaban Allah.
Now we have such confidence through Christ, toward God;
5 Ba mu da wani abin da za mu nuna cewa da iyawarmu ne muke aikin nan. Iyawarmu daga wurin Allah ne.
not that we are competent by ourselves to reckon anything as from ourselves: but our competency is from God,
6 Shi ya sa muka gwaninta a matsayinmu na masu hidimar sabon alkawari ba ta rubutacciyar Dokar ba, amma ta Ruhu; don Dokar, kisa take yi, Ruhu kuwa yana ba da rai.
who has made us competent ministers of a new institution; not of letter, but of spirit: for the letter kills; but the spirit makes alive.
7 To, in hidimar da ta kawo mutuwa, wadda an rubuta a kan allon dutse, ta zo da ɗaukaka har Isra’ilawa suka kāsa duban fuskar Musa saboda tsananin haskenta, ko da yake mai shuɗewa ce,
For if the ministration of death in letters engraved on stone was with glory, so that the children of Israel could not steadfastly behold the face of Moses, because of the glory of his face, which was to be abolished;
8 ashe, hidimar Ruhu ba za tă fi wannan ɗaukaka ba?
how much rather shall not the ministration of the Spirit be with glory?
9 In hidimar da take jawo wa mutane hukunci tana da ɗaukaka haka, to, lalle, hidimar da take kawo adalci za tă fi ta ɗaukaka nesa!
For if the ministration of condemnation was glorious, much more does the ministration of justification abound in glory.
10 Gama abin da dā take da ɗaukaka, ba ta da ɗaukaka a yanzu, in aka kwatantata da mafificiyar ɗaukaka ta yanzu.
For, indeed, that which was glorified, was not glorified, in this respect, by reason of the transcendent glory.
11 In kuma aba mai shuɗewa ta zo da ɗaukaka, ashe, abin da yake dawwammame, lalle ne yă kasance da ɗaukakar da ta fi haka nesa!
For if that which is abolished was with glory, much more that which continues, is with glory.
12 Da yake muna da bege irin wannan, to, muna da ƙarfin zuciya sosai ke nan.
Having, therefore, such confidence, we use great plainness of speech;
13 Mu ba kamar Musa ba ne, wanda ya rufe fuskarsa da lulluɓi, don kada Isra’ilawa su ga ƙarewar ɗaukakan nan mai shuɗewa.
and not as Moses, who put a vail upon his face, that the children of Israel might not steadfastly look to the end of that which is abolished.
14 Amma aka sa hankulansu suka dushe, gama har yă zuwa yau akwai lulluɓin nan a duk sa’ad da ake karatun tsohon alkawari. Ba a kawar da shi ba, sai a cikin Kiristi ne kaɗai ake kawar da shi.
Indeed, their minds were blinded: for, till this day, the same vail remains in the reading of the Old Institution; it not being discovered that it is abolished in Christ.
15 Har yă zuwa yau, duk sa’ad da ake karatun littattafan Musa, lulluɓin nan yakan rufe zukatansu.
Moreover, till this day, when Moses is read, the vail lies upon their heart.
16 Amma duk sa’ad da wani ya juyo ga Ubangiji, akan kawar da lulluɓin.
But when it shall turn to the Lord, the vail shall be taken from around it.
17 Ubangiji fa, shi ne Ruhu, kuma duk inda Ruhun Ubangiji yake, a nan’yanci yake.
Now, the Lord is the Spirit; and where the Spirit of the Lord is, there is freedom.
18 Mu da ba mu da lulluɓi a fuskokinmu duk muna nuna ɗaukakar Ubangiji, ana sauya mu mu ɗauki kamanninsa cikin ɗaukaka mai hauhawa. Ubangiji wanda yake ruhu kuwa shi ne mai zartar da haka.
And we all, with unvailed face, beholding, as in a mirror, the glory of the Lord; are transformed into the same image, from glory to glory, as by the Lord, the Spirit.

< 2 Korintiyawa 3 >