< 2 Tarihi 34 >

1 Yosiya yana da shekara goma sha takwas sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara talatin da ɗaya.
[約史雅登極]約史雅登極時才八歲,在耶路撒冷作王凡三十一年。
2 Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji ya kuma yi tafiya a hanyoyin kakansa Dawuda, ba tare da juye dama ko hagu ba.
他行了上主視為正義的事,走了他祖先達味所走的路,不偏左,也不偏右。[宗教改革]
3 A shekara ta takwas ta mulkinsa, yayinda yake matashi, sai ya fara neman Allah na kakansa Dawuda. A shekara ta goma sha biyunsa ya fara tsabtacce Yahuda da Urushalima daga masujadan kan tudu, ginshiƙan Ashera, sassaƙaƙƙun gumaka da kuma siffofin da aka yi zubi.
他在位第八年,雖然年幼,就已經開始尋求他祖先達味的天主;在位第十二年,就已開始清潔猶大和耶路撒冷,除去高丘、木偶、彫像和鑄像。
4 A ƙarƙashin umarninsa aka rurrushe bagadan Ba’al, ya kuma tumɓuke bagadan ƙona turare waɗanda suke a bisansu, ya farfashe ginshiƙan Ashera da kuma sassaƙaƙƙun siffofi. Ya ragargaza waɗannan kucu-kucu, ya barbaɗa su a kan kaburburan waɗanda suka miƙa musu hadayu.
他看著人把巴耳的丘壇拆毀,他親自打碎丘壇上的香爐,將木偶、彫像和鑄像打碎,磨成粉末,撒在祭祀偶像的人的墳上;
5 Ya ƙone ƙasusuwan firistocin gumaka a kan bagaden da a dā suke miƙa hadayunsu, ta haka ya tsabtacce Yahuda da Urushalima.
在祭壇上焚燒了邪神司祭的骨骸,這樣潔淨了猶大和耶路撒冷。
6 Ya yi haka cikin garuruwan Manasse, Efraim da Simeyon, har zuwa Naftali, da kuma cikin kangwayen kewayensu,
他在默納協、厄弗辣因、西默盎、以迄納斐塔里各城和期周圍四郊,也行了同樣的事:
7 ya farfashe bagadai da ginshiƙan Ashera; ya niƙa gumaka suka zama gari, ya kuma yayyanka dukan bagadan turare kucu-kucu ko’ina a Isra’ila. Sa’an nan ya koma Urushalima.
拆毀丘壇,將木偶和彫像打碎,將以色列全境內所有的太陽柱都砍倒;然後回了耶路撒冷。[重修聖殿]
8 A shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yosiya, ya tsarkake ƙasar da haikalin, ya aiki Shafan ɗan Azaliya da Ma’asehiya mai mulkin birni, tare da Yowa ɗan Yowahaz, marubuci, su gyara haikalin Ubangiji Allah.
約史雅在位第十八年,進行清潔各地和聖殿時,派阿匝里雅的兒子沙番,城尉瑪阿色雅和約阿哈次的兒子約阿黑御史,去修理他的天主上主的聖殿。
9 Suka tafi wurin Hilkiya babban firist suka ba shi kuɗin da aka kawo cikin haikalin Allah, wanda Lawiyawa masu tsaron ƙofofi sun tattara daga mutanen Manasse, Efraim da dukan raguwar Isra’ila da kuma daga dukan mutanen Yahuda da Benyamin da kuma mazaunan Urushalima.
他們便去見大司祭希耳克雅,將獻於天主殿宇的銀錢當面交給他。這些銀錢是守門的肋未人,由默納協、厄弗辣因和以色列全體遺民,以及猶大、本雅明和耶路撒冷居民那裏收來的。
10 Sa’an nan suka danƙa su ga mutanen da aka naɗa su lura da aiki a kan haikalin Ubangiji. Waɗannan mutane ne suke biyan ma’aikatan da suka gyara suka kuma mai da haikalin.
他們再轉交給監督上主殿內工作的人,這些人發給在上主殿內工作和修理殿宇的人,
11 Suka kuma ba da kuɗi ga kafintoci da magina don su sayi sassaƙaƙƙun duwatsu, da katakai don yin tsaiko da tankar ginin da sarakunan Yahuda suka bari yă fāɗi ya zama kango.
即發給木匠和泥水匠,或購買鑿好的石頭和作木架及棟樑的木材,來修理歷代猶大王失修的建築。
12 Mutanen fa suka yi aiki da aminci. Shugabanninsu, su ne Yahat da Obadiya, Lawiyawa zuriyar Merari da Zakariya da Meshullam, zuriyar Kohat. Dukan Lawiyawa waɗanda suke gwanaye a kayan kiɗi,
這些工人都勤於操作,監管他們工作的監督是默辣黎族的肋未人雅哈特與敖巴狄雅,和刻哈特族的則加黎雅與默叔藍;尚有精於樂器的肋未人,
13 sun lura da ma’aikata, suka kuma lura da dukan masu aiki daga aiki zuwa aiki. Waɗansu Lawiyawan su ne marubuta, magatakarda da kuma masu tsaron ƙofofi.
兼管搬運的人,督促做各種工作的人。肋未人中還有些作書記,作職員,作門丁的。[法律書的發現]
14 Yayinda suke fitar da kuɗin da aka kai cikin haikalin Ubangiji, sai Hilkiya firist ya sami Littafin Dokar Ubangiji da aka bayar ta wurin Musa.
人們將獻於上主殿宇的銀錢拿出來的時候,大司祭希耳克雅發現了上主藉梅瑟所頒布的法律書。
15 Hilkiya ya ce wa Shafan magatakarda, “Na sami Littafin Doka a cikin haikalin Ubangiji.” Sai ya ba wa Shafan.
希耳克雅告訴書記沙番說:「我在上主殿內發現了法律書。」遂將書交給了沙番。
16 Sa’an nan Shafan ya ɗauki littafin zuwa wurin sarki, ya faɗa masa, “Manyan ma’aikatanka suna yin kome da aka sa su.
沙番帶著那卷書去見君王,向君王回報說:「凡陛下命你僕人所辦的事,都已照辦了。
17 Mun ɗauke kuɗin da an ajiye a haikalin Ubangiji muka ba wa masu aiki da waɗanda suke lura da su.”
已將上主殿內所有的銀錢倒出來,交在監督和工人的手裏了。」
18 Sa’an nan Shafan magatakarda ya sanar da sarki ya ce, “Hilkiya firist ya ba ni wani littafi.” Sai Shafan ya karanta daga cikinsa a gaban sarki.
書記沙番繼而向君王報告說:「大司祭希耳克雅還交給我一卷書。」沙番就在君王面前朗誦了那書。
19 Da sarki ya ji kalmomin Doka, sai ya yage rigunansa.
君王一聽了法律上的話,就撕裂了自己的衣服,
20 Ya ba da waɗannan umarnai ga Hilkiya, Ahikam ɗan Shafan, Abdon ɗan Mika, Shafan magatakarda da kuma Asahiya mai hidimar sarki.
立即吩咐希耳克雅、沙番的兒子阿希甘、米加的兒子阿貝冬、書記沙番和君王的臣僕阿撒雅說:「
21 Ya ce, “Ku tafi ku nemi nufin Ubangiji saboda ni da kuma saboda raguwa a Isra’ila da Yahuda game da abin da aka rubuta a wannan littafin da aka samu. Fushin Ubangiji mai girma ne da aka zuba a kanmu domin kakanninmu ba su kiyaye maganar Ubangiji ba; ba su aikata bisa ga dukan abin da yake a rubuce a wannan littafi ba.”
你們快去為我,為以色列的遺民和猶大,詢問上主關於所發現的這書上的話,因為我們的祖先沒有遵守上主的話,未照這書上所記載的去行,所以上主才向我們大發憤怒。」[胡耳達女先知的神諭]
22 Hilkiya tare da waɗanda sarki ya aika, suka tafi suka yi magana da annabiya Hulda, wadda take matar Shallum ɗan Tokhat ɗan Hasra, mai tsaron wurin ajiyar riguna. Tana zama a Urushalima, a Yanki na Biyu.
希耳克雅和君王所派的人,去見胡耳達女先知,她是掌管禮服的沙隆的妻子─沙隆是哈色辣的孫子,堤刻瓦的兒子。胡耳達住在耶路撒冷新區;他們對她說明來意,
23 Sai ta ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce faɗa wa mutumin da ya aike ku gare ni,
她就回答他們說:「上主以色列的天主這樣說:你們回報那派你們來見我的人說:
24 ‘Ga abin da Ubangiji ya ce zai kawo masifa a wannan wuri da mutanensa, dukan la’anar da aka rubuta a cikin littafin da aka karanta a gaban sarkin Yahuda.
上主這意說:我必要使在猶大王前所讀的書中記載的災禍和一切詛咒,降在這地和這地上的居民身上,
25 Domin sun yashe ni suka kuma ƙone turare wa waɗansu alloli, suka tsokane ni in yi fushi ta wurin dukan abin da hannuwansu suka yi, fushina zai zuba a kan wannan wuri, ba kuma za a kwantar da shi ba.’
因為他們捨棄了我,向別的神焚香;他們所做的,無不惹我動怒,所以我的怒火要向這地方發作,總不熄滅。
26 Ku faɗa wa sarkin Yahuda, wanda ya aike ku ku nemi nufin Ubangiji, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yake cewa game da kalmomin da ka ji.
至於那派你們來求問上主的猶大王,你們要這樣對他說:上主以色列的天主這樣說:因為你聽了這些話,
27 Domin zuciyarka mai tuba ce, ka kuma ƙasƙantar da kanka a gaban Allah sa’ad da ka ji abin da ya yi magana a kan wannan wuri da mutanensa, domin kuma ka ƙasƙantar da kanka a gabana, ka yage rigunanka ka kuma yi kuka a gabana, na ji ka, in ji Ubangiji.
因為你一聽了我指著這地和這地上的居民所說的話,你的心就已感化,在上主面前自卑自賤,撕裂了你的衣服,在我面前痛哭,我也應允了你:上主的斷語。
28 Yanzu zan tara ka da kakanninka, za a kuma binne ka cikin salama. Idanunka ba za su ga dukan masifar da zan kawo a kan wannan wuri da kuma a kan waɗanda suke zama a nan ba.’” Sai suka kai amsar wa sarki.
我要使你與你祖先團聚,你要安歸你的墳墓;你的眼睛見不到我在這地上和這些居民身上要降的災禍。」他們回去,將她說的話報告給君王。[重立盟約]
29 Sai sarki ya kira dukan dattawan Yahuda da Urushalima.
君王於是派人召集猶大和耶路撒冷所有的長老來;
30 Ya haura zuwa haikalin Ubangiji tare da mutanen Yahuda, mutanen Urushalima, firistoci da Lawiyawa, dukan mutane daga ƙarami zuwa babba. Ya karanta dukan kalmomin Littafin Alkawari wanda aka samu a cikin haikalin Ubangiji a kunnuwansu.
君王同所有的猶大人,耶路撒冷的居民、司祭、肋未人、全體人民,不分貴賤,都上到上主的殿內,在上主殿內,將尋獲的約書上的一切話,讀給他們聽。
31 Sai sarkin ya miƙe tsaye a inda yake, ya sabunta alkawari a gaban Ubangiji, don yă bi Ubangiji yă kiyaye umarnansa, ƙa’idodinsa da kuma farillansa da dukan zuciyarsa da kuma dukan ransa, ya kuma yi biyayya da kalmomin alkawarin da aka rubuta a cikin wannan littafi.
君王站在高台上,在上主面前立約,要全心全意服從上主,遵守他的誡命,他的典章和他的法律,履行這書上所載的盟約的話;
32 Sa’an nan ya sa kowa a Urushalima da Benyamin ya yi alkawari ga wannan; mutanen Urushalima suka aikata wannan bisa ga alkawarin Allah, Allah na kakanninsu.
他使所有的耶路撒冷的人都接受這盟約。於是耶路撒冷的居民都按照上主,他們祖先天主的盟約而行。
33 Yosiya ya fitar da dukan gumakan banƙyama daga dukan yankunan Isra’ilawa, ya kuma sa dukan waɗanda suke a Isra’ila su bauta wa Ubangiji Allahnsu. Muddin ransa, ba su fasa bin Ubangiji Allah na kakanninsu ba.
約史雅將以色列子民各地的一切可恥之物除去,使所有在以色列的人,都奉事上主他們的天主。約史雅王在世時,他們從未離棄上主,他們祖先的天主。

< 2 Tarihi 34 >