< 2 Tarihi 29 >
1 Hezekiya yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Abiya,’yar Zakariya.
Jehiskia var fem och tjugu åra gammal, då han Konung vardt, och regerade nio och tjugu år i Jerusalem; hans moder het Abija, Zacharia dotter.
2 Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar dai yadda kakansa Dawuda ya yi.
Och han gjorde det Herranom väl behagade, såsom hans fader David.
3 A wata na farkon a farkon shekarar mulkinsa, ya buɗe ƙofofin haikalin Ubangiji ya gyara su.
Han lät upp dörrarna på Herrans hus, i första månadenom af första årena sins rikes, och gjorde dem färdiga;
4 Ya kawo firistoci da Lawiyawa, ya tattara su a filin da yake a gefen gabas
Och lät komma derin Presterna och Leviterna, och församlade dem på breda gatone östantill;
5 ya kuma ce musu, “Ku saurare ni, Lawiyawa! Ku tsarkake kanku yanzu, ku kuma tsarkake haikalin Ubangiji Allah na kakanninku. Ku fid da ƙazanta daga wuri mai tsarki.
Och sade till dem: Hörer härtill, I Leviter: Helger eder nu, på det I mågen helga Herrans edra fäders Guds hus; och hafver ut orenligheten af helgedomenom.
6 Kakanninku ba su yi aminci ba; suka aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnmu, suka kuma yashe shi. Suka juya fuskokinsu daga mazaunin Ubangiji suka kuma juya masa baya.
Ty våre fäder hafva förtagit sig, och gjort det ondt var för Herranom vårom Gud, och hafva öfvergifvit honom; förty de hafva vändt sitt ansigte ifrå Herrans boning, och vändt ryggen till,
7 Suka kulle ƙofofin shirayi, suka kuma kashe fitilu. Ba su ƙone turare ko su miƙa hadayun ƙonawa a wuri mai tsarki ga Allah na Isra’ila ba.
Och hafva igenlyckt dörrarna till förhuset, och utsläckt lamporna, och intet rökverk röka låtit, och intet bränneoffer gjort Israels Gudi i helgedomenom.
8 Saboda haka, fushin Ubangiji ya fāɗo a kan Yahuda da Urushalima; ya mai da su abin tsoro da abin banrazana da kuma abin ba’a, kamar yadda kuke gani da idanunku.
Deraf är Herrans vrede kommen öfver Juda och Jerusalem, och han hafver gifvit dem till att förskingras och förödas, så att man hvisslar åt dem, såsom I med edor ögon sen.
9 Abin da ya sa ke nan kakanninmu suka fāɗi ta takobi, kuma shi ya sa aka kai’ya’yanmu maza da’ya’yanmu mata da matanmu bauta.
Ty si, fördenskull äro våre fäder fallne genom svärd; våre söner, döttrar och hustrur äro bortförde.
10 Yanzu ina niyya in yi alkawari da Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin fushinsa yă kauce daga gare mu.
Nu hafver jag i sinnet att göra med Herranom Israels Gud ett förbund, att hans vrede och grymhet må vända sig ifrån oss.
11 ’Ya’yana maza, kada ku yi sakaci yanzu, gama Ubangiji ya zaɓe ku don ku tsaya a gabansa ku kuma yi masa hidima, don ku yi hidima a gabansa ku kuma ƙone turare.”
Nu, mine söner, varer icke försummelige; ty eder hafver Herren utkorat, att I skolen stå för honom, och att I skolen vara hans tjenare och rökare.
12 Sai waɗannan Lawiyawa suka shiga aiki, daga Kohatawa Mahat ɗan Amasai da Yowel ɗan Azariya. Daga Kabilar Merari, Kish ɗan Abdi da Azariya ɗan Yahallelel. Daga Gershonawa, Yowa ɗan Zimma da Eden ɗan Yowa.
Då stodo Leviterna upp, Mahath, Amasai son, och Joel, Asaria son af de Kehathiters barn; men af Merari barn, Kis, Abdi son, och Asaria, Jehaleleels son; af de Gersoniters barn, Joah, Simma son, och Eden, Joahs son;
13 Daga zuriyar Elizafan, Shimri da Yehiyel. Daga zuriyar Asaf, Zakariya da Mattaniya.
Och af Elizaphans barn, Simri och Jegiel; af Assaphs barn, Sacharia och Matthania;
14 Daga iyalin Heman, Yehiyel da Shimeyi. Daga zuriyar Yedutun, Shemahiya da Uzziyel.
Af Hemans barn, Jehiel och Simei; af Jeduthuns barn, Semaja och Usiel.
15 Da suka tattara’yan’uwansu suka kuma tsarkake kansu, sai suka shiga ciki suka tsarkake haikalin Ubangiji, kamar yadda sarki ya umarta, suna bin maganar Ubangiji.
Och de församlade sina bröder, och helgade sig, och gingo in, efter Konungens bud, af Herrans ord, till att rena Herrans hus.
16 Firistoci suka shiga cikin wuri mai tsarki na Ubangiji suka tsarkake shi. Suka fitar da dukan abin da yake marar tsabta da suka samu a haikalin Ubangiji zuwa filin haikalin Ubangiji. Lawiyawa suka ɗauke su suka kai su Kwarin Kidron.
Och Presterna gingo in uti Herrans hus, till att rena det, och lade all den orenhet, som i Herrans tempel funnen vardt, uppå gården åt Herrans hus; och Leviterna togo henne upp, och båro ut i Kidrons bäck.
17 Suka fara tsarkakewar a rana ta farko na farkon wata, a rana ta takwas na watan kuwa suka kai shirayin Ubangiji. Karin kwana takwas kuma suka tsarkake haikalin Ubangiji kansa, suka gama a rana ta goma sha shida na farkon wata.
På första dagen af första månadenom begynte de till att helga sig, och på åttonde dagen i den månaden gingo de uti Herrans förhus, och helgade Herrans hus åtta dagar, och fullkomnade det på sextonde dagen i första månadenom.
18 Sa’an nan suka tafi wurin Sarki Hezekiya suka faɗa masa, “Mun tsarkake haikalin Ubangiji gaba ɗaya, bagaden ƙone hadaya tare da dukan kayayyakinsa, da tebur don shirya tsarkaken burodi, tare da dukan kayayyakinsa.
Och de gingo in till Konung Hiskia, och sade: Vi hafve renat hela Herrans hus, bränneoffrets altare, och all dess tyg; skådobrödens bord, och all dess tyg;
19 Mun shirya muka kuma tsarkake dukan kayayyakin da Sarki Ahaz ya cire cikin rashin amincinsa yayinda yake sarki. Yanzu suna a gaban bagaden Ubangiji.”
Och all de kärile, som Konung Ahas, då han Konung var, bortkastat hade, då han syndade; dem hafve vi tillredt och helgat, si, de äro för Herrans altare.
20 Da sassafe kashegari Sarki Hezekiya ya tattara manyan birni wuri ɗaya, suka haura zuwa haikalin Ubangiji.
Då var Konung Jehiskia bittida uppe, och församlade de öfversta i stadenom, och gick upp till Herrans hus;
21 Suka kawo bijimai bakwai, raguna bakwai, bunsurai bakwai da kuma awaki mata bakwai a matsayin hadaya don zunubi domin masarauta, domin wuri mai tsarki da kuma domin Yahuda. Sarki ya umarce firistoci, zuriyar Haruna, su miƙa waɗannan a bagaden Ubangiji.
Och hade fram sju stutar, sju vädrar, sju lamb och sju getabockar, till syndoffer, för riket, för helgedomen, och för Juda. Och han sade till Presterna Aarons barn, att de skulle offra på Herrans altare.
22 Saboda haka suka yayyanka bijiman, firistoci suka karɓi jinin suka yayyafa a kan bagade. Suka kuma yanka ragunan suka yayyafa jinin a bagaden. Haka kuma suka yanka’yan ragunan suka yayyafa jinin a bagaden.
Då slagtade de stutarna, och Presterna togo blodet, och stänkte det på altaret; och slagtade vädrarna, och stänkte blodet på altaret; och slagtade lamben, och stänkte blodet på altaret;
23 Aka kawo awaki domin hadaya don zunubi a gaban sarki da taron, suka kuwa ɗibiya hannuwansu a kansu.
Och hade bockarna fram till syndoffer inför Konungen och menighetena, och lade sina händer på dem;
24 Sa’an nan firistoci suka yayyanka awakin suka miƙa jininsu a bagade domin hadaya don zunubi don kafara saboda dukan Isra’ila, domin sarki ya umarta a yi hadaya ta ƙonawa da hadaya don zunubi domin dukan Isra’ila.
Och Presterna slagtade dem, och stänkte deras blod på altaret, till att försona hela Israel; ty Konungen hade befallt offra bränneoffer och syndoffer för hela Israel.
25 Sarki Hezekiya ya ajiye Lawiyawa a cikin haikalin Ubangiji tare da ganguna, garayu da molaye, yadda Dawuda da Gad mai duba na sarki da kuma annabi Natan suka tsara. Ubangiji ne ya umarta wannan ta wurin annabawansa.
Och han satte Leviterna i Herrans hus med cymbaler, psaltare och harpor, såsom David det befallt hade, och Gad, Konungens Siare, och den Propheten Nathan; ty det var Herrans bud igenom hans Propheter.
26 Saboda haka Lawiyawa suka tsaya a shirye tare da kayan kiɗin Dawuda, firistoci kuma tare da ƙahoninsu.
Och Leviterna stodo med Davids strängaspel, och Presterna med trummeter.
27 Hezekiya ya ba da umarni a miƙa hadaya ta ƙonawa a kan bagade. Yayinda aka fara miƙawa, ana rerawa ga Ubangiji, tare da bushe-bushe da kiɗe-kiɗen kayan waƙa na Dawuda sarkin Isra’ila.
Och Hiskia bad dem göra bränneoffer på altarena; och som man begynte bränneoffret, begyntes ock på Herrans sång och trummeterna, och med mångahanda Davids, Israels Konungs, strängaspel.
28 Dukan taron suka durƙusa suka yi sujada, yayinda mawaƙa suke rerawa, ana kuma busa ƙahoni, dukan wannan ya ci gaba sai da aka gama miƙa hadaya ta ƙonawa.
Och hela menigheten tillbad; Och sångarenas sång och trummeternas trummetning varade allt intilldess bränneoffret öfverfaret var.
29 Sa’ad da aka gama miƙawa, sai sarki da mutanen da suke tare da shi suka durƙusa suka yi sujada.
Då nu bränneoffret gjordt var, bugade sig Konungen, och alle de som när honom vid handen voro, och tillbådo.
30 Sarki Hezekiya da fadawansa suka umarci Lawiyawa su yabi Ubangiji da kalmomin Dawuda da na Asaf mai duba. Saboda haka suka rera yabai da murna, suka sunkuyar da kawunansu suka yi sujada.
Och Konung Jehiskia, med öfverstarna, bad Leviterna lofva Herran, med Davids och den Siarens Assaphs dikt. Och de lofvade honom med glädje; och de böjde sig, och tillbådo.
31 Sa’an nan Hezekiya ya ce, “Yanzu kun keɓe kanku ga Ubangiji. Ku zo ku kuma kawo hadayu da hadayun godiya zuwa ga haikalin Ubangiji.” Saboda haka taron suka kawo hadayu da hadayun godiya, da kuma dukan waɗanda suke da niyya suka kawo hadayun ƙonawa.
Och Jehiskia svarade, och sade: Nu hafven I fyllt edra händer Herranom; går fram och bärer fram offer och lofoffer till Herrans hus. Och menigheten bar fram offer och lofoffer; och hvar och en af friviljogt hjerta bränneoffer.
32 Yawan hadayun ƙonawan da taron suka kawo, bijimai saba’in ne, raguna ɗari da kuma bunsurai ɗari biyu, dukansu kuwa domin hadayun ƙonawa ga Ubangiji ne.
Och talet på bränneoffret, som menigheten frambar, var sjutio oxar, hundrade vädrar, och tuhundrad lamb; och allt detta till bränneoffer Herranom.
33 Dabbobin da aka tsarkake a matsayi hadayu sun kai bijimai ɗari shida da tumaki da kuma awaki dubu uku.
Och de helgade sexhundrad oxar, och tretusend får.
34 Firistoci fa, suka kāsa sosai don fiɗan dukan dabbobin da za a miƙa don hadayun ƙonawa; saboda haka’yan’uwansu Lawiyawa suka taimake su har aka gama aiki kafin sauran firistoci su sami damar tsarkake kansu. Gama Lawiyawa sun fi firistoci himma wajen tsarkakewar kansu.
Men Presterna voro för få, och förmådde icke draga hudena af allo bränneoffrena; derföre togo de sina bröder Leviterna, tilldess det verk öfverståndet vardt, och så länge Presterna helgade sig; förty de Leviter stå lätteligare till att helga, än Presterna.
35 Aka kasance da hadayun ƙonawa a yalwace, tare da kitsen hadayun salama da hadayun sha da suke tafe da hadayun ƙonawa. Saboda haka aka sāke kafa hidimar haikalin Ubangiji.
Var också bränneoffret mycket, med det feta af tackoffren, och drickoffret till bränneoffret. Alltså vardt ämbetet i Herrans hus redo.
36 Hezekiya da dukan mutane suka yi farin ciki game da abin da Allah ya yi wa mutanensa, domin ya faru farat ɗaya.
Och Jehiskia fröjdade sig med allo folkena, att man var så redo vorden med Gudi; ty det skedde med hastighet.