< 2 Tarihi 26 >

1 Sai dukan mutanen Yahuda suka ɗauki Uzziya wanda yake da shekara goma sha shida da haihuwa, suka naɗa shi sarki a madadin mahaifinsa Amaziya.
And all the people of Judah take Uzziah (and he [is] a son of sixteen years), and cause him to reign instead of his father Amaziah.
2 Shi ne wanda ya sāke gina Elot ya kuma mai da shi ga Yahuda bayan Amaziya ya huta tare da kakanninsa.
He has built Eloth, and restores it to Judah after the king’s lying with his fathers.
3 Uzziya yana da shekara goma sha shida sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara hamsin da biyu. Sunan mahaifiyarsa Yekoliya ce; ita daga Urushalima ce.
Uzziah [is] a son of sixteen years in his reigning, and he has reigned fifty-two years in Jerusalem, and the name of his mother [is] Jecholiah of Jerusalem.
4 Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar dai yadda mahaifinsa Amaziya ya yi.
And he does that which is right in the eyes of YHWH, according to all that his father Amaziah did,
5 Ya nemi Allah a kwanakin Zakariya, wanda ya koyar da shi a tsoron Allah. Muddin ya nemi Ubangiji, Allah ya ba shi nasara.
and he is as one seeking God in the days of Zechariah who has understanding in visions of God: and in the days of his seeking YHWH, God has caused him to prosper.
6 Ya yi yaƙi da Filistiyawa ya kuma rushe katangar Gat, Yabne da kuma Ashdod. Sa’an nan ya sāke gina garuruwa kusa da Ashdod da sauran wurare a cikin Filistiyawa.
And he goes forth and fights with the Philistines, and breaks down the wall of Gath, and the wall of Jabneh, and the wall of Ashdod, and builds cities [around] Ashdod, and among the Philistines.
7 Allah ya taimake shi a kan Filistiyawa da kuma a kan Larabawa waɗanda suke zama a Gur-Ba’al da kuma a kan Meyunawa.
And God helps him against the Philistines, and against the Arabians who are dwelling in Gur-Ba‘al and the Mehunim.
8 Ammonawa suka kawo haraji wa Uzziya, sunan da ya yi kuwa ya bazu har iyakar Masar, domin ya zama mai iko sosai.
And the Ammonites give a present to Uzziah, and his name goes to the entering in of Egypt, for he strengthened himself greatly.
9 Uzziya ya gina hasumiyoyi a Urushalima a Ƙofar Kusurwa, a Ƙofar Kwari da kuma a kusurwar katanga, ya kuma yi musu katanga.
And Uzziah builds towers in Jerusalem, by the Corner Gate, and by the Valley Gate, and by the angle, and strengthens them;
10 Ya gina hasumiyoyi a hamada ya kuma haƙa rijiyoyi masu yawa, gama yana da dabbobi masu yawa a gindin duwatsu da kuma a kwari. Yana da mutane masu yin masa aiki a gonakinsa da gonakin inabinsa a tuddai da kuma a ƙasashe masu dausayi, gama yana son noma.
and he builds towers in the wilderness, and digs many wells, for he had much livestock, both in the low country and in the plain, farmers and vinedressers in the mountains, and in Carmel; for he was a lover of the ground.
11 Uzziya ya kasance da gogaggun mayaƙa, a shirye su fito ɓangarori-ɓangarori bisa ga yawansu yadda Yehiyel magatakarda, da Ma’asehiya jarumi, suka karkasa su bisa ga umarnin Hananiya, ɗaya daga cikin fadawa.
And Uzziah has a force making war, going forth to the host, by troops, in the number of their reckoning by the hand of Jeiel the scribe and Masseiah the officer, by the hand of Hananiah [one] of the heads of the king.
12 Yawan shugabannin iyali a bisa jarumawa sun kai 2,600.
The whole number of heads of the fathers of the mighty men of valor [is] two thousand and six hundred;
13 A ƙarƙashin shugabancinsu akwai mayaƙa 307,500 horarru don yaƙi, mayaƙa masu ƙarfi don su taimaki sarki a kan abokan gābansa.
and by their hand [is] the force of the host—three hundred thousand and seven thousand and five hundred warriors, with mighty power to give help to the king against the enemy.
14 Uzziya ya tanada garkuwoyi, māsu, hulunan kwano, kayan sulke, baka da majajjawa don mayaƙan gaba ɗaya.
And Uzziah prepares for them, for all the host, shields, and spears, and helmets, and coats of mail, and bows, even to stones of the slings.
15 A Urushalima ya yi na’urori da gwanaye suka sarrafa don amfani a hasumiyoyi da kuma a kusurwar kāriya don harbin kibiyoyi da jefan manyan duwatsu. Sunansa ya bazu ko’ina, gama ya sami taimako sosai har ya zama mai iko.
And he makes inventions in Jerusalem—a device of an inventor—to be on the towers, and on the corners, to shoot with arrows and with great stones, and his name goes out to a distance, for he has been wonderfully helped until he has been strong.
16 Amma bayan Uzziya ya zama mai iko, sai ɗaga kai ya kai shi ga fāɗuwa. Bai yi aminci ga Ubangiji Allahnsa ba, ya kuma shiga haikalin Ubangiji don yă ƙone turare a bagaden turare.
And at his being strong his heart has been high to destruction, and he trespasses against his God YHWH, and goes into the temple of YHWH to make incense on the altar of incense.
17 Azariya firist tare da waɗansu firistoci tamanin na Ubangiji masu ƙarfin hali suka bi shi ciki.
And Azariah the priest goes in after him, and with him eighty priests of YHWH, sons of valor,
18 Suka kalubalance shi suka ce, “Ba daidai ba ne, Uzziya, ka ƙone turare ga Ubangiji. Wannan aikin firistoci zuriyar Haruna ne, waɗanda aka tsarkake don ƙone turare. Ka bar wuri mai tsarki, gama ka kasance marar aminci; kuma Ubangiji Allah ba zai girmama ka ba.”
and they stand up against Uzziah the king, and say to him, “[It is] not for you, O Uzziah, to make incense to YHWH, but for priests, sons of Aaron, who are sanctified to make incense; go forth from the sanctuary, for you have trespassed, indeed, for you [will] not [have] honor from YHWH God.”
19 Uzziya wanda yake da farantin wuta a hannunsa a shirye don ƙone turare, ya husata. Yayinda yake fushi da firistocin a gabansu a gaban bagaden turare a haikalin Ubangiji, sai kuturta ta faso a goshinsa.
And Uzziah is angry, and in his hand [is] a censer to make incense, and in his being angry with the priests—the leprosy has risen in his forehead, before the priests, in the house of YHWH, from beside the altar of incense.
20 Sa’ad da Azariya babban firist da dukan sauran firistoci suka dube shi, sai suka ga cewa yana da kuturta a goshinsa, saboda haka suka gaggauta tunkuɗa shi waje nan da nan. Tabbatacce, shi kansa ma ya yi marmari yă bar wurin domin Ubangiji ya buge shi.
And Azariah the head priest looks toward him, and all the priests, and behold, he [is] leprous in his forehead, and they hurry him there, and also he himself has hurried to go out, for YHWH has plagued him.
21 Sarki Uzziya ya kasance da kuturta har ranar mutuwarsa. Ya zauna a gidan da aka ware, da kuturci, aka kuma ware shi daga haikalin Ubangiji. Yotam ɗansa ya lura da fadan ya kuma yi mulkin mutanen ƙasar.
And Uzziah the king is a leper to the day of his death, and inhabits a separate house—a leper, for he has been cut off from the house of YHWH, and his son Jotham [is] over the house of the king, judging the people of the land.
22 Sauran ayyukan mulkin Uzziya daga farko zuwa ƙarshe, suna a rubuce ta hannun annabi Ishaya ɗan Amoz.
And the rest of the matters of Uzziah, the first and the last, Isaiah son of Amoz the prophet has written;
23 Uzziya ya huta da kakanninsa aka kuma binne shi kusa da su a fili don binnewar da take ta sarakuna, domin mutane sun ce, “Yana da kuturta.” Sai Yotam ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
and Uzziah lies with his fathers, and they bury him with his fathers in the field of the burying-place that the kings have, for they said, “He [is] a leper”; and his son Jotham reigns in his stead.

< 2 Tarihi 26 >