< 2 Tarihi 25 >

1 Amaziya yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Yehoyaddin ce; ita daga Urushalima ne.
Amasías tenía veinticinco años cuando comenzó a reinar, y reinó en Jerusalén durante veintinueve años. El nombre de su madre fue Joadan de Jerusalén.
2 Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, amma ba da dukan zuciyarsa ba.
Hizo lo correcto ante los ojos del Señor, pero su corazón no era completamente fiel al Señor.
3 Bayan sarauta ta kahu a ƙarƙashinsa, sai ya kashe hafsoshin da suka kashe mahaifinsa sarki.
Y cuando se hizo fuerte en el reino, mató a aquellos hombres que habían tomado la vida del rey, su padre.
4 Duk da haka bai kashe’ya’yansu maza ba amma ya yi bisa ga abin da yake a rubuce a cikin Doka, a cikin Littafin Musa, inda Ubangiji ya umarta, “Ba za a kashe iyaye saboda’ya’yansu ba; ba kuwa za a kashe’ya’ya saboda iyayensu ba; kowa zai mutu saboda zunubansa ne.”
Pero él no mató a sus hijos, porque mantuvo las órdenes del Señor registradas en el libro de la ley de Moisés, diciendo: Los padres no deben ser condenados a muerte por sus hijos o los hijos por sus padres, pero un hombre debe ser condenado a muerte por el pecado que él mismo ha cometido.
5 Amaziya ya tattara mutanen Yahuda ya kuma ba su aiki bisa ga iyalansu, ya ba da aiki ga shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, a dukan Yahuda da Benyamin. Ya kuma tattara waɗanda suke’yan shekara ashirin da haihuwa ko fiye ya sami mutane dubu ɗari uku da suke a shirye don aikin soja, da suka isa riƙe māshi da garkuwa.
Entonces Amasías reunió a todo Judá y los ordenó a sus familias, incluso a todo Judá y Benjamín, bajo capitanes de miles y capitanes de cientos: y él tenía a los de veinte años o más, y vinieron a trescientos mil de los mejores combatientes, entrenados para la guerra y en el uso de la lanza y escudos.
6 Ya kuma ɗauko sojan haya jarumawa dubu ɗari ɗaya daga Isra’ila a kan talenti ɗari na azurfa.
Y por cien talentos de plata, él consiguió cien mil combatientes de Israel.
7 Amma mutumin Allah ya zo wurinsa ya ce, “Ya sarki, waɗannan runduna daga Isra’ila ba za su tafi tare da kai ba, gama Ubangiji ba ya tare da Isra’ila, ba ya nan da wani cikin mutanen Efraim.
Pero vino a él un hombre de Dios, que decía: Rey, no te acompañe el ejército de Israel; porque el Señor no está con Israel, es decir, los hijos de Efraín.
8 Ko da ma ya tafi ya yi faɗa da ƙwazo a cikin yaƙi, Allah zai tumɓuke shi a gaban abokan gāba, gama Allah yana da iko yă taimaka ko yă tumɓuke.”
Pero si quieres ir hazlo, y sé fuerte en la guerra; Dios te hará caer ante los que luchan contra ti; Dios tiene poder para dar ayuda o para derribar.
9 Amaziya ya tambayi mutumin Allah ya ce, “Amma game da talenti ɗarin da na biya saboda waɗannan rundunonin Isra’ila fa?” Mutumin Allah ya amsa, “Ubangiji zai ba ka fiye da wannan.”
Entonces Amasías dijo al hombre de Dios: ¿Pero qué hacer con respecto a los cien talentos que he dado para la banda armada de Israel? Y el hombre de Dios en respuesta dijo: Dios puede darte mucho más que esto.
10 Saboda haka Amaziya ya sallame rundunonin da suka zo daga Efraim, ya kuma mayar da su gida. Suka husata da Yahuda suka koma gida da fushi sosai.
Entonces, Amasías, separando las tropas armadas que había venido de Efraín, los envió de nuevo; Lo que los enojó mucho con Judá, y volvieron ardiendo de ira.
11 Sa’an nan Amaziya ya yi ƙarfin hali ya jagoranci mayaƙansa zuwa Kwarin Gishiri, inda ya kashe mutanen Seyir dubu goma.
Entonces Amasías se animó, salió a la cabeza de su pueblo y fue al Valle de la Sal, donde mató a diez mil de los hijos de Seir;
12 Mayaƙan Yahuda suka kuma kama mutane dubu goma da rai, suka ɗauke su zuwa ƙwanƙolin dutsen, suka yi ta tunkuɗa su ƙasa suka yi kaca-kaca.
Y diez mil más fueron apresados por los hijos de Israel, y los hicieron subir a la cima de la roca, empujandolos desde la cima de la roca para que sus cuerpos se rompieran por la caída.
13 Ana cikin haka, sai rundunar da Amaziya ya mai da su gida, waɗanda ba a bari suka tafi yaƙin ba, suka kai wa garuruwan Yahuda daga Samariya zuwa Bet-Horon hari. Suka kashe mutane dubu uku suka kwashe ganima mai yawan gaske.
Pero los hombres de la tropa que Amasías envió y no se llevaron a la lucha, atacaron las ciudades de Judá, desde Samaria hasta Bet-horon, y mataron a tres mil de sus habitantes y se los llevaron una gran cantidad de sus bienes.
14 Da Amaziya ya dawo daga kisan mutanen Edom, sai ya dawo da allolin mutanen Seyir. Ya kafa su a matsayin allolinsa, ya rusuna musu, ya kuma miƙa musu hadayun ƙonawa.
Cuando Amasías regresó de la destrucción de los edomitas, tomó a los dioses de los hijos de Seir y los convirtió en sus dioses, adorándolos y quemando ofrendas ante ellos.
15 Fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kan Amaziya, sai ya aiki wani annabi wurinsa wanda ya ce, “Me ya sa ka nemi shawarar allolin mutanen nan, waɗanda ba za su cece mutanensu daga hannunka ba?”
Y la ira del Señor se movió contra Amasías, y le envió un profeta que le dijo: ¿Por qué has ido tras los dioses de las personas que no le han dado la salvación a su propio pueblo de tus manos?
16 Tun yana cikin magana, sai sarki ya ce masa, “Yaushe muka naɗa ka mai ba sarki shawara? Rufe mana baki! Me zai hana a kashe ka?” Sai annabin ya yi shiru, amma ya ce, “Na dai sani Allah ya riga ya shirya zai hallaka ka, saboda ka aikata wannan, ba ka kuma saurari shawarata ba.”
Pero mientras él le estaba hablando, el rey le dijo: ¿Te hemos convertido en uno de los consejeros del rey? No digas más, o será la causa de tu muerte. Entonces el profeta dejó de protestar y dijo: Me queda claro que el propósito de Dios es tu destrucción, porque has hecho esto y no has escuchado mis palabras.
17 Bayan Amaziya sarkin Yahuda ya nemi shawara mashawartansa, sai ya kalubalanci Yowash ɗan Yehoyahaz, ɗan Yehu, sarkin Isra’ila, “Zo mu gamu fuska da fuska.”
Entonces Amasías, rey de Judá, siguiendo la sugerencia de sus siervos, envió a Joás, hijo de Joacaz, hijo de Jehú, rey de Israel, diciendo: Ven, tengamos una reunión cara a cara.
18 Amma Yowash sarkin Isra’ila ya amsa wa Amaziya sarkin Yahuda ya ce, “Wata ƙaya ce a Lebanon, ta aika da saƙo wa itacen al’ul na Lebanon cewa, ‘Ka ba ɗana’yarka aure.’ Sai wani naman jeji na Lebanon ya zo ya tattake ƙayar.
Entonces Joás, rey de Israel, envió a Amasías, rey de Judá, diciendo: El cardo envió al cedro del Líbano, diciendo: Da tu hija a mi hijo por esposa, pero una bestia pasó por bosques en el Líbano, aplastando al cardo bajo sus pies.
19 Ka ce wa kanka cewa ka ci Edom da yaƙi, yanzu kuwa kana fariya da ɗaga kai. Amma tsaya dai a gida! Me ya sa kake neman faɗa kana neman fāɗuwarka da ta Yahuda?”
Tú dices: Mira, yo he vencido a Edom; y tu corazón se enorgullece: ahora quédate en tu país; ¿Por qué causas problemas al ponerte a ti y a Judá en peligro de caída?
20 Amma Amaziya bai saurara ba gama Allah ya yi haka domin yă miƙa su ga Yehowash, domin sun nemi shawarar allolin Edom.
Pero Amasías no le prestó atención; y este era el propósito de Dios, para que él pudiera entregarlos a las manos de Joás, porque habían perseguido a los dioses de Edom.
21 Saboda haka Yowash sarkin Isra’ila ya kai yaƙi. Shi da Amaziya sarkin Yahuda suka fuskanci juna a Bet-Shemesh a Yahuda.
Y así subió Joás, rey de Israel; y él y Amasías, rey de Judá, se encontraron cara a cara en Bet-semes en Judá.
22 Isra’ila ta fatattaki Yahuda, sai kowane mutum ya gudu zuwa gidansa.
Y Judá fue vencido delante de Israel, y huyeron, cada uno a su tienda.
23 Yehowash sarkin Isra’ila ya kama Amaziya sarkin Yahuda, ɗan Yowash, ɗan Ahaziya a Bet-Shemesh. Sa’an nan Yehowash ya kawo shi Urushalima ya farfasa katangar Urushalima daga Ƙofar Efraim har zuwa Ƙofar Kusurwa, wani sashe mai tsawon ƙafa ɗari shida.
Entonces Joás, rey de Israel, hizo a Amasías, rey de Judá, hijo de Joás, hijo de Joacaz, prisionero en Bet-semes, y lo llevó a Jerusalén; y hizo que el muro de Jerusalén fuera derribado de la puerta de Efraín a la puerta en el ángulo, cuatrocientos codos.
24 Ya kwashe dukan zinariya da azurfa da dukan kayayyakin da aka samu a haikalin Allah waɗanda suke a ƙarƙashin kulawar Obed-Edom, da kaya masu daraja na gidan sarki, da waɗanda aka kamo cikin yaƙi, ya kawo Samariya.
Y tomó todo el oro y la plata y todos los vasos que estaban en la casa del Señor, bajo el cuidado de Obed-edom, y todas las riquezas de la casa del rey, así como rehenes y volví a Samaria.
25 Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda ya rayu shekara goma sha biyar bayan mutuwar Yehowash ɗan Yehoyahaz sarkin Isra’ila.
Amasías, hijo de Joás, rey de Judá, continuó viviendo quince años después de la muerte de Joás, hijo de Joacaz, rey de Israel.
26 Game da sauran ayyukan mulkin Amaziya, daga farko zuwa ƙarshe, an rubuta su a littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
Ahora, el resto de los actos de Amasías, comienzo y fin, están registrados en el libro de los reyes de Judá e Israel.
27 Sa’ad da Amaziya ya bar bin Ubangiji, aka shirya masa maƙarƙashiya a Urushalima, sai ya gudu zuwa Lakish, amma suka aiki mutane suka bi shi zuwa Lakish, a can suka kashe shi.
Desde el momento en que Amasías dejó de adorar al Señor, hicieron designios secretos contra él en Jerusalén; y se fue a huir a Laquis, pero enviaron a Laquis tras él y lo mataron allí.
28 Aka dawo da shi a kan doki, aka binne shi tare da kakanninsa a Birnin Yahuda.
Y tomaron su cuerpo a caballo y lo enterraron con sus padres en el pueblo de David.

< 2 Tarihi 25 >