< 2 Tarihi 21 >
1 Yehoshafat ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda. Sai Yehoram ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Och Josaphat af somnade med sina fäder, och vardt begrafven när sina fader uti Davids stad; och hans son Joram vardt Konung i hans stad.
2 ’Yan’uwan Yehoram,’ya’yan Yehoshafat maza su ne, Azariya, Yehiyel, Zakariya, Azariyahu, Mika’ilu da Shefatiya. Dukan waɗannan su ne’ya’yan Yehoshafat sarkin Isra’ila maza.
Och han hade bröder, Josaphats söner, Asaria, Jehiel, Zacharia, Asaria, Michael, och SephatJa; desse voro alle Josaphats, Juda Konungs, barn.
3 Mahaifinsu ya ba su kyautai masu yawa na azurfa da zinariya da kayayyaki masu daraja, tare da birane masu katanga a Yahuda, amma ya ba da mulki ga Yehoram domin shi ne ɗan farinsa.
Och deras fader gaf dem myckna gåfvor i silfver, guld och klenodier, med fasta städer i Juda; men riket gaf han Joram; ty han var den förstfödde.
4 Sa’ad da Yehoram ya kafa kansa sosai a bisa mulkin mahaifinsa, sai ya kashe dukan’yan’uwansa da takobi tare da waɗansu sarakunan Isra’ila.
Då nu Joram uppkom öfver sins faders rike, och vardt dess mägtig, drap han alla sina bröder med svärd, dertill ock somliga af de öfverstar i Israel.
5 Yehoram yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara takwas.
Tu och tretio år gammal var Joram, då han vardt Konung; och regerade åtta år i Jerusalem.
6 Ya yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila, kamar yadda gidan Ahab ta yi, gama ya auri’yar Ahab. Ya aikata mugayen ayyuka a idon Ubangiji.
Och vandrade uti Israels Konungars väg, såsom Achabs hus gjort hade; förty Achabs dotter var hans hustru; och han gjorde hvad Herranom illa behagade.
7 Duk da haka, domin alkawarin da Ubangiji ya yi wa Dawuda, Ubangiji bai so yă hallaka gidan Dawuda ba. Ubangiji ya riga ya yi alkawari zai ci gaba da riƙe fitila domin Dawuda da zuriyarsa har abada.
Men Herren ville icke förderfva Davids hus, för det förbunds skull, som han med David gjort hade, såsom han sagt hade, att gifva honom ena lykto, och hans barnom i alla dagar.
8 A zamanin Yehoram, Edom ya tayar wa Yahuda ya kuma naɗa sarkinsa.
I hans tid föllo de Edomeer af ifrå Juda, och gjorde öfver sig en Konung.
9 Saboda haka Yehoram ya tafi can tare da shugabannin sojojinsa da kuma dukan keken yaƙinsa. Mutanen Edom suka kewaye shi da shugabannin keken yaƙinsa, amma ya tashi ya fatattaki su da dare.
Förty Joram var ditöfver dragen med sina öfverstar, och alla vagnarna med honom; och hade varit uppe om nattena, och slagit de Edomeer allt omkring sig, och öfverstarna för vagnarna.
10 Har yă zuwa yau Edom na tawaye a kan Yahuda. Libna ya yi tawaye a lokaci guda, domin Yehoram ya yashe Ubangiji Allah na kakanninsa.
Derföre föllo de Edomeer af ifrå Juda, allt intill denna dag. På samma tiden föll ock Libna ifrå honom; ty han öfvergaf Herran sina fäders Gud.
11 Ya gina masujadan kan tudu a tuddan Yahuda, ya kuma sa mutanen Urushalima suka yi karuwanci, ya sa Yahuda suka kauce.
Gjorde han ock höjder på bergen i Juda, och kom dem i Jerusalem till horeri, och förförde Juda.
12 Yehoram ya sami wasiƙa daga Iliya annabi, wadda ta ce, “Ga abin da Ubangiji Allah na kakanka Dawuda ya ce, ‘Ba ka yi tafiya a hanyoyin mahaifinka Yehoshafat ko Asa sarkin Yahuda ba.
Men en skrifvelse kom till honom ifrå den Propheten Elia, så lydandes: Detta säger Herren dins faders Davids Gud: Derföre, att du icke vandrat hafver uti dins faders Josaphats vägar, icke heller i Asa, Juda Konungs, vägar;
13 Amma ka yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila, ka sa Yahuda ya kauce, ka kuma sa mutanen Urushalima suka yi karuwanci, kamar yadda gidan Ahab ta yi. Ka kuma kashe’yan’uwanka, membobi gidan mahaifinka, mutanen da suka fi ka kirki.
Utan du vandrar uti Israels Konungars väg, och kommer Juda och dem i Jerusalem till horeri, efter Achabs hus horeri; och hafver dertill dräpit dina bröder af dins faders hus, som bättre voro än du;
14 Saboda haka a yanzu Ubangiji yana shirin ya bugi mutanenka,’ya’yanka maza, matanka da kuma kome da yake naka, da bugu mai ƙarfi.
Si, Herren skall slå dig med en stor plågo på ditt folk, på din barn, på dina hustrur, och uppå alla dina ägodelar.
15 Kai kuma za ka kamu da ciwon hanji wanda zai yi ta cinka kowace rana sai har hanjinka sun fito.’”
Och du skall få mycken sjukdom uti dina inelfver, tilldess att dina inelfver skola för sjukdoms skull utgå dag frå dag.
16 Ubangiji ya sa Filistiyawa da Larabawa waɗanda suke zama kusa da Kushawa su yi gāba da Yehoram
Alltså uppväckte Herren emot Joram de Philisteers anda, och de Arabers, som ligga vid Ethiopien.
17 Suka yaƙi Yahuda, suka kai masa hari, suka kwashe dukan abubuwa masu kyau da suka samu a fadan sarki, tare da’ya’yansa maza da kuma matansa. Ba wanda aka bari, sai dai Ahaziya autansa.
Och de drogo upp till Juda, och förstörde det, och förde bort alla håfvor, som för handene voro i Konungshusena; dertill hans söner och hans hustrur, så att honom blef ingen son qvar, förutan Joahas, hans yngste son.
18 Bayan dukan wannan, sai Ubangiji ya sa wa Yehoram cuta marar warkarwa ta ciki.
Och efter allt detta plågade Herren honom i hans inelfver med en sådana sjukdom, som icke stod till botandes.
19 Cikin lokaci, a ƙarshen shekara ta biyu, sai hanjin cikinsa suka fito saboda cutar, ya kuma mutu cikin tsananin zafi. Mutanensa suka hura wuta don girmama shi, kamar yadda suka yi wa kakanninsa.
Och som det nu varade dag frå dag, och då tu års tid förgången var, gingo hans inelfver ut af honom med hans sjukdom; och han blef död af ondom sjukdom; och de gjorde intet brännande öfver honom, såsom de hans fäder gjort hade.
20 Yehoram yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara takwas. Ya mutu, ba ma wanda ya kula, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda, amma ba a makabartan sarakuna ba.
Tu och tretio år gammal var han, då han vardt Konung, och regerade i åtta år i Jerusalem, och vandrade så, att det icke mycket dogde; och de begrofvo honom i Davids stad; dock icke ibland Konungsgrifterna.