< 2 Tarihi 21 >

1 Yehoshafat ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda. Sai Yehoram ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
And Jehoshaphat lies with his fathers, and is buried with his fathers in the City of David, and his son Jehoram reigns in his stead.
2 ’Yan’uwan Yehoram,’ya’yan Yehoshafat maza su ne, Azariya, Yehiyel, Zakariya, Azariyahu, Mika’ilu da Shefatiya. Dukan waɗannan su ne’ya’yan Yehoshafat sarkin Isra’ila maza.
And he has brothers, sons of Jehoshaphat: Azariah, and Jehiel, and Zechariah, and Azariah, and Michael, and Shephatiah; all these [are] sons of Jehoshaphat king of Israel,
3 Mahaifinsu ya ba su kyautai masu yawa na azurfa da zinariya da kayayyaki masu daraja, tare da birane masu katanga a Yahuda, amma ya ba da mulki ga Yehoram domin shi ne ɗan farinsa.
and their father gives to them many gifts of silver and of gold, and of precious things, with fortified cities in Judah, and he has given the kingdom to Jehoram, for he [is] the firstborn.
4 Sa’ad da Yehoram ya kafa kansa sosai a bisa mulkin mahaifinsa, sai ya kashe dukan’yan’uwansa da takobi tare da waɗansu sarakunan Isra’ila.
And Jehoram rises up over the kingdom of his father, and strengthens himself, and slays all his brothers with the sword, and also of the heads of Israel.
5 Yehoram yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara takwas.
Jehoram [is] a son of thirty-two years in his reigning, and he has reigned eight years in Jerusalem,
6 Ya yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila, kamar yadda gidan Ahab ta yi, gama ya auri’yar Ahab. Ya aikata mugayen ayyuka a idon Ubangiji.
and he walks in the way of the kings of Israel, as the house of Ahab did, for a daughter of Ahab has been to him for a wife, and he does evil in the eyes of YHWH,
7 Duk da haka, domin alkawarin da Ubangiji ya yi wa Dawuda, Ubangiji bai so yă hallaka gidan Dawuda ba. Ubangiji ya riga ya yi alkawari zai ci gaba da riƙe fitila domin Dawuda da zuriyarsa har abada.
and YHWH has not been willing to destroy the house of David, for the sake of the covenant that He made with David, and as He had said to give a lamp to him and to his sons [for] all the days.
8 A zamanin Yehoram, Edom ya tayar wa Yahuda ya kuma naɗa sarkinsa.
In his days Edom has revolted from under the hand of Judah, and they cause a king to reign over them;
9 Saboda haka Yehoram ya tafi can tare da shugabannin sojojinsa da kuma dukan keken yaƙinsa. Mutanen Edom suka kewaye shi da shugabannin keken yaƙinsa, amma ya tashi ya fatattaki su da dare.
and Jehoram passes over with his heads, and all the chariots with him, and it comes to pass, he has risen by night and strikes the Edomites who are coming around against him, and the princes of the chariots,
10 Har yă zuwa yau Edom na tawaye a kan Yahuda. Libna ya yi tawaye a lokaci guda, domin Yehoram ya yashe Ubangiji Allah na kakanninsa.
and Edom revolts from under the hand of Judah to this day; then Libnah revolts at that time from under his hand, because he has forsaken YHWH, God of his fathers;
11 Ya gina masujadan kan tudu a tuddan Yahuda, ya kuma sa mutanen Urushalima suka yi karuwanci, ya sa Yahuda suka kauce.
also, he has made high places on the mountains of Judah, and causes the inhabitants of Jerusalem to commit whoredom, and compels Judah.
12 Yehoram ya sami wasiƙa daga Iliya annabi, wadda ta ce, “Ga abin da Ubangiji Allah na kakanka Dawuda ya ce, ‘Ba ka yi tafiya a hanyoyin mahaifinka Yehoshafat ko Asa sarkin Yahuda ba.
And a writing from Elijah the prophet comes to him, saying, “Thus said YHWH, God of your father David: Because that you have not walked in the ways of your father Jehoshaphat, and in the ways of Asa king of Judah,
13 Amma ka yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila, ka sa Yahuda ya kauce, ka kuma sa mutanen Urushalima suka yi karuwanci, kamar yadda gidan Ahab ta yi. Ka kuma kashe’yan’uwanka, membobi gidan mahaifinka, mutanen da suka fi ka kirki.
and you walk in the way of the kings of Israel, and cause Judah and the inhabitants of Jerusalem to commit whoredom like the whoredoms of the house of Ahab, and also your brothers, the house of your father, who are better than yourself, you have slain;
14 Saboda haka a yanzu Ubangiji yana shirin ya bugi mutanenka,’ya’yanka maza, matanka da kuma kome da yake naka, da bugu mai ƙarfi.
behold, YHWH is striking [with] a great striking among your people, and among your sons, and among your wives, and among all your goods—
15 Kai kuma za ka kamu da ciwon hanji wanda zai yi ta cinka kowace rana sai har hanjinka sun fito.’”
and you, with many sicknesses, with disease of your bowels, until your bowels come out by the sickness, day by day.”
16 Ubangiji ya sa Filistiyawa da Larabawa waɗanda suke zama kusa da Kushawa su yi gāba da Yehoram
And YHWH wakes up against Jehoram the spirit of the Philistines and of the Arabians, who [are] beside the Cushim,
17 Suka yaƙi Yahuda, suka kai masa hari, suka kwashe dukan abubuwa masu kyau da suka samu a fadan sarki, tare da’ya’yansa maza da kuma matansa. Ba wanda aka bari, sai dai Ahaziya autansa.
and they come up into Judah, and break into it, and take captive all the substance that is found at the house of the king, and also his sons, and his wives, and there has not been left to him a son except Jehoahaz the youngest of his sons.
18 Bayan dukan wannan, sai Ubangiji ya sa wa Yehoram cuta marar warkarwa ta ciki.
And after all this YHWH has plagued him in his bowels by a disease for which there is no healing,
19 Cikin lokaci, a ƙarshen shekara ta biyu, sai hanjin cikinsa suka fito saboda cutar, ya kuma mutu cikin tsananin zafi. Mutanensa suka hura wuta don girmama shi, kamar yadda suka yi wa kakanninsa.
and it comes to pass, from days to days, and at the time of the going out of the end of two years, his bowels have gone out with his sickness, and he dies of severe diseases, and his people have not made for him a burning like the burning of his fathers.
20 Yehoram yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara takwas. Ya mutu, ba ma wanda ya kula, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda, amma ba a makabartan sarakuna ba.
He was a son of thirty-two [years] in his reigning, and he has reigned eight years in Jerusalem, and he goes without desire, and they bury him in the City of David, and not in the graves of the kings.

< 2 Tarihi 21 >