< 2 Tarihi 13 >

1 A shekara ta sha takwas ta sarautar Yerobowam, Abiya ya zama sarkin Yahuda,
In the eighteenth year of king Jeroboam began Abijah to reign over Judah.
2 ya kuma yi mulki a Urushalima shekaru uku. Sunan mahaifiyarsa Mikahiya ce,’yar Uriyel na Gibeya. Aka kasance da yaƙe-yaƙe tsakanin Abiya da Yerobowam.
He reigned three years in Jerusalem; and his mother's name was Michaiah, the daughter of Uriel of Gibeah. And there was war between Abijah and Jeroboam.
3 Abiya ya tafi yaƙi tare da mayaƙa dubu ɗari huɗu jarumawa, Yerobowam kuwa ya ja dāgār yaƙi a kan Abiya da mayaƙa dubu ɗari takwas jarumawa.
And Abijah began the war with an army of men of war, four hundred thousand chosen men; and Jeroboam set the battle in array against him with eight hundred thousand chosen men, mighty men of valour.
4 Abiya ya tsaya a Dutsen Zemarayim, a ƙasar tudu ta Efraim ya ce, “Yerobowam da dukan Isra’ila, ku saurare ni!
And Abijah stood up on the top of mount Zemaraim, which is in mount Ephraim, and said, Hear me, Jeroboam, and all Israel!
5 Ba ku san cewa Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ba da sarautar Isra’ila ga Dawuda da zuriyarsa har abada ta wurin alkawarin gishiri ba?
Ought ye not to know that Jehovah the God of Israel gave the kingdom over Israel to David for ever, to him and to his sons [by] a covenant of salt?
6 Duk da haka Yerobowam ɗan Nebat, ma’aikacin Solomon ɗan Dawuda, ya tayar wa maigidansa,
But Jeroboam the son of Nebat, the servant of Solomon the son of David, rose up and rebelled against his lord.
7 sai ya tara wa kansa’yan iska da mugayen mutane suka yi gāba da Rehobowam ɗan Solomon. Rehobowam lokacin kuwa ba shi da wayo, don haka bai iya tsai da su ba.
And vain men, sons of Belial, gathered to him and strengthened themselves against Rehoboam the son of Solomon, and Rehoboam was young and faint-hearted, and did not shew himself strong against them.
8 “Yanzu kuna shirin yin tsayayya da mulkin Ubangiji, wanda yake a hannuwan zuriyar Dawuda. Tabbatacce ku ƙasaitacciyar mayaƙa ne kuma kuna tare da ku maruƙan zinariyar da Yerobowam ya yi domin su zama allolinku.
And now ye think to shew yourselves strong against the kingdom of Jehovah in the hand of the sons of David; and ye are a great multitude, and ye have with you the golden calves that Jeroboam made you for gods.
9 Ba ku ne kuka kori firistocin Ubangiji,’ya’yan Haruna maza, da Lawiyawa kuka kuma zaɓi firistocinku kamar yadda sauran al’ummai suke yi ba? Duk wanda ya zo ya miƙa ɗan bijimi da raguna bakwai don yă tsarkake kansa, ya zama firist na gumaka ke nan, ba na Allah ba.
Have ye not cast out the priests of Jehovah, the sons of Aaron, and the Levites, and made you priests as the peoples of the lands? whoever comes to consecrate himself with a young bullock and seven rams, he becomes a priest of what is not God.
10 “Gare mu kuwa, Ubangiji shi ne Allah, kuma ba mu yashe shi ba. Firistocin da suke bauta wa Ubangiji’ya’yan Haruna maza ne, Lawiyawa ne kuwa suke taimakonsu.
But as for us, Jehovah is our God, and we have not forsaken him; and the priests that serve Jehovah are the sons of Aaron, and the Levites are at their work:
11 Kowace safiya da kowace yamma sukan miƙa hadayun ƙonawa da turare mai ƙanshi ga Ubangiji. Sukan shirya burodi a tsarkaken tebur mai tsabta, sukan kuma ƙuna fitilu a alkukai kowace yamma. Muna kiyaye ƙa’idodin Ubangiji Allahnmu. Amma ku kun yashe shi.
and they burn to Jehovah every morning and every evening burnt-offerings and sweet incense; the loaves also are set in order upon the pure table; and the candlestick of gold with its lamps to burn every evening: for we keep the charge of Jehovah our God; but ye have forsaken him.
12 Allah yana tare da mu; shi ne shugabanmu. Firistocinsa tare da ƙahoni za su busa kirarin yaƙi a kanku. Mutanen Isra’ila, kada ku yi yaƙi da Ubangiji Allah na kakanninku, gama ba za ku yi nasara ba.”
And behold, we have God with us at our head, and his priests, and the loud-sounding trumpets to sound an alarm against you. Children of Israel, do not fight with Jehovah the God of your fathers; for ye shall not prosper.
13 To, fa, Yerobowam ya aiki mayaƙa su zagaya daga baya, domin yayinda yake a gaban Yahuda, sai’yan kwanto su kasance a bayansu.
But Jeroboam caused an ambush to come about behind them; and they were before Judah, and the ambush behind them.
14 Yahuda ya juya sai ya ga cewa ana yaƙe su gaba da baya. Sai suka yi kuka ga Ubangiji. Firistoci suka busa ƙahoni
And Judah looked back, and behold, they had the battle in front and behind; and they cried to Jehovah, and the priests sounded with the trumpets.
15 mutanen Yahuda kuwa suka tā da kirarin yaƙi. Da ji kirarin yaƙi, Allah ya fatattake Yerobowam da dukan Isra’ila a gaban Abiya da Yahuda.
And the men of Judah gave a shout; and as the men of Judah shouted, it came to pass that God smote Jeroboam and all Israel before Abijah and Judah.
16 Isra’ilawa suka gudu a gaban Yahuda, Allah kuwa ya bashe su a hannuwansu.
And the children of Israel fled before Judah; and God delivered them into their hand.
17 Abiya da mutanensa suka kashe su sosai, har mutum dubu ɗari biyar suka mutu a cikin jarumawan Isra’ila.
And Abijah and his people slew them with a great slaughter; and there fell down slain of Israel five hundred thousand chosen men.
18 Aka cinye mutanen Isra’ila a wannan lokaci, mutanen Yahuda kuwa suka yi nasara domin sun dogara ga Ubangiji Allah na kakanninsu.
And the children of Israel were humbled at that time, and the children of Judah were strengthened, because they relied upon Jehovah the God of their fathers.
19 Abiya ya kori Yerobowam ya kuma ƙwace garuruwan Betel, Yeshana da Efron, tare da ƙauyukan da suke kewaye daga gare shi.
And Abijah pursued after Jeroboam, and took cities from him: Bethel with its dependent villages, and Jeshanah with its dependent villages, and Ephron with its dependent villages.
20 Yerobowam bai sāke yin ƙarfi a zamanin Abiya ba. Ubangiji ya buge shi ya kuma mutu.
And Jeroboam did not recover strength again in the days of Abijah; and Jehovah smote him, and he died.
21 Amma Abiya ya ƙara ƙarfi. Ya auri mata goma sha huɗu, ya kuma kasance da’ya’ya maza ashirin da biyu da kuma’ya’ya mata goma sha shida.
But Abijah strengthened himself, and took fourteen wives, and begot twenty-two sons and sixteen daughters.
22 Sauran ayyukan sauratar Abiya, abin da ya yi da abin da ya faɗa, a rubuce suke a cikin rubuce-rubucen annabi Iddo.
And the rest of the acts of Abijah, and his ways and his sayings, are written in the treatise of the prophet Iddo.

< 2 Tarihi 13 >