< 2 Tarihi 12 >

1 Bayan mulkin Rehobowam ya kahu kamar sarki ya kuma yi ƙarfi, shi da dukan Isra’ila suka yi biris da dokar Ubangiji.
And it comes to pass, at the establishing of the kingdom of Rehoboam, and at his strengthening himself, he has forsaken the Law of YHWH, and all Israel with him.
2 Domin sun yi rashin biyayya ga Ubangiji, saboda haka Shishak sarkin Masar ya yaƙi Urushalima a shekara ta biyar ta Sarki Rehobowam.
And it comes to pass, in the fifth year of King Rehoboam, Shishak king of Egypt has come up against Jerusalem—because they trespassed against YHWH—
3 Da kekunan yaƙi dubu ɗaya da ɗari biyu da kuma mahayan dawakai dubu haɗe da mayaƙan Libiyawa, Sukkatawa da kuma Kushawa waɗanda suka wuce ƙidaya suka zo tare da shi daga Masar,
with one thousand and two hundred chariots, and with sixty thousand horsemen, and there is no number to the people who have come with him out of Egypt—Lubim, Sukkiim, and Cushim—
4 ya ci biranen katanga na Yahuda har zuwa Urushalima.
and he captures the cities of the bulwarks that [are] of Judah, and comes to Jerusalem.
5 Sai annabi Shemahiya ya zo wurin Rehobowam da kuma wajen shugabannin Yahuda waɗanda suka taru a Urushalima don tsoron Shishak, ya kuma faɗa musu, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Kun yi biris da ni; saboda haka, yanzu na bashe ku ga Shishak.’”
And Shemaiah the prophet has come to Rehoboam and the heads of Judah who have been gathered to Jerusalem [to escape] from the presence of Shishak, and says to them, “Thus said YHWH: You have forsaken Me, and also, I have left you in the hand of Shishak”;
6 Shugabannin Isra’ila da sarki suka ƙasƙantar da kansu suka ce, “Ubangiji mai adalci ne.”
and the heads of Israel are humbled—and the king—and they say, “YHWH [is] righteous.”
7 Sa’ad da Ubangiji ya ga sun ƙasƙantar da kansu, sai wannan maganar Ubangiji ta zo wa Shemahiya, “Tun da yake sun ƙasƙantar da kansu, to, ba zan hallaka su ba, amma zan cece su, ba zan kwararo fushina ta hannun Shishak a kan Urushalima ba.
And when YHWH sees that they have been humbled, a word of YHWH has been [sent] to Shemaiah, saying, “They have been humbled; I do not destroy them, and I have given to them as a little thing for an escape, and I do not pour out My fury in Jerusalem by the hand of Shishak;
8 Duk da haka za su zama bayinsa, don su san bambanci tsakanin yin mini bauta da kuma yin wa sarakunan sauran ƙasashe bauta.”
but they become servants to him, and they know My service, and the service of the kingdoms of the lands.”
9 Da Shishak sarkin Masar ya yaƙi Urushalima, sai ya kwashi ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma ma’ajin fadan sarki. Ya kwashe kome da kome, har da garkuwoyin zinariyar da Solomon ya yi.
And Shishak king of Egypt comes up against Jerusalem, and takes the treasures of the house of YHWH and the treasures of the house of the king—he has taken the whole—and he takes the shields of gold that Solomon had made;
10 Sai sarki Rehobowam ya ƙera garkuwoyin tagulla a madadin na zinariya, ya sa su a hannun shugabannin matsara na mashigin gidan sarki.
and King Rehoboam makes shields of bronze in their stead, and has given [them] a charge on the hand of the heads of the runners who are keeping the opening of the house of the king;
11 Duk sa’ad da sarki ya tafi haikalin Ubangiji, masu tsaron sukan tafi tare da shi, suna riƙe da garkuwoyi, daga baya kuma su mai da su a ɗakin tsaro.
and it comes to pass, from the time of the going in of the king to the house of YHWH, the runners have come in and lifted them up, and brought them back to the chamber of the runners.
12 Gama Rehobowam ya ƙasƙantar da kansa, fushin Ubangiji ya bar shi, ba a kuwa hallaka shi ƙaƙaf ba. Tabbatacce an yi’yan abubuwa masu kyau a Yahuda.
And in his being humbled, the wrath of YHWH has turned back from him, so as not to destroy to completion; and also, there have been good things in Judah.
13 Sarki Rehobowam ya kafa kansa daram a Urushalima, ya kuma ci gaba a matsayin sarki. Yana da shekara arba’in da ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara goma sha bakwai a Urushalima, birnin da Ubangiji ya zaɓa daga dukan kabilan Isra’ila wanda zai sa Sunansa. Sunan mahaifiyarsa Na’ama ce, ita mutuniyar Ammon ce.
And King Rehoboam strengthens himself in Jerusalem and reigns; for Rehoboam [is] a son of forty-two years in his reigning, and he has reigned seventeen years in Jerusalem, the city that YHWH has chosen to put His Name there, out of all the tribes of Israel, and the name of his mother [is] Naamah the Ammonitess,
14 Ya aikata mugunta domin bai sa zuciyarsa ga neman Ubangiji ba.
and he does evil, for he has not prepared his heart to seek YHWH.
15 Game da ayyukan mulkin Rehobowam, daga farko zuwa ƙarshe, ba a rubuce suke a tarihin Shemahiya annabi da Iddo mai gani wanda yake zancen zuriyoyi ba? Aka kasance da yaƙe-yaƙe tsakanin Rehobowam da Yerobowam.
And the matters of Rehoboam, the first and the last, are they not written among the matters of Shemaiah the prophet, and of Iddo the seer, concerning genealogy? And the wars of Rehoboam and Jeroboam [are for] all the days;
16 Rehobowam ya huta da kakanninsa aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Abiya ɗansa kuma ya gāje shi a matsayin sarki.
and Rehoboam lies with his fathers, and is buried in the City of David, and his son Abijah reigns in his stead.

< 2 Tarihi 12 >