< 1 Tessalonikawa 2 >

1 Kun sani,’yan’uwa, cewa ziyararmu a gare ku ba tă zama a banza ba.
Para vocês mesmos sabem, irmãos, nossa visita a vocês não foi em vão,
2 Mun riga mun sha wahala, aka kuma zage mu a Filibbi, kamar yadda kuka sani, amma da taimakon Allahnmu muka yi ƙarfin hali muka sanar muku bishararsa duk da matsananciyar gāba.
mas tendo sofrido antes e sido vergonhosamente tratados, como sabem, em Philippi, ousamos em nosso Deus contar-lhes a Boa Nova de Deus em muitos conflitos.
3 Gama roƙon da muke yi bai fito daga kuskure ko munafunci ba, ba kuwa ƙoƙari muke yi mu yaudare ku ba.
Pois nossa exortação não é de erro, nem de impureza, nem de engano.
4 A maimako haka, muna magana ne kamar mutanen da Allah ya amince yă danƙa musu amanar wannan bishara. Ba ma ƙoƙari mu gamshi mutane sai dai Allah, mai auna zukatanmu.
Mas mesmo que tenhamos sido aprovados por Deus para receber a Boa Nova, assim falamos - não como homens agradáveis, mas Deus, que testa nossos corações.
5 Kun san ba ma taɓa yin daɗin baki ko mu yi ƙoƙarin kasance da halin kwaɗayin da muke ɓoyewa, Allah shi ne shaidarmu.
Pois não fomos encontrados em nenhum momento usando palavras de bajulação, como você sabe, nem um manto de cobiça (Deus é testemunha),
6 Ba ma neman yabo daga wurin mutane, ko a gare ku, ko ga waɗansu. A matsayinmu na manzannin Kiristi da mun so, da mun nawaita muku,
nem buscando glória dos homens (nem de você nem de outros), quando poderíamos ter reivindicado autoridade como apóstolos de Cristo.
7 amma muka kasance masu sauƙinkai a cikinku, kamar yadda mahaifiya take lura da ƙananan’ya’yanta.
Mas nós fomos gentis entre vocês, como uma mãe lactante cuida de seus próprios filhos.
8 Muka ƙaunace ku ƙwarai har muka ji daɗin bayyana muku, ba bisharar Allah kaɗai ba amma har rayukanmu ma, domin kun zama ƙaunatattu a gare mu.
Mesmo assim, desejando carinhosamente por você, tivemos o prazer de lhe transmitir não somente a Boa Nova de Deus, mas também nossas próprias almas, porque você se tornou muito querido para nós.
9 Ba shakka kuna iya tunawa,’yan’uwa, famarmu da kuma wahalarmu; mun yi aiki dare da rana don kada mu zama nauyi wa wani yayinda muke muku wa’azin bisharar Allah.
Para vocês se lembram, irmãos, de nosso trabalho e trabalho; para trabalhar noite e dia, para não sobrecarregar nenhum de vocês, nós lhes pregamos a Boa Nova de Deus.
10 Ku shaidu ne, haka ma Allah, na yadda muka yi zaman tsarki, adalci da kuma marar aibi a cikinku, ku da kuka ba da gaskiya.
Vós sois testemunhas com Deus de quão santos, justos e irrepreensíveis nos comportamos para com vocês que acreditam.
11 Gama kun san cewa mun bi da kowannenku yadda mahaifi yakan yi da’ya’yansa,
Como vocês sabem, nós exortamos, confortamos e imploramos a cada um de vocês, como um pai faz com seus próprios filhos,
12 muna ƙarfafa ku, muna ta’azantar da ku, muna kuma gargaɗe ku ku yi rayuwar da za tă cancanci Allah, wanda ya kira ku zuwa mulkinsa da kuma ɗaukakarsa.
para que caminhem dignamente de Deus, que os chama para seu próprio Reino e glória.
13 Muna kuma gode wa Allah ba fasawa domin, sa’ad da kuka karɓi maganar Allah, wadda kuka ji daga gare mu, kun karɓe ta ba kamar maganar mutane ba, sai dai kamar yadda take, maganar Allah wadda take aiki a cikinku ku da kuka ba da gaskiya.
Por esta causa também agradecemos a Deus sem cessar que, quando você recebeu de nós a palavra de Deus, você a aceitou não como a palavra dos homens, mas como é na verdade, a palavra de Deus, que também funciona em você que acredita.
14 Gama ku,’yan’uwa, kun zama masu koyi da ikkilisiyoyin Allah a Yahudiya waɗanda suke cikin Kiristi Yesu. Kun sha wahala a hannun mutanen ƙasarku kamar yadda ikkilisiyoyin nan ma suka sha a hannun Yahudawa,
Para vocês, irmãos, tornaram-se imitadores das assembléias de Deus que estão na Judéia em Cristo Jesus; pois vocês também sofreram as mesmas coisas de seus próprios compatriotas, assim como eles sofreram dos judeus
15 waɗanda suka kashe Ubangiji Yesu da annabawa suka kuma kore mu. Ba sa yin aikin da Allah yake so, masu gāba ne kuwa da dukan mutane
que mataram tanto o Senhor Jesus quanto seus próprios profetas, e nos expulsaram, e não agradam a Deus, e são contrários a todos os homens,
16 suna ƙoƙarin hana mu yin magana ga Al’ummai don kada su sami ceto. Ta haka kullum suke ƙara tara tsibin zunubansu. Fushin Allah ya aukar musu a ƙarshe.
proibindo-nos de falar aos gentios para que eles possam ser salvos, para encher seus pecados sempre. Mas a ira chegou sobre eles até o extremo.
17 Amma,’yan’uwa, sa’ad da aka raba mu da ku na ɗan lokaci (a jiki, ba a tunani ba), daga cikin marmarinmu mai tsanani mun yi duk abin da muke iya yi mu gan ku.
Mas nós, irmãos, sendo enlutados por uma curta temporada na presença, não no coração, tentamos ainda mais ver seu rosto com grande desejo,
18 Gama mun so mu zo wurinku, tabbatacce ni, Bulus, na yi ƙoƙari sau da sau, amma Shaiɗan ya hana mu.
porque queríamos ir até você - eu, Paulo, uma e outra vez - mas Satanás nos impediu.
19 Gama mene ne begenmu, farin cikinmu, ko kuma rawanin da zai zama mana abin ɗaukaka a gaban Ubangijinmu Yesu sa’ad da ya dawo? Ba ku ba ne?
Para que nossa esperança, ou alegria, ou coroa de regozijo? Não é mesmo você, diante de nosso Senhor Jesus em sua vinda?
20 Tabbatacce, ku ne ɗaukakarmu da kuma farin cikinmu.
Pois vós sois nossa glória e nossa alegria.

< 1 Tessalonikawa 2 >