< 1 Tessalonikawa 2 >

1 Kun sani,’yan’uwa, cewa ziyararmu a gare ku ba tă zama a banza ba.
Yes, Brothers, you yourselves know that your reception of us was not without result.
2 Mun riga mun sha wahala, aka kuma zage mu a Filibbi, kamar yadda kuka sani, amma da taimakon Allahnmu muka yi ƙarfin hali muka sanar muku bishararsa duk da matsananciyar gāba.
For, although we had experienced suffering and ill-treatment, as you know, at Philippi, we had the courage, by the help of our God, to tell you God’s Good News in spite of great opposition.
3 Gama roƙon da muke yi bai fito daga kuskure ko munafunci ba, ba kuwa ƙoƙari muke yi mu yaudare ku ba.
Our appeal to you was not based on a delusion, nor was it made from unworthy motives, or with any intention of misleading you.
4 A maimako haka, muna magana ne kamar mutanen da Allah ya amince yă danƙa musu amanar wannan bishara. Ba ma ƙoƙari mu gamshi mutane sai dai Allah, mai auna zukatanmu.
But, having been found worthy by God to be entrusted with the Good News, therefore we tell it; with a view to please, not men, but God who proves our hearts.
5 Kun san ba ma taɓa yin daɗin baki ko mu yi ƙoƙarin kasance da halin kwaɗayin da muke ɓoyewa, Allah shi ne shaidarmu.
Never at any time, as you know, did we use the language of flattery, or make false professions in order to hide selfish aims. God will bear witness to that.
6 Ba ma neman yabo daga wurin mutane, ko a gare ku, ko ga waɗansu. A matsayinmu na manzannin Kiristi da mun so, da mun nawaita muku,
Nor did we seek to win honour from men, whether from you or from others, although, as Apostles of Christ, we might have burdened you with our support.
7 amma muka kasance masu sauƙinkai a cikinku, kamar yadda mahaifiya take lura da ƙananan’ya’yanta.
But we lived among you with the simplicity of a child; we were like a woman nursing her own children.
8 Muka ƙaunace ku ƙwarai har muka ji daɗin bayyana muku, ba bisharar Allah kaɗai ba amma har rayukanmu ma, domin kun zama ƙaunatattu a gare mu.
In our strong affection for you, that seemed to us the best way of sharing with you, not only God’s Good news, but our very lives as well — so dear had you become to us.
9 Ba shakka kuna iya tunawa,’yan’uwa, famarmu da kuma wahalarmu; mun yi aiki dare da rana don kada mu zama nauyi wa wani yayinda muke muku wa’azin bisharar Allah.
You will not have forgotten, Brothers, our labour and toil. Night and day we used to work at our trades, so as not be a burden to any of you, while we proclaimed to you God’s Good News.
10 Ku shaidu ne, haka ma Allah, na yadda muka yi zaman tsarki, adalci da kuma marar aibi a cikinku, ku da kuka ba da gaskiya.
You will bear witness, and God also, that our relations with you who believed in Christ were pure, and upright, and beyond reproach.
11 Gama kun san cewa mun bi da kowannenku yadda mahaifi yakan yi da’ya’yansa,
Indeed, you know that, like a father with his own children, we used to encourage and comfort every one of you, and solemnly plead with you;
12 muna ƙarfafa ku, muna ta’azantar da ku, muna kuma gargaɗe ku ku yi rayuwar da za tă cancanci Allah, wanda ya kira ku zuwa mulkinsa da kuma ɗaukakarsa.
so that you should make your daily lives worthy of God who is calling you into the glory of his Kingdom.
13 Muna kuma gode wa Allah ba fasawa domin, sa’ad da kuka karɓi maganar Allah, wadda kuka ji daga gare mu, kun karɓe ta ba kamar maganar mutane ba, sai dai kamar yadda take, maganar Allah wadda take aiki a cikinku ku da kuka ba da gaskiya.
This, too, is a reason why we, on our part, are continually thanking God — because, in receiving the teaching that you had from us, you accepted it, not as the teaching of man, but as what it really is — the teaching of God, which is even now doing its work within you who believe in Christ.
14 Gama ku,’yan’uwa, kun zama masu koyi da ikkilisiyoyin Allah a Yahudiya waɗanda suke cikin Kiristi Yesu. Kun sha wahala a hannun mutanen ƙasarku kamar yadda ikkilisiyoyin nan ma suka sha a hannun Yahudawa,
For you, Brothers, began to follow the example of the Churches of God in Judea which are in union with Jesus Christ; you, in your turn, suffering at the hands of your fellow-citizens, in the same way as those Churches did at the hands of the Jews —
15 waɗanda suka kashe Ubangiji Yesu da annabawa suka kuma kore mu. Ba sa yin aikin da Allah yake so, masu gāba ne kuwa da dukan mutane
The men who killed both the Lord Jesus and the Prophets, and persecuted us also. They do not try to please God, and they are enemies to all mankind,
16 suna ƙoƙarin hana mu yin magana ga Al’ummai don kada su sami ceto. Ta haka kullum suke ƙara tara tsibin zunubansu. Fushin Allah ya aukar musu a ƙarshe.
for they would prevent us from speaking to the Gentiles with a view to their Salvation, and thus are always ‘filling up the measure of their iniquity.’ But the Wrath of God has come upon them to the full!
17 Amma,’yan’uwa, sa’ad da aka raba mu da ku na ɗan lokaci (a jiki, ba a tunani ba), daga cikin marmarinmu mai tsanani mun yi duk abin da muke iya yi mu gan ku.
As for ourselves, Brothers, our having been bereaved of you even for a short time — though in body only, and not in spirit — made us all the more eager to see your faces again; and the longing to do so was strong upon us.
18 Gama mun so mu zo wurinku, tabbatacce ni, Bulus, na yi ƙoƙari sau da sau, amma Shaiɗan ya hana mu.
That was why we made up our minds to go and see you — at least I, Paul, did, more than once — but Satan put difficulties in our way.
19 Gama mene ne begenmu, farin cikinmu, ko kuma rawanin da zai zama mana abin ɗaukaka a gaban Ubangijinmu Yesu sa’ad da ya dawo? Ba ku ba ne?
For what hope or joy will be ours, or what crown shall we have to boast of, in the presence of our Lord Jesus, at his Coming, if it be not you?
20 Tabbatacce, ku ne ɗaukakarmu da kuma farin cikinmu.
You are our pride and our delight!

< 1 Tessalonikawa 2 >