< 1 Tessalonikawa 2 >

1 Kun sani,’yan’uwa, cewa ziyararmu a gare ku ba tă zama a banza ba.
For, yourselves, know, brethren, our entrance which was unto you—that it hath not proved void;
2 Mun riga mun sha wahala, aka kuma zage mu a Filibbi, kamar yadda kuka sani, amma da taimakon Allahnmu muka yi ƙarfin hali muka sanar muku bishararsa duk da matsananciyar gāba.
But, though we had previously suffered, and been insulted, even as ye know, in Philippi, we waxed bold in our God to speak unto you the glad-message of God with much conflict.
3 Gama roƙon da muke yi bai fito daga kuskure ko munafunci ba, ba kuwa ƙoƙari muke yi mu yaudare ku ba.
For, our exhortation, is not of error, nor of uncleanness, nor in guile,
4 A maimako haka, muna magana ne kamar mutanen da Allah ya amince yă danƙa musu amanar wannan bishara. Ba ma ƙoƙari mu gamshi mutane sai dai Allah, mai auna zukatanmu.
But, even as we have been approved by God, to be entrusted with the glad-message, so, we speak, —not as, unto men, giving pleasure, but unto God—who proveth our hearts.
5 Kun san ba ma taɓa yin daɗin baki ko mu yi ƙoƙarin kasance da halin kwaɗayin da muke ɓoyewa, Allah shi ne shaidarmu.
For neither at any time were we found, using words of flattery, —even as ye know, nor a pretext for greed—God, is witness!
6 Ba ma neman yabo daga wurin mutane, ko a gare ku, ko ga waɗansu. A matsayinmu na manzannin Kiristi da mun so, da mun nawaita muku,
Nor, of men, seeking glory—either from you, or from others, though we could have assumed, dignity, as Apostles of Christ;
7 amma muka kasance masu sauƙinkai a cikinku, kamar yadda mahaifiya take lura da ƙananan’ya’yanta.
But we became gentle in your midst, —as though, a nursing mother, had been cherishing her own children:
8 Muka ƙaunace ku ƙwarai har muka ji daɗin bayyana muku, ba bisharar Allah kaɗai ba amma har rayukanmu ma, domin kun zama ƙaunatattu a gare mu.
Thus, yearning after you, we could have been well-pleased to impart unto you—not only the glad-message of God, but, our own lives also, —because, very dear to us, had ye become.
9 Ba shakka kuna iya tunawa,’yan’uwa, famarmu da kuma wahalarmu; mun yi aiki dare da rana don kada mu zama nauyi wa wani yayinda muke muku wa’azin bisharar Allah.
For ye remember, brethren, our toil and hardship: night and day, working, so as not to be a burden unto any of you, we proclaimed unto you the glad-message of God,
10 Ku shaidu ne, haka ma Allah, na yadda muka yi zaman tsarki, adalci da kuma marar aibi a cikinku, ku da kuka ba da gaskiya.
Ye, are witnesses—God also, how kindly and righteously and blamelessly, unto you who were believing, we were found to behave;
11 Gama kun san cewa mun bi da kowannenku yadda mahaifi yakan yi da’ya’yansa,
Even as ye know how, unto each one of you, we were as a father unto his own children, consoling you, and soothing, and calling to witness, —
12 muna ƙarfafa ku, muna ta’azantar da ku, muna kuma gargaɗe ku ku yi rayuwar da za tă cancanci Allah, wanda ya kira ku zuwa mulkinsa da kuma ɗaukakarsa.
To the end ye might be walking in a manner worthy of God, who is calling you unto his own kingdom and glory,
13 Muna kuma gode wa Allah ba fasawa domin, sa’ad da kuka karɓi maganar Allah, wadda kuka ji daga gare mu, kun karɓe ta ba kamar maganar mutane ba, sai dai kamar yadda take, maganar Allah wadda take aiki a cikinku ku da kuka ba da gaskiya.
And, for this cause, we, are also giving thanks unto God unceasingly, that, when ye received a spoken word from us—which was God’s, ye welcomed it—not as a human word, but, even as it truly is, a divine word, —which is also inwardly working itself in you who believe.
14 Gama ku,’yan’uwa, kun zama masu koyi da ikkilisiyoyin Allah a Yahudiya waɗanda suke cikin Kiristi Yesu. Kun sha wahala a hannun mutanen ƙasarku kamar yadda ikkilisiyoyin nan ma suka sha a hannun Yahudawa,
For, ye, became, imitators, brethren, of the assemblies of God which are in Judaea, in Christ Jesus, in that, the same things, ye, also suffered by your own fellow-countrymen, even as, they, also by the Jews:
15 waɗanda suka kashe Ubangiji Yesu da annabawa suka kuma kore mu. Ba sa yin aikin da Allah yake so, masu gāba ne kuwa da dukan mutane
Who have both slain the, Lord, Jesus—and the prophets, and, us, have persecuted, and, unto God, are displeasing, and, unto all men, are contrary, —
16 suna ƙoƙarin hana mu yin magana ga Al’ummai don kada su sami ceto. Ta haka kullum suke ƙara tara tsibin zunubansu. Fushin Allah ya aukar musu a ƙarshe.
Hindering us from speaking, unto the nations, that they might be saved, to the filling up of their own sins, continually; but anger hath overtaken them at length.
17 Amma,’yan’uwa, sa’ad da aka raba mu da ku na ɗan lokaci (a jiki, ba a tunani ba), daga cikin marmarinmu mai tsanani mun yi duk abin da muke iya yi mu gan ku.
Now, we, brethren, having been bereaved away from you, for the season of an hour, —in presence, not in heart, gave more abundant diligence, your face, to behold, with much longing;
18 Gama mun so mu zo wurinku, tabbatacce ni, Bulus, na yi ƙoƙari sau da sau, amma Shaiɗan ya hana mu.
Wherefore, we desired to come unto you—even, I, Paul, both once and again, —and, Satan, thwarted us.
19 Gama mene ne begenmu, farin cikinmu, ko kuma rawanin da zai zama mana abin ɗaukaka a gaban Ubangijinmu Yesu sa’ad da ya dawo? Ba ku ba ne?
For what shall be our hope, or joy, or crown of boasting? Shall not even, ye, before our Lord Jesus, in his Presence?
20 Tabbatacce, ku ne ɗaukakarmu da kuma farin cikinmu.
Ye, in fact, are our glory and joy.

< 1 Tessalonikawa 2 >