< 1 Tessalonikawa 2 >

1 Kun sani,’yan’uwa, cewa ziyararmu a gare ku ba tă zama a banza ba.
For you yourselves know, brothers, that my visit to you did not fail of its purpose;
2 Mun riga mun sha wahala, aka kuma zage mu a Filibbi, kamar yadda kuka sani, amma da taimakon Allahnmu muka yi ƙarfin hali muka sanar muku bishararsa duk da matsananciyar gāba.
for you remember that although I had already borne ill-treatment and insult at Philippi, I took courage in my God to tell you the gospel of God, in the face of much opposition.
3 Gama roƙon da muke yi bai fito daga kuskure ko munafunci ba, ba kuwa ƙoƙari muke yi mu yaudare ku ba.
For my preaching was not grounded on a delusion, or on impure motives, on in deceit.
4 A maimako haka, muna magana ne kamar mutanen da Allah ya amince yă danƙa musu amanar wannan bishara. Ba ma ƙoƙari mu gamshi mutane sai dai Allah, mai auna zukatanmu.
But as my fitness to be entrusted with the gospel has been tested and approved by God, I so speak, not to please men, but to please God, who is testing my motives.
5 Kun san ba ma taɓa yin daɗin baki ko mu yi ƙoƙarin kasance da halin kwaɗayin da muke ɓoyewa, Allah shi ne shaidarmu.
For as you well know, I never resorted to flattery, nor to any pretext for enriching myself. God is my witness!
6 Ba ma neman yabo daga wurin mutane, ko a gare ku, ko ga waɗansu. A matsayinmu na manzannin Kiristi da mun so, da mun nawaita muku,
Now was I seeking glory from men, either yourselves or others, although I might have exercised authority as Christ’s apostle.
7 amma muka kasance masu sauƙinkai a cikinku, kamar yadda mahaifiya take lura da ƙananan’ya’yanta.
On the contrary I showed myself among you as gentle as a mother, when she tenderly nurses her own children.
8 Muka ƙaunace ku ƙwarai har muka ji daɗin bayyana muku, ba bisharar Allah kaɗai ba amma har rayukanmu ma, domin kun zama ƙaunatattu a gare mu.
So in my fond affection it was my joy to give you, not only the gospel of God, but my very life also, because you had become dear to me.
9 Ba shakka kuna iya tunawa,’yan’uwa, famarmu da kuma wahalarmu; mun yi aiki dare da rana don kada mu zama nauyi wa wani yayinda muke muku wa’azin bisharar Allah.
You recall, brothers, my labor and toil; how, while working at my trade day and night, so as not to become a burden to any of you, I proclaimed to you the gospel of God.
10 Ku shaidu ne, haka ma Allah, na yadda muka yi zaman tsarki, adalci da kuma marar aibi a cikinku, ku da kuka ba da gaskiya.
You are witnesses - and so is God - how pure and just and blameless was my behavior among you believers.
11 Gama kun san cewa mun bi da kowannenku yadda mahaifi yakan yi da’ya’yansa,
You know how I was wont to treat each of you as a father treats his children,
12 muna ƙarfafa ku, muna ta’azantar da ku, muna kuma gargaɗe ku ku yi rayuwar da za tă cancanci Allah, wanda ya kira ku zuwa mulkinsa da kuma ɗaukakarsa.
exhorting and imploring and adjuring each one among you to lead a life worthy of the God who called you into his own kingdom and glory.
13 Muna kuma gode wa Allah ba fasawa domin, sa’ad da kuka karɓi maganar Allah, wadda kuka ji daga gare mu, kun karɓe ta ba kamar maganar mutane ba, sai dai kamar yadda take, maganar Allah wadda take aiki a cikinku ku da kuka ba da gaskiya.
For this reason also I am giving continual thanks to God, because when you heard from me the spoken word of God, you received it not as the word of men, but as the word of God (which in truth it is), who himself is effectually at work in you believe.
14 Gama ku,’yan’uwa, kun zama masu koyi da ikkilisiyoyin Allah a Yahudiya waɗanda suke cikin Kiristi Yesu. Kun sha wahala a hannun mutanen ƙasarku kamar yadda ikkilisiyoyin nan ma suka sha a hannun Yahudawa,
For you, brothers, began to follow the example of the churches of God in Judea, which are in Christ Jesus; and you in your turn suffered at the hands of your fellow citizens persecutions like to those which they endured from the Jews -
15 waɗanda suka kashe Ubangiji Yesu da annabawa suka kuma kore mu. Ba sa yin aikin da Allah yake so, masu gāba ne kuwa da dukan mutane
The men who killed both the Lord Jesus and the prophets, and drove us out - they are displeasing to God, and are the enemies of all mankind.
16 suna ƙoƙarin hana mu yin magana ga Al’ummai don kada su sami ceto. Ta haka kullum suke ƙara tara tsibin zunubansu. Fushin Allah ya aukar musu a ƙarshe.
They forbid me to speak to the Gentiles with a view to their salvation. They continue always to fill up the measure of their sins; but the wrath of God is come upon them to the full!
17 Amma,’yan’uwa, sa’ad da aka raba mu da ku na ɗan lokaci (a jiki, ba a tunani ba), daga cikin marmarinmu mai tsanani mun yi duk abin da muke iya yi mu gan ku.
But I, my brothers, although torn from you for a short season (in presence, not in heart), made eager efforts to behold you face to face with strong longing.
18 Gama mun so mu zo wurinku, tabbatacce ni, Bulus, na yi ƙoƙari sau da sau, amma Shaiɗan ya hana mu.
For that reason I would fain have visited you - I, Paul, again and again - but Satan hindered me.
19 Gama mene ne begenmu, farin cikinmu, ko kuma rawanin da zai zama mana abin ɗaukaka a gaban Ubangijinmu Yesu sa’ad da ya dawo? Ba ku ba ne?
For what is my hope, or joy? What is the victor’s wreath in which I exult? What but your own selves in the presence of our Lord Jesus, at his coming!
20 Tabbatacce, ku ne ɗaukakarmu da kuma farin cikinmu.
For you are my pride and my delight.

< 1 Tessalonikawa 2 >