< 1 Tessalonikawa 2 >

1 Kun sani,’yan’uwa, cewa ziyararmu a gare ku ba tă zama a banza ba.
Nebo vy sami víte, bratří, že příchod náš k vám nebyl daremný.
2 Mun riga mun sha wahala, aka kuma zage mu a Filibbi, kamar yadda kuka sani, amma da taimakon Allahnmu muka yi ƙarfin hali muka sanar muku bishararsa duk da matsananciyar gāba.
Ale i prvé trpěvše, i pohanění snáševše, (jakož víte, ) v městě Filippis, osvobodili jsme se v Bohu svém mluviti vám směle evangelium Boží s mnohými odpory.
3 Gama roƙon da muke yi bai fito daga kuskure ko munafunci ba, ba kuwa ƙoƙari muke yi mu yaudare ku ba.
Napomínání zajisté naše nebylo z podvodu, ani z nečistoty, ani ve lsti.
4 A maimako haka, muna magana ne kamar mutanen da Allah ya amince yă danƙa musu amanar wannan bishara. Ba ma ƙoƙari mu gamshi mutane sai dai Allah, mai auna zukatanmu.
Ale jakož Bůh nás oblíbil, aby nám svěřeno bylo evangelium, takť mluvíme, ne jako lidem se líbíce, ale Bohu, kterýž libuje srdce naše.
5 Kun san ba ma taɓa yin daɗin baki ko mu yi ƙoƙarin kasance da halin kwaɗayin da muke ɓoyewa, Allah shi ne shaidarmu.
Anižť jsme zajisté kdy užívali řeči pochlebné, jakož víte, ani za příčinou něčeho lakomství provodili. Bůhť jest svědek.
6 Ba ma neman yabo daga wurin mutane, ko a gare ku, ko ga waɗansu. A matsayinmu na manzannin Kiristi da mun so, da mun nawaita muku,
Ani jsme hledali od lidí chvály, ani od vás, ani od jiných, ač jsme mohli vás obtěžovati, jako Kristovi apoštolé.
7 amma muka kasance masu sauƙinkai a cikinku, kamar yadda mahaifiya take lura da ƙananan’ya’yanta.
Ale byli jsme tiší mezi vámi, jako když matka chová dítky své.
8 Muka ƙaunace ku ƙwarai har muka ji daɗin bayyana muku, ba bisharar Allah kaɗai ba amma har rayukanmu ma, domin kun zama ƙaunatattu a gare mu.
Tak nakloněni k vám byvše, hotovi jsme byli s velikou chutí vydati vám netoliko evangelium Boží, ale také i duše své, proto že jste nám byli milí.
9 Ba shakka kuna iya tunawa,’yan’uwa, famarmu da kuma wahalarmu; mun yi aiki dare da rana don kada mu zama nauyi wa wani yayinda muke muku wa’azin bisharar Allah.
Nebo pamatujete, bratří, na práci naši a ustávání. Ve dne i v noci zajisté pracovavše, proto abychom žádného z vás neobtěžovali, kázali jsme u vás evangelium Boží.
10 Ku shaidu ne, haka ma Allah, na yadda muka yi zaman tsarki, adalci da kuma marar aibi a cikinku, ku da kuka ba da gaskiya.
Vy jste svědkové i Bůh, žeť jsme svatě, a spravedlivě, a bez úhony obcovali mezi vámi, kteříž jste uvěřili,
11 Gama kun san cewa mun bi da kowannenku yadda mahaifi yakan yi da’ya’yansa,
Jakož víte, že jednoho každého z vás, jako otec dítek svých, napomínali jsme a potěšovali,
12 muna ƙarfafa ku, muna ta’azantar da ku, muna kuma gargaɗe ku ku yi rayuwar da za tă cancanci Allah, wanda ya kira ku zuwa mulkinsa da kuma ɗaukakarsa.
I s osvědčováním, abyste chodili hodně Bohu, kterýž povolal vás do království svého a v slávu.
13 Muna kuma gode wa Allah ba fasawa domin, sa’ad da kuka karɓi maganar Allah, wadda kuka ji daga gare mu, kun karɓe ta ba kamar maganar mutane ba, sai dai kamar yadda take, maganar Allah wadda take aiki a cikinku ku da kuka ba da gaskiya.
Protož i my díky činíme Bohu bez přestání, že přijavše slovo Boží, kteréž jste slyšeli od nás, přijali jste ne jako slovo lidské, ale (jakož v pravdě jest, ) jako slovo Boží, kterýž i dílo své působí v vás věřících.
14 Gama ku,’yan’uwa, kun zama masu koyi da ikkilisiyoyin Allah a Yahudiya waɗanda suke cikin Kiristi Yesu. Kun sha wahala a hannun mutanen ƙasarku kamar yadda ikkilisiyoyin nan ma suka sha a hannun Yahudawa,
Vy zajisté, bratří, následovníci učiněni jste církví Božích, kteréž jsou v Židovstvu v Kristu Ježíši; nebo jste takovéž věci i vy trpěli od svého pokolení, jako i oni od Židů.
15 waɗanda suka kashe Ubangiji Yesu da annabawa suka kuma kore mu. Ba sa yin aikin da Allah yake so, masu gāba ne kuwa da dukan mutane
Kteříž i Pána Ježíše zabili, i své vlastní proroky, a nás vyhnali, a Bohu se nelíbí, a všechněm lidem jsou odporní,
16 suna ƙoƙarin hana mu yin magana ga Al’ummai don kada su sami ceto. Ta haka kullum suke ƙara tara tsibin zunubansu. Fushin Allah ya aukar musu a ƙarshe.
Nedopouštějíce nám mluviti pohanům, aby spaseni byli, aby tak vždy doplňovali hříchy své. Nebo vylit jest na ně hněv konečný.
17 Amma,’yan’uwa, sa’ad da aka raba mu da ku na ɗan lokaci (a jiki, ba a tunani ba), daga cikin marmarinmu mai tsanani mun yi duk abin da muke iya yi mu gan ku.
My pak, bratří, zbaveni byvše vás na chvíli, tělem ne srdcem, opravdověji usilovali jsme viděti tvář vaši s mnohou žádostí.
18 Gama mun so mu zo wurinku, tabbatacce ni, Bulus, na yi ƙoƙari sau da sau, amma Shaiɗan ya hana mu.
Protož chtěli jsme přijíti k vám, (zvláště já Pavel, ) jednou i podruhé, ale překazil nám satan.
19 Gama mene ne begenmu, farin cikinmu, ko kuma rawanin da zai zama mana abin ɗaukaka a gaban Ubangijinmu Yesu sa’ad da ya dawo? Ba ku ba ne?
Nebo která jest naše naděje neb radost aneb koruna chlouby? Zdali ne i vy před oblíčejem Pána našeho Jezukrista v příchodu jeho?
20 Tabbatacce, ku ne ɗaukakarmu da kuma farin cikinmu.
Vy jistě jste sláva naše i radost.

< 1 Tessalonikawa 2 >