< 1 Tessalonikawa 1 >

1 Bulus, Sila da Timoti, Zuwa ga ikkilisiyar Tessalonikawa ta Allah Uba da Ubangiji Yesu Kiristi. Alheri da salama su kasance tare da ku.
To the Thessalonian Church in union with God the Father and the Lord Jesus Christ, from Paul, Silas, and Timothy. May God bless you and give you peace.
2 Kullum muna gode wa Allah dominku duka, muna ambatonku cikin addu’o’inmu.
We always mention you in our prayers and thank God for you all;
3 Muna tunawa da aikinku ba fasawa a gaban Allah da Ubanmu ta wurin bangaskiya, da famar da kuke yi domin ƙauna, da kuma begenku marar gushewa ga Ubangijinmu Yesu Kiristi.
recalling continually before our God and Father the efforts that have resulted from your faith, the toil prompted by your love, and the patient endurance sustained by your hope in our Lord Jesus Christ.
4 Gama mun sani,’yan’uwa, ƙaunatattu na Allah, cewa ya zaɓe ku,
Brothers, whom God loves, we know that he has chosen you,
5 domin bishararmu ba tă zo gare ku da kalmomi kawai ba, amma da iko, da Ruhu Mai Tsarki, da kuma cikakken tabbaci. Kun san irin rayuwar da muka yi a cikinku don amfaninku.
because the Good News that we brought came home to you, not merely as so many words, but with a power and a fulness of conviction due to the Holy Spirit. For you know the life that we lived among you for your good.
6 Har kuka zama masu koyi da mu da kuma Ubangiji; duk da tsananin wahala, kuka karɓi saƙon nan da farin ciki wanda Ruhu Mai Tsarki ya bayar.
And you yourselves began to follow, not only our example, but the Master’s also; and, in spite of much suffering, you welcomed the Message with a joy inspired by the Holy Spirit,
7 Ta haka kuwa kuka zama gurbi ga dukan masu bi a Makidoniya da Akayya.
and so became a pattern to all who believed in Christ throughout Macedonia and Greece.
8 Saƙon Ubangiji ya fito daga gare ku ne ba a Makidoniya da Akayya kaɗai ba bangaskiyarku ga Allah ta zama sananne ko’ina. Saboda haka ba ma bukata mu faɗa wani abu a kai,
For it was from you that the Lord’s Message resounded throughout Macedonia and Greece; and, more than that, your faith in God has become known far and wide; so that there is no need for us to say another word.
9 gama su kansu su suke ba da labari irin karɓar da kuka yi mana. Suna faɗin yadda kuka juyo ga Allah daga gumaka don ku bauta wa Allah rayayye da kuma na gaskiya,
Indeed, in speaking about us, the people themselves tell of the reception you gave us, and how, turning to God from your idols, you became servants of the true and living God,
10 ku kuma jira dawowar Ɗansa daga sama, wanda ya tasa daga matattu, Yesu, wanda ya cece mu daga fushi mai zuwa.
and are now awaiting the return from Heaven of his Son whom he raised from the dead — Jesus, our deliverer from the Coming Wrath.

< 1 Tessalonikawa 1 >