< 1 Sama’ila 9 >

1 An yi wani mutum, attajiri daga kabilar Benyamin, sunansa Kish, ɗan Abiyel, jikan Zeror na iyalin Bekorat daga dangin Afiya.
Živio u ono vrijeme jedan čovjek u Benjaminovu plemenu po imenu Kiš, sin Abiela, sina Serora, sina Bekorata, sina Afijahova; bio je iz plemena Benjaminova, čovjek imućan.
2 Yana da ɗa mai suna Shawulu, wani kyakkyawan saurayi. A cikin mutanen Isra’ila ba wanda ya fi shi kyau, ya kuma fi kowa tsaye.
Imao je sina po imenu Šaula, koji je bio mlad i lijep. Među sinovima Izraelovim nije bilo ljepšega čovjeka od njega: za glavu bijaše viši od svega naroda.
3 To, ana nan sai jakunan Kish mahaifin Shawulu suka ɓace. Kish ya ce wa ɗansa, “Tashi ka tafi tare da wani daga cikin bayi, ku nemo jakunan.”
Uto se Kišu, Šaulovu ocu, izgubilo nekoliko magarica, pa Kiš reče svome sinu Šaulu: “Uzmi sa sobom jednoga momka pa ustani i idi tražiti magarice!”
4 Suka bi ta ƙasar tudu ta Efraim, suka ratsa ta ƙasar Shalisha amma ba su same su ba. Suka bi ta ƙasar Shalim, a can ma ba su same su ba sai suka bi ta ƙasar Benyamin, a can ma ba su same su ba.
I prođoše oni Efrajimovu goru i prođoše zemlju Šališu, ali ne nađoše ništa; prođoše zemlju Šaalim, ali magarica ne bijaše ondje; prođoše i zemlju Benjaminovu, ali ne nađoše ništa.
5 Da suka iso gunduman Zuf, sai Shawulu ya ce wa bawan da yake tare da shi, “Zo mu koma kada mahaifina yă bar damuwa a kan jakuna, yă shiga damuwa game da mu.”
Kad su došli u zemlju Suf, reče Šaul momku koji ga je pratio: “Hajde, vratimo se da se ne bi otac okanio magarica i zabrinuo se za nas!”
6 Amma bawan ya amsa ya ce, “Duba, a wannan gari akwai wani mutumin Allah, ana ganin girmansa ƙwarai kuma duk abin da ya faɗa yakan zama gaskiya. Mu tafi can wurinsa wataƙila zai gaya mana hanyar da za mu bi.”
A on mu odgovori: “Eno, u onom ondje gradu živi čovjek Božji; to je vrlo ugledan čovjek: što god rekne, sve se zacijelo ispunja. Pođimo, dakle, k njemu, možda će nas uputiti u ono zbog čega smo pošli na put.”
7 Shawulu ya ce wa bawan, “Idan muka isa can, me za mu ba wa mutumin? Ga shi abinci guzurinmu duk ya ƙare, ba mu da wani abin da za mu kai wa mutumin Allahn nan. Me muke da shi?”
A Šaul reče svome momku: “Ako zaista pođemo onamo, što ćemo ponijeti čovjeku? Kruha je nestalo u našim torbama, nemamo dara da ponesemo čovjeku Božjem. Što mu možemo dati?”
8 Bawan ya sāke ce masa, “Duba ina da kwatar azurfar da zan ba wa mutumin Allah don yă gaya mana wace hanya ce za mu bi.”
A momak opet progovori i reče Šaulu: “Gle, imam u ruci četvrt šekela srebra: dat ću ga Božjem čovjeku da nas uputi kamo bismo išli.”
9 (A dā a Isra’ila, in wani yana so yă nemi nufin Allah, mutumin yakan ce, “Zo mu tafi wajen mai duba.” Gama wanda ake ce da shi annabi a yanzu, a dā ana kiransa mai duba ne.)
Nekoć se u Izraelu, kad bi išli pitati Boga za savjet, govorilo: “Hajde, pođimo k vidiocu!” Jer koga danas zovu prorokom nekoć se zvao vidjelac. -
10 Shawulu ya ce wa bawansa, “Madalla, zo mu tafi.” Sai suka kama hanya suka nufi birnin da mutumin Allah yake.
Šaul odvrati svome momku: “Dobro veliš. Hajdemo!” I krenuše u grad gdje je živio čovjek Božji.
11 Sa’ad da suke haura tudun zuwa birnin, sai suka sadu da waɗansu’yan mata sun fito za su ɗiban ruwa. Sai suka tambaye su, suka ce, “Mai duba yana nan?”
Kad su se penjali usponom prema gradu, sretoše djevojke koje su izašle da zahvate vode. I zapitaše ih: “Je li gore vidjelac?” -
12 ’Yan matan suka ce, “I, yana nan, ai, ga shi ma a gabanku, ku hanzarta. Shigowarsa ke nan a garin, domin yau mutane za su ba da sadaka a bagade a kan tudu.
One im odgovore ovako: “Jest, vidjelac je pred vama. Upravo je stigao u grad, jer danas narod ima žrtvu na uzvišici.
13 Da zarar kun shiga garin, za ku same shi kafin yă tafi cin abinci a wurin yin sadakar, can kan tudu. Gama jama’a ba za su ci ba, sai ya kai can ya sa albarka a sadakar, sa’an nan waɗanda aka gayyata su ci. Ku haura da sauri, za ku same.”
Čim uđete u grad, naći ćete ga još prije nego što se popne na uzvišicu da sudjeluje na žrtvenoj gozbi. Narod neće jesti dok on ne dođe, jer on mora blagosloviti žrtvu, a onda će tek uzvanici jesti. Zato idite odmah gore, jer ćete ga sada još naći.”
14 Suka haura zuwa birnin, da shigarsu sai ga Sama’ila ya nufo su a hanyarsa ta zuwa kan tudu.
Oni otiđoše gore u grad. Kad su ulazili na vrata, Samuel ih susrete polazeći na uzvišicu.
15 Kafin zuwa Shawulu, Ubangiji ya riga ya bayyana wa Sama’ila ya ce,
A dan prije nego što je Šaul došao bijaše Jahve objavio Samuelu:
16 “Gobe war haka zan aiko maka da wani mutum daga ƙasar Benyamin. Ka keɓe shi shugaban mutanena Isra’ila. Shi zai cece mutanena daga hannun Filistiyawa. Na ga azabar mutanena gama kukansu ya hauro wurina.”
“Sutra u ovo doba poslat ću k tebi čovjeka iz Benjaminove zemlje. Ti ćeš ga pomazati za kneza nad mojim narodom Izraelom. On će izbaviti moj narod iz ruke filistejske. Vidio sam nevolju svoga naroda i njegov je vapaj dopro do mene.”
17 Da Sama’ila ya hangi Shawulu, Ubangiji ya ce masa, “Ga mutumin da na yi maka magana, shi ne zai bi da mutanena.”
A kad je Samuel ugledao Šaula, Jahve mu progovori: “Evo ti čovjeka za koga ti rekoh: 'Taj će vladati nad mojim narodom.'”
18 Shawulu ya sami Sama’ila a hanyar shiga gari, sai ya tambaye shi ya ce, “Ina roƙonka ka nuna mini gidan mai duba?”
Šaul pristupi Samuelu na vratima i reče: “Daj mi kaži gdje je vidiočeva kuća.”
19 Sama’ila ya ce, “Ni ne mai duban, ka yi gaba zuwa ka tudu, gama yau za ka ci tare da ni, da safe kuma in sallame ka, in gaya muku duk abin da yake a zuciyarku.
A Samuel odgovori Šaulu: “Ja sam vidjelac. Pođi preda mnom na uzvišicu, danas ćete sa mnom jesti. Sutra ću te ujutro otpustiti i sve ću ti kazati što ti je na srcu.
20 Game da jakunan da suka ɓace kwana uku kuwa, kada ka damu, an same su. Ga wane ne Isra’ila ta sa dukan zuciya, in ba ga kai da kuma dukan iyalin mahaifinka ba?”
A za magarice koje su ti se izgubile prije tri dana ne uznemiruj se jer su se našle. Uostalom, kome pripada sve što je najdragocjenije u Izraelu? Zar ne tebi i svemu domu tvoga oca?”
21 Shawulu ya ce, “Ashe, ni ba mutumin Benyamin ba ne daga ƙaramar kabila ta Isra’ila? Dangina kuma ba shi ba ne mafi kakanni a cikin kabilar Benyamin ba? Yaya za ka faɗa mini irin wannan magana.”
A Šaul odgovori ovako: “Nisam li ja od Benjaminova plemena, najmanjega plemena Izraelova? A moj rod nije li najneznatniji između svih rodova Benjaminova plemena? Zašto mi, dakle, govoriš takve riječi?”
22 Sa’an nan Sama’ila ya shiga da Shawulu da baransa ya zaunar da su a gaban waɗanda aka gayyata, mutanen sun kai wajen mutum talatin.
Samuel uze Šaula i njegova momka, odvede ih u sobu i dade im mjesto u pročelju među uzvanicima, kojih je bilo tridesetak.
23 Sama’ila ya ce wa mai dahuwa, “Kawo naman da na ba ka, wannan da na ce ka ajiye dabam.”
Zatim Samuel reče kuharu: “Donesi dio koji ti dadoh i za koji ti rekoh da ga staviš na stranu.”
24 Sai mai dahuwan ya ɗauko cinya da abin da yake bisanta ya kawo ya ajiye a gaban Shawulu. Sama’ila ya ce, “Ga abin da aka ajiye dominka. Ka ci, gama an keɓe shi dominka saboda wannan hidima daga lokacin da na ce, ‘Na gayyaci baƙi.’” Shawulu kuwa ya ci tare da Sama’ila a ranan nan.
Kuhar uze but, donese ga i stavi pred Šaula, a Samuel mu reče: “Evo, pred tobom je ono što je sačuvano za tebe. Jedi, jer to ti je sačuvano baš za ovu zgodu.” Tako je u onaj dan Šaul jeo sa Samuelom.
25 Bayan suka gangaro daga tudu zuwa cikin gari, Sai Sama’ila ya yi magana da Shawulu a ɗakin samansa.
Potom odande siđoše u grad. Ondje prostriješe Šaulu na krovu.
26 Da asuba sai suka tashi, Sama’ila ya kira Shawulu daga ɗakin sama ya ce, “Ka shirya, zan sallame ka.” Da Shawulu ya shirya, sai Sama’ila da Shawulu suka fita waje tare.
I on leže na počinak. Čim je svanula zora, Samuel zovnu Šaula (na krovu) govoreći: “Ustani da te otpustim!” Kad je Šaul ustao, izađoše obojica, on i Samuel.
27 Suna dab da ƙarshen gari, sai Sama’ila ya ce wa Shawulu, “Ka ce wa bawanka yă yi gaba, kai ka ɗan dakata a nan tukuna, domin in ba ka saƙo daga Allah.”
Kad su došli na kraj grada, reče Samuel Šaulu: “Kaži momku neka pođe naprijed pred nama! A ti stani sada da ti objavim riječ Božju.”

< 1 Sama’ila 9 >