< 1 Sama’ila 6 >
1 Lokacin da akwatin alkawarin Ubangiji ya kai wata bakwai a ƙasar Filistiyawa.
After the Ark of the Lord had been in the country of the Philistines for seven months,
2 Filistiyawa suka kira firistoci da bokaye suka ce, “Me za mu yi da akwatin alkawarin Ubangiji? Ku gaya mana yadda za mu komar da shi inda ya fito.”
the Philistines summoned the priests and fortune-tellers, and asked, “What should we do with the Ark of the Lord? Explain to us how to send it back to where it came from.”
3 Suka ce, in za ku komar da akwatin alkawarin Allah na Isra’ila kada ku komar da shi hannu wofi; amma ku tabbata kun aika da hadaya don laifi zuwa wurinsa. Sa’an nan za ku warke ku kuma san dalilin da ya sa bai cire hannunsa a kanku ba.
“If you're going to send back the Ark of the God of Israel, do not send it back empty-handedly, but make sure to send along with it a gift of a guilt offering to him,” they replied. “Then you will be healed, and you will understand why he has treated you like this.”
4 Filistiyawa suka ce, “Wace irin hadaya don laifi za mu aika masa?” Suka ce, “Marurai biyar na zinariya da ɓeraye biyar na zinariya bisa ga yawan sarakunan Filistiyawa. Saboda annoba iri ɗaya ce ta buga ku da shugabanninku.
“What kind of guilt offering should we send back to him?” asked the Philistines. “Five gold objects in the shape of the swellings, and five gold rats representing the number of rulers of the Philistines,” they replied. “The same plague attacked both you and your rulers.
5 Ku yi siffofin marurai da na ɓeraye da suke hallaka gari, ku ba da girma ga Allah na Isra’ila. Wataƙila zai ɗauke hukuncinsa daga gare ku da allolinku da kuma ƙasarku.
Make models to represent your swellings and the rats destroying the country, and honor the God of Israel. Perhaps he will stop punishing you, your gods, and your land.
6 Me ya sa kun taurare kanku kamar yadda Masarawa da Fir’auna suka yi? Da ya ba su matsanancin wahala, ba su bar Isra’ilawa suka tafi hanyarsu ba?
Why be stubborn like the Egyptians and Pharaoh? When he punished them, didn't they send the Israelites on their way as they left?
7 “Yanzu fa ku shirya sabon keken shanu da shanu biyu masu ba wa’ya’yansu nono, waɗanda ba a taɓa sa musu karkiya ba. Ku daure keken shanu wa shanun, amma ku tsare’yan maruƙansu a gida.
So get a new cart ready, pulled by two milk cows that have never been yoked. Tie the cows to the cart, but take their calves away and put them in a stall.
8 Ku ɗauki wani akwati ku sa siffofin zinariyan nan a ciki, waɗanda za su zama kyautai na shafen laifi, ku ajiye kusa da Akwati na UBANGIJI. Bayan haka sai ku sa keken shanun da akwatin a hanya, ku bar shi yă tafi.
Pick up the Ark of the Lord, put it on the cart, and place the gold objects you are sending him as a guilt offering in a chest beside it. Then send the Ark away. Let it go whichever way it wants,
9 Amma ku zuba ido ku ga in ya haura zuwa yankinsa, zuwa Bet-Shemesh, to, Ubangiji ne ya kawo mana babban masifar a kanmu. Amma in bai bi ta nan ba, za mu san cewa ba shi ne ya buge mu ba, tsautsayi ne kawai.”
but keep watching it. If it goes up the road to its home country, to Beth-shemesh, then it is the Lord who caused all this terrible trouble for us. But if it doesn't, then we'll know that it wasn't him who punished us—it just happened to us by chance.”
10 Suka yi haka. Suka ɗauki shanun tatsa guda biyu suka ɗaura musu keken shanu, suka tsare’yan maruƙansu a gida.
So that's what the people did. They took two milk cows and tied them to the cart, and kept their calves in a stall.
11 Suka aza akwatin alkawarin Ubangiji a bisa keken shanun tare da akwatin siffofin ɓerayen zinariya da siffofin maruran.
They put the Ark of the Lord on the cart, together with the chest containing the gold rats and models of their swellings.
12 Sai shanun suka miƙe zuwa Bet-Shemesh. Suka bi hanya daidai, ba su juya dama ko hagu ba. Shugabannin Filistiyawa suka bi har zuwa iyakar ƙasar Bet-Shemesh.
The cows went straight up the road to Beth-shemesh, lowing as they went, going directly on the main road and not turning either left or right. The Philistine rulers followed them all the way to the border of Beth-shemesh.
13 A lokacin kuwa mutanen Bet-Shemesh suna girbin alkamansu a kwari da suka ɗaga ido suka hangi akwatin alkawarin Ubangiji, sai suka yi farin ciki ganinsa.
The people of Beth-shemesh were reaping wheat in the valley. When they looked up and saw the Ark, they were so happy to see it.
14 Keken shanun ya zo filin Yoshuwa a Bet-Shemesh ya tsaya a gefen wani babban dutse. Mutanen suka faskare keken shanun suka miƙa shanun hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji.
The cart came into the field of Joshua of Beth-shemesh, and stopped there beside a large rock. The people cut up the cart for wood and sacrificed the cows as a burnt offering to the Lord.
15 Lawiyawa suka saukar da akwatin alkawarin Ubangiji tare da babban akwati mai siffofin zinariya na ɓeraye da marurai suka ajiye su a kan ƙaton dutse. A wannan rana mutanen Bet-Shemesh suka miƙa hadaya ta ƙonawa da waɗansu hadayu ga Ubangiji.
The Levites took down the Ark of the Lord and the chest containing the gold objects, and put them on the large rock. The people of Beth-shemesh presented burnt offerings and made sacrifices to the Lord that day.
16 Shugabanni biyar na Filistiyawan nan suka ga duk abin da ya faru, suka koma zuwa Ekron a ranar.
The five Philistine rulers saw all that happened this and then went back to Ekron the same day.
17 Waɗannan su ne siffofi marurai na zinariya waɗanda Filistiyawa suka aika domin miƙa hadaya don laifi ga Ubangiji, ɗaya domin Ashdod, ɗaya domin Gaza, ɗaya domin Ashkelon, ɗaya domin Gat, ɗaya kuma domin Ekron.
The five gold models of swellings sent by the Philistines as a guilt offering to the Lord were from the rulers of Ashdod, Gaza, Ashkelon, Gath, and Ekron.
18 Filistiyawa kuma suka aika da siffofin ɓeraye biyar na zinariya. Yawan ɓerayen sun yi daidai da yawan garuruwan sarakunan nan biyar na Filistiyawa. Garuruwan sun ƙunshi waɗanda aka gina katangar birni kewaye da su, da kuma ƙauyukansu. Babban dutsen da suka ajiye akwatin alkawarin Ubangiji, ya zama shaida har wa yau a filin Yoshuwa a Bet-Shemesh.
The gold rats represented the number of Philistine towns of the five rulers—the fortified towns and their surrounding villages. The large rock on which they placed the Ark of the Lord still stands to this day in the field of Joshua of Beth-shemesh as a witness to what happened there.
19 Amma Allah ya kashe waɗansu mutum saba’in na mutanen Bet-Shemesh domin sun leƙa cikin akwatin alkawarin Ubangiji. Mutane kuwa suka yi makoki domin Ubangiji ya hallaka mutane da yawa.
But God killed some of the people of Beth-shemesh because they looked inside the Ark of the Lord. He killed seventy, and the people mourned deeply because the Lord had killed so many.
20 Mutanen Bet-Shemesh suka yi tambaya suka ce, wa zai iya tsaya a gaban Ubangiji Allah Mai Tsarki? Wurin wa akwatin alkawari zai je daga nan?
The people of Beth-shemesh asked, “Who can stand before the Lord, this holy God? Where should the Ark go from here?”
21 Sai suka aiki manzanni zuwa Kiriyat Yeyarim suka ce, “Filistiyawa sun komo da akwatin alkawarin Ubangiji, ku zo ku ɗauka ku kai wajenku.”
They sent messengers to the people of Kiriath-jearim to say, “The Philistines have returned the Ark of the Lord. Come down and take it home with you.”