< 1 Sama’ila 5 >

1 Bayan Filistiyawa sun ƙwace akwatin alkawarin Allah, sai suka ɗauke shi daga Ebenezer suka kai shi Ashdod.
Now the Philistines had taken the ark of God, and they brought it from Ebenezer to Ashdod.
2 Sa’an nan suka ɗauki akwatin alkawarin suka kai shi cikin haikalin gunkinsu Dagon, suka ajiye kusa da Dagon.
The Philistines took it, and brought it into the house of Dagon, and set it by Dagon.
3 Kashegari da safe da mutanen Ashdod suka farka sai ga Dagon ya fāɗi a gaban akwatin alkawarin Ubangiji. Sai suka ɗauki Dagon suka ajiye a wurin zamansa.
And the Ashdodites rose early on the next day, and look, Dagon had fallen on his face before the ark of Jehovah. So they raised up Dagon and set him in his place again.
4 Amma kashegari kuma da safe suka farka sai ga Dagon ya fāɗi a ƙasa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji! Kansa ya fashe, hannuwansa kuma sun kakkarye sun zube a madogarar ƙofa; jikinsa ne kaɗai ya rage.
And it happened when they arose early the next morning, look, Dagon had fallen on his face before the ark of Jehovah; and the head of Dagon and both the palms of his hands were cut off on the threshold. Only Dagon's torso was intact.
5 Saboda haka firistocin Dagon da waɗanda suke sujada a haikalin Dagon ba sa taka bakin ƙofar Dagon a Ashdod har wa yau.
Therefore neither the priests of Dagon, nor any who come into Dagon's house, step on the threshold of Dagon in Ashdod, to this day.
6 Hannun Ubangiji kuwa ya yi nauyi a bisa Ashdod da kewayenta. Ya kawo hallaka ga dukansu, ya kuma buga su da marurai.
But the hand of Jehovah was heavy on the Ashdodites, and he ravaged them and afflicted them with tumors, both Ashdod and its territory. And he brought up against them mice, and they burst out in their ships, and mice sprang up in the midst of their land, and there was a great terror of death in the city.
7 Da mutanen Ashdod suka ga abin da yake faruwa, sai suka ce, “Lalle Akwatin Alkawarin Allah na Isra’ila ba zai kasance da mu ba, domin hannunsa yana da nauyi a kanmu da bisan Dagon allahnmu.”
When the men of Ashdod saw what was happening, they said, "The ark of God shall not stay with us; for his hand is severe on us, and on Dagon our god."
8 Saboda haka suka kira duka shugabannin Filistiyawa suka tambaye su, suka ce, “Me za mu da akwatin alkawarin Allahn Isra’ila?” Sai suka amsa suka ce, “A ɗauki akwatin alkawarin Allah na Isra’ila a kai shi Gat.” Sai suka ɗauki akwatin alkawarin Allah na Isra’ila.
So they sent and gathered all the lords of the Philistines to them, and said, "What shall we do with the ark of God?" Then the Gittites answered, "Let the ark of God be carried over to us." So they brought the ark of God to Gath.
9 Amma bayan sun kai shi can, sai hannun Ubangiji ya yi gāba da birnin, aka jefa shi cikin wani mawuyacin hali. Ya buga mutanen birnin da marurai, babba da yaro.
And it came about that after they had brought it around, the hand of Jehovah was against the city with a very great confusion: and he struck the men of the city, both small and great; and tumors broke out on them.
10 Sai suka aika da akwatin alkawarin Allah zuwa Ekron. Yayinda akwatin alkawarin Allah yana shiga cikin Ekron, mutanen Ekron suka yi ihu, suka ce, “An kawo mana akwatin alkawarin Allah na Isra’ila domin yă kashe mu da mutanenmu.”
So they sent the ark of God to Ekron. It happened, as the ark of God came to Ekron, that the Ekronites cried out, saying, "Why have you brought about the ark of the God of Israel to us, to kill us and our people?"
11 Saboda haka suka kira ga dukan shugabannin Filistiyawa suka ce, “Ku komar da akwatin alkawarin Allah na Isra’ila inda ya fito; in ba haka ba zai kashe mu da mutanenmu.” Gama mutuwa ta cika garin da tsoro. Hannun Allah ya yi nauyi a kansa.
And they sent and gathered together all the lords of the Philistines, and they said, "Send away the ark of the God of Israel, and let it go again to its own place, so that it will not kill us and our people." For there was a panic throughout all the city when the ark of God arrived there.
12 Waɗanda ba su mutu ba kuwa, sun kamu da marurai. Kukan birnin kuwa ta hau har zuwa sama.
The men who did not die were struck with the tumors; and the cry of the city went up to heaven.

< 1 Sama’ila 5 >