< 1 Sama’ila 31 >

1 Filistiyawa suka yi yaƙi da Isra’ilawa, sai Isra’ilawa suka gudu a gaban Filistiyawa, aka kuma karkashe da yawa a dutsen Gilbowa.
Los filisteos atacaron a Israel, y los hombres de Israel huyeron en fuga ante los filisteos, cayendo muertos en el monte Gilboa.
2 Filistiyawa suka abka wa Shawulu da’ya’yansa maza, suka kashe’ya’yan Shawulu. Yonatan da Abinadab da Malki-Shuwa.
Y los filisteos tomaron a Saúl y sus hijos; y mataron a Jonatán, a Abinadab y a Malquisua, los hijos de Saúl.
3 Yaƙin ya yi zafi ƙwarai kewaye da Shawulu, har maharba suka ji masa ciwo sosai bayan sun sha ƙarfinsa.
Y la lucha iba mal para Saúl, y los arqueros se cruzaron con él y fue herido por los arqueros.
4 Sai Shawulu ya ce wa mai ɗauka masa makami, “Ka zare takobinka ka soke ni, kada waɗannan marasa kaciya su zo su ci mini mutunci, su kashe ni.” Amma mai ɗaukan makaman bai yarda ba don ya ji tsoro sosai. Sai Shawulu ya zāre takobinsa ya soki kansa.
Entonces Saúl dijo al siervo su escudero: Saca tu espada y pásala a través de mí, antes de que estos hombres sin circuncisión vengan y se burlen de mí. Pero su sirviente, lleno de miedo, no lo hizo. Entonces Saúl sacó su espada y cayendo sobre ella, se puso fin a sí mismo.
5 Da mai ɗaukar makamai ya ga Shawulu ya mutu, sai shi ma ya zāre takobinsa ya soki kansa ya mutu.
Y cuando su criado vio que Saúl estaba muerto, él hizo lo mismo, y se unió a él en la muerte.
6 Shawulu da yaransa uku da mai ɗaukar makamansa da dukan mutanensa suka mutu a rana ɗaya.
Entonces la muerte alcanzó a Saúl y sus tres hijos y su siervo el mismo día.
7 Sa’ad da Isra’ilawa na bakin kwari da waɗanda suke hayin Urdun suka ga sojojin Isra’ila suna gudu, Shawulu da yaransa uku kuma duk sun mutu, sai suka bar mallakansu suka sheƙa da gudu. Filistiyawa kuwa suka zo suka mamaye wuraren.
Y cuando los hombres de Israel cruzaron el valle y al otro lado del Jordán vieron que el ejército de Israel estaba huyendo y que Saúl y sus hijos estaban muertos, salieron de sus ciudades y huyeron; Y vinieron los filisteos y los tomaron para sí mismos.
8 Kashegari, da Filistiyawa suka zo domin su washe kayan matattun, sai suka tarar Shawulu da’ya’yansa uku duk sun mutu, a dutsen Gilbowa.
Al día siguiente, cuando los filisteos vinieron a sacar sus bienes de los muertos, vieron a Saúl y sus tres hijos muertos en la tierra en el monte Gilboa.
9 Suka sare kansa suka tuɓe makamansa, suka aika manzanni a dukan ƙasar Filistiyawa, su ba da labarin a haikalin allolinsu da cikin mutanensu.
Y cortándole la cabeza y quitándole el traje de guerra, enviaron un mensaje a la tierra de los filisteos por todas partes, para llevar las noticias a sus dioses y al pueblo.
10 Suka ajiye makaman Shawulu a cikin haikalin gumakan Ashtarot. Suka kafa gawarsa a kan katanga Bet-Shan.
Se pusieron sus ropas de guerra en la casa de Astarté. y su cuerpo fue fijado en la pared de Beth-san.
11 Sa’ad da mutanen Yabesh Gileyad suka sami labarin abin da Filistiyawa suka yi wa Shawulu.
Y cuando los habitantes de Jabes-galaad tuvieron noticias de lo que los filisteos habían hecho a Saúl,
12 Sai dukan jarumawansu suka tashi cikin dare suka tafi Bet-Shan suka saukar da gawar Shawulu da na’ya’yansa daga kan katangan Bet-Shan suka tafi Yabesh inda suka ƙone su.
Se levantaron todos los fuertes y valientes, viajando toda la noche, tomaron el cuerpo de Saúl y los cuerpos de sus hijos del muro de Bet-sán; y viniendo a Jabes y los quemaron allí.
13 Sai suka kwashi ƙasusuwansu suka binne a gindin itace tsamiya a Yabesh, suka kuma yi azumi kwana bakwai.
Y tomando los huesos lo enterraron debajo del árbol tamarisco en Jabes; Y por siete días guardaron ayuno.

< 1 Sama’ila 31 >