< 1 Sama’ila 22 >

1 Dawuda ya bar Gat, ya tsere zuwa kogon Adullam. Da’yan’uwansa da kuma iyalan mahaifinsa suka ji labari, sai suka tafi can wurinsa.
David partit de là et s'enfuit dans la caverne d'Odollam. Ses frères et toute la maison de son père l'ayant appris, ils descendirent là, vers lui.
2 Dukan mutanen da suke cikin wahala, da waɗanda ake binsu bashi, da masu damuwoyi, suka tattaru a wurin Dawuda. Shi kuwa ya zama shugabansu. Yawansu ya kai ɗari huɗu.
Tous les opprimés, tous ceux qui avaient des créanciers et tous ceux qui étaient dans l'amertume, se rassemblèrent auprès de lui, et il devint leur chef; il y eut ainsi avec lui environ quatre cents hommes.
3 Daga can Dawuda ya tafi Mizfa a Mowab. Ya ce wa sarkin Mowab, “Za ka yarda mahaifina da mahaifiyata su zo su zauna a wurinka kafin in san abin da Allah zai yi da ni?”
De là, David s'en alla à Maspha de Moab. Il dit au roi de Moab: « Que mon père et ma mère puissent, je te prie, se retirer chez vous, jusqu'à ce que je sache ce que Dieu fera de moi. »
4 Saboda haka ya bar su a wurin sarkin Mowab, suka zauna da shi duk tsawon lokacin da Dawuda yake ta ɓuya a kogwannin duwatsu.
Et il les amena devant le roi de Moab, et ils demeurèrent chez lui tout le temps que David fut dans le lieu fort.
5 Amma annabin nan Gad ya ce wa Dawuda, “Kada ka zauna a nan, maza ka tashi ka shiga ƙasar Yahuda”. Sai Dawuda ya tashi ya tafi jejin Heret.
Le prophète Gad dit à David: « Ne reste pas dans le lieu fort; va-t'en et reviens dans le pays de Juda. » Et David s'en alla et se rendit à la forêt de Haret.
6 Sai Shawulu ya sami labari cewa an ga Dawuda da mutanensa. Shawulu kuwa yana zaune da māshinsa kusa a ƙarƙashin itacen tsamiya a tudun Gibeya, tare da dukan ma’aikatansa kewaye da shi.
Saül apprit que David et les gens qui étaient avec lui avaient été reconnus. Or Saül était assis, à Gabaa, sous le tamarisque, sur la hauteur, sa lance à la main, et tous ses serviteurs étaient rangés devant lui.
7 Ya ce musu, “Mutanen Benyamin, ku saurara; ɗan Yesse zai iya ba dukanku filaye da gonakin inabi ne? Zai ba dukanku shugabanci na dubbai ko shugabanci na ɗari-ɗari?
Saül dit à ses serviteurs qui étaient rangés devant lui: « Ecoutez, Benjamites: le fils d'Isaï vous donnera-t-il aussi à tous des champs et des vignes, fera-t-il de vous tous des chefs de milliers et des chefs de centaines,
8 Abin da ya sa dukanku kuka gama baki a kaina? Ba wanda ya gaya mini lokacin da ɗana ya yi yarjejjeniya da ɗan Yesse, ba wanda ya kulla da ni, ko ya gaya mini cewa ɗana ya sa bawana yă tayar mini, yana fakona kamar yadda yake a yau.”
que vous vous soyez tous ligués contre moi, qu'il n'y ait personne qui m'ait informé que mon fils a fait alliance avec le fils d'Isaï, et que nul de vous n'en souffre pour moi et ne m'avertisse que mon fils a soulevé mon serviteur contre moi, pour me dresser des embûches, comme il le fait aujourd'hui? »
9 Amma Doyeg mutumin Edom da yake tsaye tare da fadawan Shawulu ya ce, “Na ga ɗan Yesse ya zo wurin Ahimelek ɗan Ahitub a Nob.
Doëg, l'Edomite, qui était le chef des serviteurs de Saül, répondit et dit: « J'ai vu le fils d'Isaï venir à Nobé, auprès d'Achimélech, fils d'Achitob.
10 Ahimelek ya roƙi Ubangiji saboda shi, ya kuma ba shi guzuri da takobin Goliyat Bafilistin.”
Achimélech a consulté pour lui Yahweh, et il lui a donné des vivres; il lui a aussi donné l'épée de Goliath, le Philistin. »
11 Sai sarki ya aika aka kira masa Ahimelek firist ɗan Ahitub da dukan iyalin mahaifinsa. Dukansu suka zo wurin sarki.
Le roi envoya appeler le prêtre Achimélech, fils d'Achitob, et toute la maison de son père, les prêtres qui étaient à Nobé.
12 Shawulu ya ce, “Ka saurara yanzu, ɗan Ahitub.” Ya amsa ya ce, “Ina saurara, ranka yă daɗe.”
Ils vinrent tous vers le roi; et Saül dit: « Ecoute, fils d'Achitob! » Il répondit: « Me voici, mon seigneur. »
13 Shawulu ya ce masa, “Don me ka gama baki da ɗan Yesse a kaina har ka ba shi burodi da takobin (Goliyat), ka kuma roƙi Allah don yă tayar mini, yă kuma yi fakona kamar yadda yake yi yau?”
Saül lui dit: « Pourquoi vous êtes-vous ligués contre moi, toi et le fils d'Isaï? Tu lui as donné du pain et une épée, et tu as consulté Dieu pour lui, pour qu'il s'élève contre moi et me dresse des embûches, comme il le fait aujourd'hui? »
14 Ahimelek ya ce wa sarki, “A cikin bayinka duka, wa ke da aminci iri na Dawuda, surukin sarki, shugaban jarumanka wanda ake girmamawa da gaske a gidanka?
Achimélech répondit au roi et dit: « Lequel d'entre tous tes serviteurs est, comme David, d'une fidélité éprouvée, gendre du roi, admis à tes conseils et honoré dans ta maison?
15 A wannan rana ce da na fara roƙon Allah saboda shi? Kada sarki yă zargi bawansa ko wani daga iyalin mahaifinsa, gama bawanka bai san kome a kan dukan waɗannan al’amura ba.”
Est-ce aujourd'hui que j'aurais commencé à consulter Dieu pour lui? Loin de moi! Que le roi ne mette pas à la charge de son serviteur une chose qui pèserait sur toute la maison de mon père, car ton serviteur n'a rien su de tout cela, ni peu ni beaucoup. »
16 Amma sarki ya ce, “Lalle Ahimelek za ka mutu, da kai da dukan iyalin mahaifinka.”
Le roi dit: « Tu mourras, Achimélech, toi et toute la maison de ton père. »
17 Sai sarki ya umarci matsaran da suke tsaye kusa da shi ya ce, “Ku kakkashe firistocin Ubangiji, gama su ma sun goyi bayan Dawuda. Sun san yana gudu, duk da haka ba su gaya mini ba.” Amma ma’aikatan sarki ba su yarda su sa hannu su kashe firistocin Ubangiji ba.
Et le roi dit aux gardes qui se tenaient près de lui: « Tournez-vous et mettez à mort les prêtres de Yahweh; car leur main est avec David et, sachant bien qu'il était en fuite, ils ne m'en ont pas informé. » Mais les serviteurs du roi ne voulurent pas étendre la main pour frapper les prêtres de Yahweh.
18 Sai sarki ya umarce Doyeg ya ce, “Ka juya ka kakkashe firistocin.” Doyeg mutumin Edom ya juya ya kakkashe firistocin. A ranar kuwa ya kashe mutum tamanin da biyar waɗanda suke sanye da efod na lilin.
Alors le roi dit à Doëg: « Tourne-toi et frappe les prêtres. » Et Doëg l'Edomite se tourna, et ce fut lui qui frappa les prêtres; il mit à mort en ce jour quatre-vingt-cinq hommes portant l'éphod de lin.
19 Ya kuma hallaka Nob birnin firistoci, ya kashe dukan mata, da maza, da yara, da jarirai, da shanu, da jakuna, da kuma tumaki.
Saül frappa encore du tranchant de l'épée Nobé, ville sacerdotale: hommes et femmes, enfants et nourrissons, bœufs, ânes et brebis, furent passés au fil de l'épée.
20 Amma Abiyatar ɗan Ahimelek jikan Ahitub ya tsere, ya gudu zuwa wurin Dawuda.
Un seul fils d'Achimélech, fils d'Achitob, s'échappa; son nom était Abiathar, et il se réfugia auprès de David.
21 Abiyatar gaya wa Dawuda cewa, “Shawulu ya hallaka firistocin Ubangiji.”
Abiathar annonça à David que Saül avait tué les prêtres de Yahweh.
22 Dawuda ya ce wa Abiyatar, “Lalle a wancan ranar, sa’ad da na ga Doyeg mutumin Edom a can, na san tabbatacce zai gaya wa sarki. Ni ne sanadin mutuwar dukan iyalin mahaifinka.
Et David dit à Abiathar: « Je savais bien, en ce jour-là, que Doëg l'Edomite, qui était là, ne manquerai pas d'informer Saül. C'est moi qui suis cause de la mort de toute la maison de ton père.
23 Ka zauna tare da ni, kada ka ji tsoro mutumin da yake neman ranka, yana nema raina ma. Ka zauna lafiya tare da ni.”
Reste avec moi, ne crains rien; car celui qui en veut à ma vie en veut à ta vie, et près de moi tu auras bonne garde. »

< 1 Sama’ila 22 >