< 1 Sama’ila 17 >
1 To, fa, Filistiyawa suka tattara mayaƙansu suka haɗu a Soko cikin Yahuda domin yaƙi. Suka yi sansani a Efes-Dammim, tsakanin Soko da Azeka.
Nowe the Philistims gathered their armies to battell, and came together to Shochoh, which is in Iudah, and pitched betweene Shochoh and Azekah, in the coast of Dammim.
2 Shawulu da Isra’ilawa suka taru suka yi sansani a Kwarin Ela suka ja dāgā don su yi yaƙi da Filistiyawa.
And Saul, and the men of Israel assembled, and pitched in the valley of Elah, and put themselues in battell araie to meete the Philistims.
3 Filistiyawa suka zauna a tudu guda, Isra’ilawa kuma suka zauna a ɗaya tudun. Kwari yana a tsakaninsu.
And the Philistims stoode on a mountaine on the one side, and Israel stoode on a mountaine on the other side: so a valley was betweene them.
4 Wani jarumin da ake kira Goliyat wanda ya fito daga Gat, ya fita daga sansanin Filistiyawa. Tsawonsa ya fi ƙafa tara.
Then came a man betweene them both out of the tents of the Philistims, named Goliath of Gath: his height was sixe cubites and an hande breadth,
5 Ya sa hular kwanon da aka yi da tagulla, da rigar ƙarfe mai sulke, nauyin rigar ya kai shekel dubu biyar.
Aud had an helmet of brasse vpon his head, and a brigandine vpon him: and the weight of his brigandine was fiue thousand shekels of brasse.
6 A ƙafafunsa kuwa ya sa ƙarafar tagulla, rataye a bayansa kuma māshi ne na tagulla.
And he had bootes of brasse vpon his legs, and a shield of brasse vpon his shoulders.
7 Ƙotar kibiyarsa kuwa kamar sandar saƙar igiya take, ƙarfen kibiyar kuma nauyinsa ya kai shekel ɗari shida. Mai riƙe masa garkuwa yana tafe a gabansa.
And the shaft of his speare was like a weauers beame: and his speare head weyed sixe hundreth shekels of yron: and one bearing a shielde went before him.
8 Goliyat ya tsaya ya tā da murya wa hafsoshin Isra’ila ya ce, “Me ya sa kuka fito kuna layi don yaƙi? Ni ba Bafilistin ba ne? Ku kuma ba bayin Shawulu ba ne? Ku zaɓi waninku yă zo nan.
And he stoode, and cried against the hoste of Israel, and saide vnto them, Why are yee come to set your battell in aray? am not I a Philistim, and you seruaunts to Saul? chuse you a man for you, and let him come downe to me.
9 In zai iya yin faɗa har yă kashe ni, to, za mu zama bayinku. Amma in na fi ƙarfinsa na kashe shi, to, sai ku zama bayinmu, ku kuma yi mana bauta.”
If he be able to fight with me, and kill me, then wil we be your seruants: but if I ouercome him, and kill him, then shall yee be our seruants, and serue vs.
10 Sai Bafilistin ya ce, “A wannan rana, na kalubalanci sojojin Isra’ila, ku ba ni mutum ɗaya mu yi faɗa.”
Also the Philistim saide, I defie the hoste of Israel this day: giue mee a man, that we may fight together.
11 Da jin maganganun Bafilistin, sai Shawulu da dukan Isra’ila suka damu suka kuma ji tsoro.
When Saul and all Israel heard those wordes of the Philistim, they were discouraged, and greatly afraide.
12 To, Dawuda dai ɗan wani mutumin Efratawa ne mai suna Yesse, shi mutumin Betlehem ne a cikin Yahudiya. Yesse yana da yara maza takwas, a zamanin Shawulu kuwa, Yesse ya riga ya tsufa.
Nowe this Dauid was the sonne of an Ephrathite of Beth-lehem Iudah, named Ishai, which had eight sonnes: and this man was taken for an olde man in the daies of Saul.
13 Manyan’ya’yansa maza uku, sun bi Shawulu wajen yaƙi. Ɗansa na fari shi ne Eliyab, na biyu shi ne Abinadab, na uku kuwa shi ne Shamma.
And the three eldest sonnes of Ishai went and followed Saul to the battel: and the names of his three sonnes that went to battell, were Eliab the Eldest, and the next Abinadab, and the thirde Shammah.
14 Dawuda shi ne ɗan autansu. Manyan’yan mazan nan uku suka bi Shawulu.
So Dauid was the least: and the three eldest went after Saul.
15 Amma Dawuda yakan tafi sansanin Shawulu lokaci-lokaci yă kuma koma Betlehem don yă yi kiwon tumakin mahaifinsa.
Dauid also went, but hee returned from Saul to feede his fathers sheepe in Beth-lehem.
16 Kwana arba’in cif, Bafilistin nan ya yi ta fitowa kowane safe da kuma kowace yamma.
And the Philistim drew neere in the morning, and euening, and continued fourtie daies.
17 Yesse ya ce wa ɗansa Dawuda, “Ka ɗauki wannan gasasshen hatsi da waɗannan curin burodi goma, ka kai wa’yan’uwanka a sansani da sauri.
And Ishai said vnto Dauid his sone, Take nowe for thy brethren an Ephah of this parched corne, and these ten cakes, and runne to the hoste to thy brethren.
18 Ka haɗa da waɗannan cuku guda goma, ka kai wa komandan rundunarsu. Ka ga lafiyar’yan’uwanka, ka kawo mini labari daga wurinsu.
Also carie these ten fresh cheeses vnto the captaine, and looke howe thy brethren fare, and receiue their pledge.
19 Suna tare da Shawulu da kuma dukan mutanen Isra’ila a Kwarin Ela, suna can suna yaƙi da Filistiyawa.”
(Then Saul and they, and all the men of Israel were in the valley of Elah, fighting with the Philistims)
20 Kashegari da sassafe, Dawuda ya tashi ya bar tumakinsa wa wani yă lura da su, sai ya ɗauki kayansa, ya kama hanya kamar yadda Yesse ya umarce shi. Ya isa sansanin daidai sa’ad da rundunar tana fitowa zuwa bakin dāgā, suna kirarin yaƙi.
So Dauid rose vp earely in the morning, and left the sheepe with a keeper, and tooke and went as Ishai had commanded him, and came within the compasse of the hoste: and the hoste went out in araie, and shouted in the battell.
21 Isra’ila da Filistiyawa suka ja dāgā suna fuskantar junansu.
For Israel and the Philistims had put themselues in araie, armie against armie.
22 Dawuda ya bar kayansa a wajen wani mai lura da kaya, sai ya ruga zuwa bakin dāgā yă gai da’yan’uwansa.
And Dauid left the things, which hee bare, vnder the handes of the keeper of the cariage, and ranne into the hoste, and came, and asked his brethren howe they did.
23 Da yana magana da su sai Goliyat, jarumin nan Bafilistin daga Gat ya fito daga rundunar Filistiyawa, ya tā da murya kamar yadda ya saba. Dawuda kuwa ya ji shi.
And as hee talked with them, beholde, the man that was betweene the two armies, came vp, (whose name was Goliath ye Philistim of Gath) out of the armie of the Philistims, and spake such woordes, and Dauid heard them.
24 Da Isra’ilawa suka ga mutumin, sai dukansu suka gudu saboda tsananin tsoro.
And all the men of Israel, when they sawe the man, ranne away from him, and were sore afraied.
25 Isra’ilawa suka yi ta cewa, “Kun ga yadda wannan mutum yana ta fitowa? Yana fitowa ne don yă kalubalanci Isra’ila. Sarki zai sāka wa mutumin da ya kashe wannan da dukiya mai yawa. Zai kuma ba shi’yarsa yă aura, yă cire suna mahaifinsa daga biyan kuɗin haraji cikin Isra’ila.”
For euery man of Israel saide, Sawe yee not this man that commeth vp? euen to reuile Israel is he come vp: and to him that killeth him, wil the king giue great riches, and will giue him his daughter, yea, and make his fathers house free in Israel.
26 Dawuda ya tambayi mutanen da suke tsaye kusa da shi ya ce, “Me za a yi wa wanda ya kashe Bafilistin nan, ya kuma cire wannan kunya daga Isra’ila? Wane ne wannan bafilistin marar kaciya da yake kalubalantar rundunar yaƙi na Allah mai rai?”
Then Dauid spake to the men that stoode with him, and sayde, What shall be done to the man that killeth this Philistim, and taketh away the shame from Israel? for who is this vncircumcised Philistim, that he shoulde reuile the hoste of the liuing God?
27 Sai suka sāke gaya masa abin da suka faɗa cewa, “Ga abin da zai faru da wanda ya kashe shi.”
And the people answered him after this maner, saying, Thus shall it be done to the man that killeth him.
28 Da wansa Eliyab, ya ji yana magana da mutanen, sai ransa ya ɓace ƙwarai saboda fushi, sai ya ce wa Dawuda, “Me ka zo yi a nan? Wa kuma ka bar wa’yan tumakin a jeji? Na san ka da taurinkai, da kuma mugun hali. Ka zo nan ne don ka yi kallon yaƙi kawai.”
And Eliab his eldest brother heard when he spake vnto the men, and Eliab was verie angrie with Dauid, and sayde, Why camest thou downe hither? and with whome hast thou left those fewe sheepe in the wildernesse? I knowe thy pride and the malice of thine heart, that thou art come downe to see the battell.
29 Dawuda ya ce, “To, yanzu me na yi? Ba zan ma yi magana ba?”
Then Dauid sayde, What haue I nowe done? Is there not a cause?
30 Sai ya juya wajen wani kuma ya sāke kawo zancen, mutanen kuwa suka amsa masa kamar dā.
And hee departed from him into the presence of another, and spake of the same maner, and the people answered him according to the former woordes.
31 Aka ji abin da Dawuda ya ce, aka kuwa gaya wa Shawulu, Shawulu kuma ya aika a kawo shi.
And they that heard the wordes which Dauid spake, rehearsed them before Saul, which caused him to be brought.
32 Da Shawulu ya tambayi Dawuda, sai Dawuda ya ce masa, “Kada kowa yă damu saboda wannan Bafilistin. Bawanka zai je yă yi faɗa da shi.”
So Dauid saide to Saul, Let no mans heart faile him, because of him: thy seruant wil goe, and fight with this Philistim.
33 Shawulu ya ce, “Ba za ka iya yin faɗa da wannan Bafilistin ba, ya daɗe yana yaƙi, ya yi yaƙi tun yana saurayi. Ga shi kuwa kai ɗan yaro ne kawai.”
And Saul sayde to Dauid, Thou art not able to goe against this Philistim to fight with him: for thou art a boye, and he is a man of warre from his youth.
34 Amma Dawuda ya ce wa Shawulu, “Bawanka yana kiwon tumakin mahaifinsa. Sa’ad da zaki ko beyar ta zo ta kama tunkiya, ta tafi da ita.
And Dauid answered vnto Saul, Thy seruant kept his fathers sheepe, and there came a lyon, and likewise a beare, and tooke a sheepe out of the flocke,
35 Nakan bi ta a baya in buga ta in kuma ƙwato tunkiyar daga bakinta. In kuma ta taso mini, nakan cafke ta a gashinta in buga ta in kashe.
And I went out after him and smote him, and tooke it out of his mouth: and when he arose against me, I caught him by the beard, and smote him, and slue him.
36 Bawanka ya kashe zaki da beyar, wannan Bafilistin marar kaciya zai zama kamar ɗaya daga cikinsu, domin ya rena rundunar Allah mai rai.
So thy seruaunt slue both the lyon, and the beare: therefore this vncircumcised Philistim shall be as one of them, seeing hee hath railed on the hoste of the liuing God.
37 Ubangiji wanda ya cece ni daga kumbar zaki da kuma kumbar beyar, zai cece ni daga hannun wannan Bafilistin.” Shawulu ya ce wa Dawuda, “Je ka, Ubangiji yă kasance tare da kai.”
Moreouer Dauid sayd, The Lord that deliuered me out of the pawe of the lyon, and out of the paw of the beare, he wil deliuer me out of the hand of this Philistim. Then Saul sayd vnto Dauid, Go, and the Lord be with thee.
38 Sai Shawulu ya kawo kayan yaƙinsa ya sa wa Dawuda. Ya sa masa hular kwanon da aka yi da tagulla a kansa, ya kuma sa masa rigar ƙarfensa.
And Saul put his rayment vpon Dauid, and put an helmet of brasse vpon his head, and put a brigandine vpon him.
39 Dawuda ya ɗaura māshin Shawulu a sulken, ya yi ƙoƙari yă zaga, sai ya ji ba zai iya ba saboda bai saba ba. Ya cewa Shawulu, “Ba zan iya tafiya da waɗannan ba, domin ban saba ba.” Don haka ya tuɓe su.
Then girded Dauid his sword vpon his rayment, and began to go: for he neuer proued it: and Dauid sayde vnto Saul, I can not goe with these: for I am not accustomed. wherefore Dauid put them off him.
40 Sai ya ɗauki sandansa, ya zaɓi duwatsu guda biyar masu sulɓi daga cikin rafi, ya sa su a’yar jakarsa ta makiyaya; ya kuma ɗauki majajjawarsa, ya tafi, yă fuskanci Bafilistin.
Then tooke he his staffe in his hand, and chose him fiue smoothe stones out of a brooke, and put them in his shepheards bagge or skrippe, and his sling was in his hand, and he drewe neere to the Philistim.
41 Ana ciki haka, sai Bafilistin nan shi ma ya fita yana gusowa zuwa wurin Dawuda. Mai riƙe masa garkuwar yaƙi kuwa yana tafe a gabansa.
And the Philistim came and drew neere vnto Dauid, and the man that bare the shielde went before him.
42 Bafilistin ya dubi Dawuda daga sama har ƙasa, ya gan dai ɗan yaro ne kawai, kyakkyawa kuma mai ƙoshin lafiya, sai ya rena shi.
Now when the Philistim looked about and saw Dauid, he disdeined him: for he was but yong, ruddie, and of a comely face.
43 Ya ce masa, “Kana tsammani ni kare ne da za ka zo mini da sanda?” Sai ya la’anci Dawuda da sunayen allolin Filistiyawa.
And the Philistim sayde vnto Dauid, Am I a dog, that thou commest to me with staues? And the Philistim cursed Dauid by his gods.
44 Ya ce, “Zo nan, ni kuwa zan ba da naman jikinka ga tsuntsayen sama da namun jeji su ci.”
And the Philistim sayd to Dauid, Come to me, and I will giue thy flesh vnto the foules of the heauen, and to the beastes of the field.
45 Dawuda ya ce wa Bafilistin, “Kana zuwa ka yaƙe ni da māshi da takobi da kere, amma ni ina zuwa in yaƙe ka a cikin sunan Ubangiji Maɗaukaki, Allah na rundunar Isra’ila, wanda ka rena.
Then sayd Dauid to the Philistim, Thou commest to me with a sword, and with a speare, and with a shield, but I come to thee in the Name of the Lord of hostes, the God of the hoste of Israel, whom thou hast rayled vpon.
46 Yau nan, Ubangiji zai bashe ka a hannuna, zan kuwa kashe ka, in datse kanka. Yau, zan ba da gawawwakin rundunar Filistiyawa ga tsuntsayen sama da namun jeji, da haka duniya za tă sani lalle akwai Allah a cikin Isra’ila.
This day shall the Lord close thee in mine hand, and I shall smite thee, and take thine head from thee, and I wil giue the carkeises of the hoste of the Philistims this daye vnto the foules of the heauen, and to the beasts of the earth, that all the world may know that Israel hath a God,
47 Duk waɗanda suka taru a nan za su san cewa ba da māshi ko takobi ne Ubangiji yake ceto ba, gama yaƙin nan na Ubangiji ne, shi kuwa zai bashe ku duka a hannuwanmu.”
And that all this assembly may know, that the Lord saueth not with sworde nor with speare (for the battel is the Lords) and he will giue you into our handes.
48 Yayinda Bafilistin yana matsowa kusa domin yă fāɗa wa Dawuda, sai Dawuda ya ruga a guje zuwa bakin dāgā don yă same shi.
And when the Philistim arose to come and drawe neere vnto Dauid, Dauid hasted and ran to fight against the Philistim.
49 Ya sa hannu a jakarsa ya ɗauki dutse, ya sa cikin majajjawa ya wurga, dutsen kuwa ya bugi Bafilistin a goshi, dutsen ya shiga cikin goshinsa, sai Bafilistin ya fāɗi rubda ciki.
And Dauid put his hande in his bagge, and tooke out a stone, and slang it, and smote the Philistim in his forehead, that the stone sticked in his forehead, and he fell groueling to the earth.
50 Da majajjawa da dutse kawai Dawuda ya ci nasara a kan Bafilistin. Ya buge shi, ya kashe shi ba tare da takobi a hannunsa ba.
So Dauid ouercame the Philistim with a sling and with a stone, and smote the Philistim, and slew him, when Dauid had no sword in his hand.
51 Dawuda ya ruga ya tsaya a bisan Bafilistin, ya zare takobin Bafilistin daga kubensa, ya datse masa kai da shi. Da Filistiyawa suka ga jaruminsu ya mutu, sai suka juya suka gudu.
Then Dauid ranne, and stood vpon the Philistim, and tooke his sword and drew it out of his sheath, and slewe him, and cut off his head therewith. So whe the Philistims saw, that their champion was dead, they fled.
52 Mutanen Isra’ila da na Yahuda suka rugo gaba da babbar murya, suka fafari Filistiyawa har zuwa mashigin Gat da kuma ƙofofin Ekron. Gawawwakin Filistiyawa suka bazu a hanyar Sha’arayim zuwa Gat da kuma Ekron.
And the men of Israel and Iudah arose, and shouted, and followed after the Philistims, vntill they came to the valley, and vnto the gates of Ekron: and the Philistims fell downe wounded by the way of Shaaraim, euen to Gath and to Ekron.
53 Da Isra’ilawa suka komo daga bin Filistiyawa sai suka washe sansanin Filistiyawa.
And the children of Israel returned from pursuing the Philistims, and spoyled their tents.
54 Dawuda ya ɗauki kan Bafilistin zuwa Urushalima. Sai Dawuda ya ajiye kayan yaƙin Bafilistin a tentinsa.
And Dauid tooke the head of ye Philistim, and brought it to Ierusalem, and put his armour in his tent.
55 Yayinda Shawulu yake kallon Dawuda sa’ad da za shi yă yaƙi Bafilistin, sai ya tambayi Abner, komandan rundunarsa ya ce, “Abner, ɗan wane ne wannan saurayi?” Abner ya ce ran sarki yă daɗe, “Ban sani ba.”
When Saul sawe Dauid go forth against the Philistim, he sayd vnto Abner the captaine of his hoste, Abner, whose sonne is this yong man? and Abner answered, As thy soule liueth, O King, I can not tell.
56 Sarki ya ce, “Ka tambaya mini ko yaron wane ne wannan saurayi.”
Then the King sayde, Enquire thou whose sonne this yong man is.
57 Dawuda yana dawowa daga karkashe Filistiyawa ke nan, sai Abner ya kai shi gaban Shawulu, riƙe da kan Bafilistin.
And when Dauid was returned from the slaughter of the Philistim, then Abner tooke him, and brought him before Saul with the head of the Philistim in his hand.
58 Sai Shawulu ya ce, “Kai ɗan wane ne, saurayi?” Dawuda ya ce, “Ni ɗan bawanka Yesse ne, na Betlehem.”
And Saul sayde to him, Whose sonne art thou, thou yong man? And Dauid answered, I am the sonne of thy seruant Ishai the Bethlehemite.