< 1 Bitrus 2 >

1 Saboda haka, ku rabu da kowace ƙeta da dukan ruɗu, munafunci, kishi, da kuma kowace irin ɓata suna.
Protož složíce všelikou zlost, a všelikou lest, a pokrytství, a závist, i všecka utrhání,
2 Kamar sababbin jarirai, ku yi marmarin madara zalla ta ruhaniya, domin ta wurinta za ku yi girma cikin cetonku,
Jakožto nyní zrozená nemluvňátka, mléka beze lsti, Božího slova žádostivi buďte, abyste jím rostli,
3 yanzu da kuka ɗanɗana alherin Ubangiji.
Jestliže však okusili jste, kterak dobrotivý jest Pán.
4 Da kuka zo gare shi, rayayyen Dutse, da mutane suka ƙi amma Allah ya zaɓa, kuma mai daraja a gare shi
K kterémuž přistupujíce k kameni živému, od lidí zajisté zavrženému, ale od Boha vyvolenému a drahému,
5 ku ma, a matsayinku na duwatsu masu rai, ana gina ku ga zama gidan ruhaniya don ku zama tsattsarkar ƙungiyar firistoci, kuna miƙa hadayun ruhaniya, abin karɓa ga Allah ta wurin Yesu Kiristi.
I vy, jako kamení živé, vzdělávejte se v dům duchovní, kněžstvo svaté, k obětování duchovních obětí, vzácných Bohu skrze Jezukrista.
6 Gama a cikin Nassi an ce, “Ga shi, na kafa dutse a Sihiyona, zaɓaɓɓen dutse na kusurwar gini mai daraja, wanda kuma ya dogara gare shi ba zai taɓa kunyata ba.”
A protož praví písmo: Aj, zakládámť na Sionu kámen úhelný, vybraný, drahý, v kterýž kdokoli věří, nikoli nebude zahanben.
7 A gare ku da kuka gaskata, wannan dutse mai daraja ne. Amma ga waɗanda ba su gaskata ba, “Dutsen da magina suka ƙi ya zama dutsen kusurwar gini,
Vám tedy věřícím jest poctivost, ale nepovolným kámen, kterýž zavrhli stavitelé, tenť jest učiněn v hlavu úhelní, a kámen úrazu, a skála pohoršení,
8 kuma, “Dutse ne da yake sa mutane tuntuɓe kuma fā ne da yake sa su fāɗi.” Sun yi tuntuɓe domin sun ƙi su yi biyayya da saƙon, wanda kuma yake abin da aka ƙaddara musu.
Těm, kteříž se urážejí na slovu, nepovolní jsouce, k čemuž i odloženi jsou.
9 Amma ku zaɓaɓɓu ne, ƙungiyar firistocin babban Sarki, al’umma mai tsarki, jama’a mallakar Allah, domin ku shaida yabon shi wanda ya kira ku daga cikin duhu zuwa haskensa mai banmamaki.
Ale vy jste rod vyvolený, královské kněžstvo, národ svatý, lid dobytý, abyste zvěstovali ctnosti toho, kterýž vás povolal ze tmy v předivné světlo své.
10 Dā ku ba mutane ba ne, amma yanzu ku mutanen Allah ne; Dā ba ku karɓi jinƙai ba, amma yanzu kun karɓi jinƙai.
Kteříž jste někdy ani lidem nebyli, nyní pak jste lid Boží; kteříž jste někdy byli nedošli milosrdenství, nyní pak jste došli milosrdenství.
11 Abokaina ƙaunatattu, ina roƙonku, a matsayin bare da kuma baƙi a duniya, ku rabu da sha’awace-sha’awacen zunubin da suke yaƙi da ranku.
Nejmilejší, prosímť vás, abyste jakožto příchozí a pohostinní zdržovali se od tělesných žádostí, kteréž rytěřují proti duši,
12 Ku yi irin rayuwa mai kyau a cikin masu bautar gumaka, yadda ko da sun zarge ku da yin laifi, za su iya ganin ayyukanku nagari, su ɗaukaka Allah a ranar da zai ziyarce mu.
Obcování své mezi pohany majíce dobré, aby místo toho, kdež utrhají vám jako zločincům, dobré skutky vaše spatřujíce, velebili Boha v den navštívení.
13 Saboda Ubangiji, ku yi biyayya ga kowace hukumar da aka kafa cikin mutane, ko ga sarki, a matsayi wanda ya fi iko,
Poddáni tedy buďte všelikému lidskému zřízení pro Pána, buďto králi, jako nejvyššímu,
14 ko ga gwamnoni, waɗanda ya aika domin su hukunta masu laifi su kuma yabi masu aikata abin da yake daidai.
Buďto vládařům, jako od něho poslaným, ku pomstě zle činících, a k chvále dobře činících.
15 Gama nufin Allah ne cewa ta wurin yin nagarta za ku toshe jahilcin marasa azanci.
Nebo tak jest vůle Boží, abyste dobře činíce, zacpali ústa nemoudrých a neumělých lidí.
16 Ku yi rayuwa kamar mutanen da aka’yantar, sai dai kada ku yi amfani da’yancinku a matsayin hujjar aikata mugunta; ku yi rayuwa kamar bayin Allah.
Buďtež jako svobodní, však ne jako zástěru majíce své zlosti svobodu, ale jakožto služebníci Boží.
17 Ku nuna ladabin da ya dace ga kowa. Ku ƙaunaci’yan’uwantakar masu bi, ku ji tsoron Allah, ku girmama sarki.
Všecky ctěte, bratrstvo milujte, Boha se bojte, krále v poctivosti mějte.
18 Bayi, ku yi biyayya ga iyayengijinku da matuƙar ladabi, ba kawai ga waɗanda suke da kirki da masu sauƙinkai ba, amma har ga masu zafin rai ma.
Služebníci poddáni buďte ve vší bázni pánům, netoliko dobrým a mírným, ale i zlým.
19 Gama abin yabo ne in mutum ya yi haƙuri cikin zafin wahalar rashin adalci saboda yana sane da Allah.
Nebo toť jest milé, jestliže kdo pro svědomí Boží snáší zámutky, trpě bez viny.
20 Amma ina abin taƙama in kuka sha duka saboda kun yi laifi kuka kuma jimre? Sai dai in kuka sha wahala saboda yin nagari kuka kuma jimre, abin yabo ne a gaban Allah.
Nebo jaká jest chvála, byste pak i snášeli pohlavkování, hřešíce? Ale jestliže dobře činíce, a bez viny trpíce, snášíte, toť jest milé před Bohem.
21 Ga wannan ne aka kira ku, domin Kiristi ya sha wahala dominku, ya bar muku gurbin da ya kamata ku bi.
Nebo i k tomu povoláni jste, jako i Kristus trpěl za nás, nám pozůstaviv příklad, abyste následovali šlepějí jeho.
22 “Bai taɓa yin laifi ba sam, ba a kuma sami ƙarya a bakinsa ba.”
Kterýž hříchu neučinil, aniž jest lest nalezena v ústech jeho.
23 Sa’ad da suka zazzage shi, bai rama ba; sa’ad da ya sha wahala, bai yi barazana ba. A maimakon haka, ya miƙa kansa ga wanda yake shari’ar adalci.
Kterýžto, když mu zlořečili, nezlořečil zase; trpěv, nehrozil, ale poroučel tomu, kterýž spravedlivě soudí.
24 Shi kansa ya ɗauki zunubanmu a jikinsa a kan itace, domin mu mutu ga zunubai mu kuma rayu ga adalci; ta wurin raunukansa ne kuka sami warkarwa.
Kterýžto hříchy naše na svém těle sám vnesl na dřevo, abychom hříchům zemrouce, spravedlnosti živi byli, jehož zsinalostí uzdraveni jste.
25 Gama dā kuna kama da tumakin da suka ɓace, amma yanzu kun dawo ga Makiyayi da kuma Mai lura da rayukanku.
Nebo jste byli jako ovce bloudící, ale nyní obráceni jste ku pastýři a biskupu duší svých.

< 1 Bitrus 2 >