< 1 Sarakuna 9 >

1 Sa’ad da Solomon ya gama ginin haikalin Ubangiji da kuma fadan sarki, ya kuma yi dukan abin da yake so yă yi,
And it cometh to pass, at Solomon's finishing to build the house of Jehovah, and the house of the king, and all the desire of Solomon that he delighted to do,
2 sai Ubangiji ya bayyana gare shi sau na biyu, kamar yadda ya bayyana masa a Gibeyon.
that Jehovah appeareth unto Solomon a second time, as He appeared unto him in Gibeon,
3 Ubangiji ya ce masa, “Na ji addu’arka da kuma roƙon da ka yi a gabana; na tsarkake wannan haikali wanda ka gina, ta wurinsa Sunana zai kasance a can har abada. Idanuna da zuciyata kullum za su kasance a can.
and Jehovah saith unto him, 'I have heard thy prayer and thy supplication with which thou hast made supplication before Me; I have hallowed this house that thou hast built to put My name there — unto the age, and Mine eyes and My heart have been there all the days.
4 “Kai kuwa, in ka yi tafiya a gabana da mutunci a zuci da kuma gaskiya, kamar yadda Dawuda mahaifinka ya yi, ka yi dukan abin da na umarta, ka kuma yi biyayya da ƙa’idodina da kuma dokokina,
'And thou — if thou dost walk before Me as David thy father walked, in simplicity of heart, and in uprightness, to do according to all that I have commanded thee — My statutes and My judgments thou dost keep —
5 zan kafa kujerar sarautarka a bisa Isra’ila har abada, kamar yadda na alkawarta wa Dawuda mahaifinka sa’ad da na ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani a kan kujerar sarautar Isra’ila ba.’
then I have established the throne of thy kingdom over Israel — to the age, as I spake unto David thy father, saying, There is not cut off to thee a man from [being] on the throne of Israel.
6 “Amma in kai, ko’ya’yanka maza, suka juye daga gare ni, ba ku kuma kiyaye umarnai da ƙa’idodin da na ba ku ba, kuka yi gaba, kuka bauta wa waɗansu alloli, kuka kuma yi musu sujada,
'If ye at all turn back — you and your sons — from after Me, and keep not My commands — My statutes, that I have set before you, and ye have gone and served other gods, and bowed yourselves to them,
7 sai in yanke mutanen Isra’ila daga ƙasar da na ba su, in kuma ƙi wannan haikalin da na tsarkake domin Sunana. Isra’ila kuwa za tă zama abin gori da abin dariya a cikin dukan mutane.
then I have cut off Israel from the face of the ground that I have given to them, and the house that I have hallowed for My name I send away from My presence, and Israel hath been for a simile and for a byword among all the peoples;
8 Wannan haikali zai zama tarin juji. Duk wanda ya wuce ta hanyan nan kuwa zai ji tausayi, yă kuma yi tsaki yana cewa, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi haka ga wannan ƙasa da kuma wannan haikali?’
as to this house, [that] is high, every one passing by it is astonished, and hath hissed, and they have said, Wherefore hath Jehovah done thus to this land and to this house?
9 Mutane za su amsa su ce, ‘Saboda sun yashe Ubangiji Allahnsu, wanda ya fitar da su daga Masar, suka rungumi waɗansu alloli, suna yin musu sujada, suna bauta musu ne, ya sa Ubangiji ya kawo dukan masifan nan a kansu.’”
and they have said, Because that they have forsaken Jehovah their God, who brought out their fathers from the land of Egypt, and they lay hold on other gods, and bow themselves to them, and serve them; therefore hath Jehovah brought in upon them all this evil.'
10 A ƙarshen shekaru ashirin da Solomon ya ɗauka yana gina haikalin Ubangiji da fadan sarki,
And it cometh to pass, at the end of twenty years, that Solomon hath built the two houses, the house of Jehovah, and the house of the king.
11 sai Sarki Solomon ya ba wa Hiram sarkin Taya garuruwa ashirin a yankin Galili, gama Hiram ya tanada masa da dukan katakai al’ul da na fir, da kuma zinariyar da ya bukaci domin aiki.
Hiram king of Tyre hath assisted Solomon with cedar-trees, and with fir-trees, and with gold, according to all his desire; then doth king Solomon give to Hiram twenty cities in the land of Galilee.
12 Amma sa’ad da Hiram ya zo daga Taya don yă ga garuruwan da Solomon ya ba shi, sai bai ji daɗi ba.
And Hiram cometh out from Tyre to see the cities that Solomon hath given to him, and they have not been right in his eyes,
13 Sai ya ce, “Wanda irin garuruwa ke nan ka ba ni, ɗan’uwana?” Saboda haka ya kira su Ƙasar Kabul, sunan da suke da shi har wa yau.
and he saith, 'What [are] these cities that thou hast given to me, my brother?' and one calleth them the land of Cabul unto this day.
14 Hiram kuwa ya aika wa sarki talenti 120 na zinariya.
And Hiram sendeth to the king a hundred and twenty talents of gold.
15 Ga lissafin ma’aikatan gandun da Sarki Solomon ya ɗauka don ginin haikalin Ubangiji, da fadarsa, da madogaran gini, da katangar Urushalima, da kuma Hazor Megiddo da Gezer.
And this [is] the matter of the tribute that king Solomon hath lifted up, to build the house of Jehovah, and his own house, and Millo, and the wall of Jerusalem, and Hazor, and Megiddo, and Gezer,
16 (Fir’auna sarkin Masar ya kai wa Gezer hari, ya kuma ci ta da yaƙi. Ya sa mata wuta, ya kashe Kan’aniyawanta mazaunan wurin, ya kuma ba da ita a matsayin kyautar aure ga’yarsa, matar Solomon.
(Pharaoh king of Egypt hath gone up and doth capture Gezer, and doth burn it with fire, and the Canaanite who is dwelling in the city he hath slain, and giveth it [with] presents to his daughter, wife of Solomon.)
17 Solomon kuwa ya sāke gina Gezer.) Ya gina Bet-Horon ta Kwari,
And Solomon buildeth Gezer, and Beth-Horon the lower,
18 da Ba’alat, da Tadmor a hamada, na cikin ƙasarsa.
and Baalath, and Tadmor in the wilderness, in the land;
19 Haka kuma ya gina dukan biranen ajiyarsa, da garuruwa domin kekunan yaƙinsa, da garuruwa domin dawakansa. Ya gina duk abin da ya so yă ginawa a Urushalima, da Lebanon, da kuma ko’ina a dukan yankin da ya yi mulki.
and all the cities of stores that king Solomon hath, and the cities of the chariots, and the cities of the horsemen, and the desire of Solomon that he desired to build in Jerusalem, and in Lebanon, and in all the land of his dominion.
20 Dukan Amoriyawa, da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Hiwiyawa da Yebusiyawan da suka ragu a ƙasar (waɗanda ba Isra’ilawa ba ne),
The whole of the people that is left of the Amorite, the Hittite, the Perizzite, the Hivite, and the Jebusite, who [are] not of the sons of Israel —
21 wato, waɗanda suka ragu a ƙasar, waɗanda Isra’ilawa ba su iya hallakawa ba, su ne Solomon ya ɗauka su zama bayinsa don aikin gandu, kamar yadda yake har wa yau.
their sons who are left behind them in the land, whom the sons of Israel have not been able to devote — he hath even lifted up [on] them a tribute of service unto this day.
22 Amma Solomon bai mai da Isra’ilawa bayi ba; su ne mayaƙansa, shugabannin gwamnatinsa, dogarawansa, shugabannin sojojinsa, da shugabanninsa na kekunan yaƙi da mahayan kekunan yaƙinsa.
And out of the sons of Israel Solomon hath not appointed a servant, for they [are] the men of war, and his servants, and his heads, and his captains, and the heads of his chariots, and his horsemen.
23 Su ne kuma manyan shugabanni masu lura da ayyukan Solomon, su ne shugabanni 550 masu lura da mutanen da suke aiki.
These [are] the heads of the officers who [are] over the work of Solomon, fifty and five hundred, those ruling among the people who are labouring in the work.
24 Bayan’yar Fir’auna ta haura daga Birnin Dawuda zuwa fadan da Solomon ya gina mata, sai ya gina madogaran gini.
Only, the daughter of Pharaoh went up out of the city of David unto her house that [Solomon] built for her; then he built Millo.
25 Sau uku a shekara Solomon kan miƙa hadayun ƙonawa da hadayun salama a kan bagaden da ya gina wa Ubangiji, yana ƙone turare a gaban Ubangiji haɗe da su, ta haka ya cika abin da ake bukata na haikali.
And Solomon caused to ascend, three times in a year, burnt-offerings and peace-offerings on the altar that he built to Jehovah, and he perfumed it with that which [is] before Jehovah, and finished the house.
26 Sarki Solomon ya kuma gina jiragen ruwa a Eziyon Geber, wadda take kusa da Elot a Edom, a bakin Jan Teku.
And a navy hath king Solomon made in Ezion-Geber, that is beside Eloth, on the edge of the Sea of Suph, in the land of Edom.
27 Hiram kuwa ya aiki mutanensa, masu tuƙan jirgin ruwa waɗanda suka san teku, don su yi hidima a jerin jiragen ruwa tare da mutanen Solomon.
And Hiram sendeth in the navy his servants, shipmen knowing the sea, with servants of Solomon,
28 Suka tafi Ofir suka kuma dawo da talenti 420 na zinariya, wanda suka ba wa Sarki Solomon.
and they come in to Ophir and take thence gold, four hundred and twenty talents, and bring [it] in unto king Solomon.

< 1 Sarakuna 9 >