< 1 Sarakuna 4 >

1 Sai Sarki Solomon ya yi mulki a bisa dukan Isra’ila.
And King Solomon is king over all Israel,
2 Waɗannan su ne manyan shugabanninsa. Azariya ɗan Zadok shi ne firist;
and these [are] the heads whom he has: Azariah son of Zadok [is] the priest;
3 Elihoref da Ahiya,’ya’yan Shisha maza, su ne marubuta. Yehoshafat ɗan Ahilud, shi ne mai lura da takardu.
Elihoreph and Ahiah sons of Shisha [are] scribes; Jehoshaphat son of Ahilud [is] remembrancer;
4 Benahiya ɗan Yehohiyada, shi ne shugaban mayaƙa. Zadok da Abiyatar, su ne firistoci.
and Benaiah son of Jehoiada [is] over the host; and Zadok and Abiathar [are] priests;
5 Azariya ɗan Natan, shi ne mai lura da shugabannin yanki. Zabud ɗan Natan, shi ne firist da kuma mai wa sarki shawara.
and Azariah son of Nathan [is] over the officers; and Zabud son of Nathan [is] minister, friend of the king;
6 Ahishar, shi ne sarkin fada. Adoniram ɗan Abda, shi ne mai lura da aikin gandu.
and Ahishar [is] over the household, and Adoniram son of Abda [is] over the tribute.
7 Solomon yana da gwamnoni yankuna goma sha biyu a bisa dukan Isra’ila, waɗanda suke tanaji abinci domin sarki da kuma gidan sarauta. Kowanne yakan tanada abinci na wata ɗaya a shekara.
And Solomon has twelve officers over all Israel, and they have sustained the king and his household—a month in the year is on each one for sustenance;
8 Ga sunayensu, Ben-Hur, shi ne a ƙasar tudun Efraim;
and these [are] their names: Ben-Hur in the hill-country of Ephraim;
9 Ben-Deker, shi ne a Makaz, Sha’albim, Bet-Shemesh da Elon Bet-Hanan;
Ben-Dekar in Makaz, and Shaalbim, and Beth-Shemesh, and Elon-Beth-Hanan;
10 Ben-Hesed, shi ne a Arubbot (Soko da dukan ƙasar Hefer);
Ben-Hesed, in Aruboth, has Sochoh and all the land of Hepher;
11 Ben-Abinadab, shi ne a Nafot Dor (ya auri Tafat’yar Solomon);
Ben-Abinadab [has] all the elevation of Dor; Taphath daughter of Solomon became his wife;
12 Ba’ana ɗan Ahilud, shi ne a Ta’anak da Megiddo, da kuma dukan Bet-Sheyan biye da Zaretan ƙasa da Yezireyel, daga Bet-Sheyan zuwa Abel-Mehola a ƙetaren Yokmeyam;
Baana Ben-Ahilud [has] Taanach and Megiddo, and all Beth-Shean, which [is] by Zartanah beneath Jezreel, from Beth-Shean to Abel-Meholah, to beyond Jokneam;
13 Ben-Geber, shi ne a Ramot Gileyad (Mazaunan Yayir ɗan Manasse a Gileyad suna a ƙarƙashinsa, haka ma yankin Argob a Bashan tare da manyan biranen sittin masu katanga da suke da ƙyamare na tagulla);
Ben-Geber, in Ramoth-Gilead, has the small towns of Jair son of Manasseh, which [are] in Gilead; he has a portion of Argob that [is] in Bashan—sixty great cities [with] wall and bronze bar;
14 Ahinadab ɗan Iddo, shi ne a Mahanayim;
Ahinadab son of Iddo [has] Mahanaim;
15 Ahimawaz, shi ne a Naftali (ya auri Basemat’yar Solomon);
Ahimaaz [is] in Naphtali; he also has taken Basemath daughter of Solomon for a wife;
16 Ba’ana ɗan Hushai, shi ne a Asher da Bayelot;
Baanah Ben-Hushai [is] in Asher, and in Aloth;
17 Yehoshafat ɗan Faruwa, shi ne a Issakar;
Jehoshaphat Ben-Paruah [is] in Issachar;
18 Shimeyi ɗan Ela, shi ne a Benyamin;
Shimei Ben-Elah [is] in Benjamin;
19 Geber ɗan Uri, shi ne a Gileyad (ƙasar Sihon sarkin Amoriyawa da kuma Og sarkin Bashan). Shi ne kaɗai gwamna a bisa yankin.
Geber Ben-Uri [is] in the land of Gilead, the land of Sihon king of the Amorite, and of Og king of Bashan: and [he is] the one officer who [is] in the land.
20 Mutanen Yahuda da na Isra’ila sun yi yawa sai ka ce yashi a bakin teku. Suka ci, suka sha, suka kuma yi farin ciki.
Judah and Israel [are] many, as the sand that [is] by the sea for multitude, eating and drinking and rejoicing.
21 Solomon kuwa ya yi mulki a bisa dukan masarautai daga Kogi zuwa ƙasar Filistiyawa, har zuwa iyakar Masar. Waɗannan ƙasashe sun yi ta kawo haraji, suka kuma zama bayin Solomon dukan kwanakin ransa.
And Solomon has been ruling over all the kingdoms, from the River [to] the land of the Philistines and to the border of Egypt: they are bringing a present near, and serving Solomon, all [the] days of his life.
22 Tanajin Solomon na kowace rana su ne, garwa talatin na garin abinci,
And the provision of Solomon for one day is thirty cors of flour, and sixty cors of meal,
23 shanun da aka yi kiwo a gida guda goma, shanu ashirin da suka ƙoshi daga kiwo, tumaki da awaki ɗari; ban da ƙishimai, bareyi, batsiyoyi, da kaji masu ƙiba.
ten fat oxen, and twenty feeding oxen, and one hundred sheep, apart from deer, and roe, and fallow-deer, and fatted beasts of the stalls,
24 Gama ya yi mulki a bisa dukan masarautai yamma da Kogi, daga Tifsa zuwa Gaza, aka kuwa sami zaman lafiya a kowane gefe.
for he is ruling over all beyond the river, from Tiphsah and to Gaza, over all the kings beyond the River, and he has peace from all his surrounding servants.
25 A kwanakin da Solomon yake raye, Yahuda da Isra’ila, daga Dan zuwa Beyersheba, sun zauna lafiya, kowane mutum ya zauna a ƙarƙashin itacen inabi da na ɓaurensa.
And Judah dwells—and Israel—in confidence, each under his vine, and under his fig tree, from Dan even to Beer-Sheba, all the days of Solomon.
26 Solomon yana da rumfunan dawakai masu jan kekunan yaƙi, dubu huɗu, da kuma dawakai dubu goma sha biyu
And Solomon has forty thousand stalls of horses for his chariots, and twelve thousand horsemen.
27 Shugabannin yankuna, kowanne a watansa yakan yi tanajin abinci domin Sarki Solomon da kuma duk wanda ya zo teburin sarki. Sun tabbatar ba a rasa kome ba.
And these officers have sustained King Solomon and everyone drawing near to the table of King Solomon, each [in] his month; they let nothing be lacking.
28 Kowa a cikinsu, bisa ga lokacin da aka ba shi, yakan kai hatsin sha’ir da ciyawa domin dawakan-kekunan yaƙi, da sauran dawakai a inda aka ajiye su.
And the barley and the straw, for horses and for dromedaries, they bring to the place where they are, each according to his ordinance.
29 Allah ya ba Solomon hikima da hangen nesa mai girma, da kuma fāɗin fahimta marar iyaka, kamar yashi a bakin teku.
And God gives very much wisdom and understanding to Solomon, and breadth of heart, as the sand that [is] on the edge of the sea;
30 Hikimar Solomon ta fi hikimar mutanen Gabas, ta kuma fi dukan hikimar Masar girma.
and the wisdom of Solomon is greater than the wisdom of any of the sons of the east, and [greater] than all the wisdom of Egypt;
31 Ya fi kowane mutum hikima, har da Etan dangin Ezra ma. Yana da hikima fiye da Heman, Kalkol da Darda,’ya’yan Mahol maza. Sunansa ya bazu ko’ina a ƙasashen da suke kewaye.
and he is wiser than all men, [wiser] than Ethan the Ezrahite, and Heman, and Chalcol, and Darda, sons of Mahol, and his name is in all the surrounding nations.
32 Ya yi karin magana dubu uku. Waƙoƙinsa kuwa sun kai dubu ɗaya da biyar.
And he speaks three thousand allegories, and his songs [are] one thousand and five;
33 Ya yi magana a kan rayuwar itatuwa, daga al’ul na Lebanon zuwa hizzob da yake girma a bangaye. Ya kuma yi koyarwa game da dabbobi, da tsuntsaye, da abubuwa masu rarrafe, da kuma kifi.
and he speaks concerning the trees, from the cedar that [is] in Lebanon, even to the hyssop that is coming out in the wall, and he speaks concerning the livestock, and concerning the bird, and concerning the creeping things, and concerning the fishes,
34 Mutane suka yi ta zuwa daga ƙasashe dabam-dabam don su ji hikimar Solomon. Sarakuna daga ko’ina a duniya, sun ji labarin hikimarsa, suka kuma aika da mutane don su ji shi.
and there come out [those] of all the peoples to hear the wisdom of Solomon, from all kings of the earth who have heard of his wisdom.

< 1 Sarakuna 4 >