< 1 Sarakuna 18 >

1 Bayan dogon lokaci, a cikin shekara ta uku, maganar Ubangiji ta zo wa Iliya, ta ce, “Tafi, ka gabatar da kanka ga Ahab, zan kuwa aika da ruwan sama a ƙasar.”
Après beaucoup de jours, la parole de Yahweh fut adressée à Elie, dans la troisième année, en ces termes: « Va, parais devant Achab, et je ferai tomber de la pluie sur la face du sol. »
2 Saboda haka Iliya ya tafi ya gabatar da kansa ga Ahab. Yanzu dai yunwa ta tsananta a Samariya,
Et Elie partit, pour se présenter devant Achab. La famine était devenue grande à Samarie,
3 Ahab kuma ya aika a kawo Obadiya, sarkin fadansa (Obadiya dai cikakken mai gaskata da Ubangiji ne.
Achab fit appeler Abdias, chef de sa maison. — Or Abdias craignait beaucoup Yahweh,
4 Yayinda Yezebel tana kisan annabawan Ubangiji, Obadiya ya ɗauki annabawa ɗari ya ɓoye a kogwanni biyu, hamsin a kowanne, ya kuma tanada musu abinci da kuma ruwa.)
car, lorsque Jézabel massacra les prophètes de Yahweh, Abdias prit cent prophètes et les cacha cinquante par cinquante dans des cavernes, où il les nourrit de pain et d'eau. —
5 Ahab ya ce wa Obadiya, “Ka ratsa ƙasar zuwa dukan maɓulɓulai da fadamu. Mai yiwuwa ka sami ciyawa mu ba dawakai da alfadarai don su rayu, don kada mu kashe dabbobinmu.”
Achab dit à Abdias: « Va par le pays vers toutes les sources d'eau et vers tous les torrents; peut-être se trouvera-t-il de l'herbe, et nous conserverons la vie aux chevaux et aux mulets, et nous n'aurons pas à abattre de bétail. »
6 Saboda haka suka raba ƙasar da za su ratsa, Ahab zai tafi gefe ɗaya, Obadiya kuma yă bi gefe ɗaya.
Ils se partagèrent le pays pour le parcourir; Achab alla seul par un chemin, et Abdias alla seul par un autre chemin.
7 Yayinda Obadiya yana tafiya, sai Iliya ya sadu da shi. Obadiya ya gane shi, ya rusuna har ƙasa, ya ce, “Kai ne, shugabana, Iliya?”
Comme Abdias était en route, voici qu'Elie le rencontra. Abdias, l'ayant reconnu, tomba sur son visage et dit: « Est-ce toi, mon seigneur Elie? »
8 Iliya ya amsa, ya ce, “I, je ka faɗa wa maigidanka cewa, ‘Iliya yana a nan.’”
Il lui répondit: « C'est moi; va dire à ton maître: Voici Elie! »
9 Obadiya ya yi tambaya, “Me na yi da ba daidai ba, da kake miƙa bawanka ga Ahab don yă kashe?
Et Abdias dit: « Quel péché ai-je commis, que tu livres ton serviteur entre les mains d'Achab, pour qu'il me fasse mourir?
10 Na rantse da Ubangiji Allahnka, babu al’umma ko masarauta da mai girma sarki bai aika a nemo ka ba. In suka ce ba ka can, sai yă sa mulkin ko al’ummar su rantse, cewa ai, ba su same ka ba.
Yahweh, ton Dieu, est vivant! Il n'y a ni nation ni royaume où mon maître n'ait envoyé pour te chercher; et quand on disait: Elie n'est pas ici, il faisait jurer le royaume et la nation qu'on ne t'avait pas trouvé.
11 Amma yanzu kana faɗa mini in tafi wurin mai girma in ce, ‘Iliya yana a nan.’
Et maintenant tu me dis: Va dire à ton maître: Voici Elie!
12 Ban san inda Ruhun Ubangiji zai kai ka sa’ad da na bar ka ba. In na tafi na faɗa wa Ahab bai kuma same ka a nan ba, zai sa a kashe ni. Tuna fa, ni bawanka, na yi wa Ubangiji sujada tun ina saurayi.
Et lorsque je t'aurai quitté, l'Esprit de Yahweh te transportera je ne sais où; et j'irai informer Achab, qui ne te trouvera pas et me tuera. Cependant ton serviteur craint Yahweh dès sa jeunesse.
13 Ranka yă daɗe, ashe, ba a faɗa maka abin da na yi lokacin da Yezebel ta karkashe annabawan Ubangiji ba? Yadda na ɓoye annabawa ɗari, na sa su hamsin-hamsin a kogwanni biyu, na yi ta ba su abinci da ruwa.
N'a-t-on pas dit à mon seigneur ce que j'ai fait quand Jézabel a massacré les prophètes de Yahweh? J'ai caché cent des prophètes de Yahweh, cinquante par cinquante, dans des cavernes, et je les ai nourris de pain et d'eau.
14 Yanzu fa, kana ce in tafi wurin mai girma sarki, in ce, ‘Iliya yana a nan.’ Ai, zai kashe ni!”
Et maintenant tu dis: Va dire à ton maître: Voici Elie! Il me tuera. »
15 Iliya ya ce, “Na rantse da Ubangiji Maɗaukaki, wanda nake bauta wa, tabbatacce zan gabatar da kaina ga Ahab a yau.”
Mais Elie dit: « Yahweh des armées, devant qui je me tiens, est vivant! Aujourd'hui je me présenterai devant Achab. »
16 Saboda haka sai Obadiya ya tafi wurin Ahab ya faɗa masa, Ahab kuwa ya tafi wurin Iliya.
Abdias alla à la rencontre d'Achab et lui apprit la nouvelle; et Achab se rendit au-devant d'Elie.
17 Sa’ad da Ahab ya ga Iliya, sai ya ce masa, “Kai ne wannan, kai mai tā-da-na-zaune-tsaye a Isra’ila?”
Dès qu'Achab aperçut Elie, Achab lui dit: « Toi ici, le perturbateur d'Israël? »
18 Iliya ya amsa, ya ce, “Ban tā-da-na-zaune-tsaye a Isra’ila ba. Amma kai da iyalin mahaifinka, ku kuka tā-da-na-zaune-tsaye. Ka ƙyale umarnai Ubangiji, ka bi Ba’al.
Elie répondit: « Je ne trouble point Israël; c'est toi, au contraire, et la maison de ton père, en ce que vous avez abandonné les commandements de Yahweh et que tu es allé après les Baals.
19 Yanzu ka tara mutane daga dukan Isra’ila su sadu da ni a kan Dutsen Karmel. Ka kuma kawo annabawa ɗari huɗu da hamsin na Ba’al, da kuma annabawa ɗari huɗu na Ashera, waɗanda suke ci a teburin Yezebel.”
Maintenant, envoie rassembler tout Israël auprès de moi, à la montagne du Carmel, ainsi que les quatre cent cinquante prophètes de Baal et les quatre cents prophètes d'Astarté, qui mangent de la table de Jézabel. »
20 Sai Ahab ya aika a duk fāɗin Isra’ila, ya kuma tattara annabawan a kan Dutsen Karmel.
Achab envoya des messagers vers tous les enfants d'Israël, et rassembla les prophètes à la montagne du Carmel.
21 Iliya ya je gaban mutane ya ce, “Har yaushe za ku yi ta yawo tsakanin ra’ayoyi biyu? In Ubangiji ne Allah, ku bi shi; amma in Ba’al Allah ne, ku bi shi.” Mutane dai ba su ce uffam ba.
Alors Elie s'approcha de tout le peuple et dit: « Jusques à quand clocherez-vous des deux côtés? Si Yahweh est Dieu, allez après lui; si c'est Baal, allez après lui! » Le peuple ne lui répondit rien.
22 Sai Iliya ya ce musu, “Ni ne kaɗai annabin Ubangiji da ya rage, amma Ba’al yana da annabawa ɗari huɗu da hamsin.
Et Elie dit au peuple: « Je suis resté seul des prophètes de Yahweh, et il y a quatre cent cinquante prophètes de Baal.
23 Ku samo mana bijimai biyu. Bari su zaɓa ɗaya wa kansu, bari kuma su yanka shi kucu-kucu su sa a itace, sai dai, kada su sa wuta a kansa. Ni kuwa zan shirya ɗaya bijimin in sa a kan itace, ni ma, ba zan sa wuta a kansa ba.
Que l'on nous donne deux taureaux; qu'ils choisissent pour eux l'un des taureaux, qu'ils le coupent par morceaux et qu'ils le placent sur le bois, sans y mettre le feu; et moi je préparerai l'autre taureau, et je le placerai sur le bois, sans y mettre le feu.
24 Sa’an nan ku kira bisa sunan allahnku, ni kuwa zan kira bisa sunan Ubangiji. Duk allahn da ya amsa ta wurin wuta, shi ne Allah.” Sai dukan jama’a suka ce, “Abin nan da faɗa yana da kyau.”
Puis invoquez le nom de votre dieu, et moi j'invoquerai le nom de Yahweh. Le dieu qui répondra par le feu, celui-là est Dieu. » Tout le peuple répondit en disant: « C'est bien! »
25 Iliya ya ce wa annabawan Ba’al, “Ku ku fara zaɓi bijimi ɗaya, ku shirya, da yake kuna da yawa. Ku kira a bisa sunan allahnku, amma kada ku ƙuna wuta.”
Elie dit aux prophètes de Baal: « Choisissez pour vous l'un des taureaux, préparez-le d'abord, car vous êtes les plus nombreux, et invoquez le nom de votre dieu, mais ne mettez pas le feu. »
26 Sai suka ɗauki bijimin da aka ba su suka shirya shi. Sa’an nan suka kira bisa sunan Ba’al daga safe har tsakar rana. Suna ihu, “Ya Ba’al, ka amsa mana!” Amma babu wata amsa, babu wani da ya amsa. Suka yi ta rawa kewaye da bagaden da suka yi.
Ils prirent le taureau qu'on leur donna et le préparèrent; et ils invoquèrent le nom de Baal depuis le matin jusqu'à midi, en disant: « Baal, réponds-nous! » Mais il n'y eut ni voix ni réponse. Et ils sautaient devant l'autel qu'ils avaient fait.
27 Da tsakar rana, Iliya ya fara yin musu ba’a. Ya ce, “Ku yi ihu da ƙarfi, tabbatacce shi allah ne! Mai yiwuwa yana cikin zurfin tunani, ko dai aiki ya yi masa yawa, ko ya yi tafiya. Mai yiwuwa yana barci ne, dole a tashe shi.”
A midi, Elie se moqua d'eux et dit: « Criez à haute voix, car il est dieu; il est en méditation, ou il est occupé, ou il est en voyage; peut-être qu'il dort, et il se réveillera. »
28 Sai suka yi ta ihu da ƙarfi suna tsattsaga kansu da takuba da māsu, yadda al’adarsu take, sai da jininsu ya yi ta zuba.
Et ils crièrent à haute voix, et ils se firent, selon leur coutume, des incisions avec des épées et avec des lances, jusqu'à ce que le sang coulât sur eux.
29 Tsakar rana ta wuce, suka ci gaba da ƙoƙari, suna annabci har lokacin miƙa hadayar yamma ya yi. Amma babu wani da ya tanƙa, babu wani da ya amsa, babu wanda ya kula.
Lorsque midi fut passé, ils prophétisèrent jusqu'au moment où l'on présente l'oblation. Mais il n'y eut ni voix, ni réponse, ni signe d'attention.
30 Sa’an nan Iliya ya ce wa dukan mutane, “Ku zo nan wurina.” Suka zo wurinsa, ya kuma shirya bagaden Ubangiji, da ya riga ya zama kufai.
Elie dit à tout le peuple: « Approchez-vous de moi. » Tout le peuple s'étant approché de lui, Elie rétablit l'autel de Yahweh, qui avait été renversé.
31 Iliya ya ɗauki duwatsu goma sha biyu, ɗaya don kowace kabila zuriyar Yaƙub, wanda maganar Ubangiji ta zo masa, cewa, “Sunanka zai zama Isra’ila.”
Elie prit douze pierres, d'après le nombre des tribus des fils de Jacob, auquel la parole de Yahweh avait été adressée en ces termes: « Israël sera ton nom. »
32 Da waɗannan duwatsun ya gina bagade cikin sunan Ubangiji, ya kuma haƙa wuriya kewaye da shi, isashe da zai ci garwa biyu na irin ƙwayar gyada.
Il bâtit avec ces pierres un autel au nom de Yahweh; puis, ayant fait autour de l'autel un fossé de la capacité de deux mesures de semence,
33 Ya shirya itace, ya yayyanka bijimin kucu-kucu, ya shimfiɗa shi a itacen. Sa’an nan ya ce musu, “Ku cika manyan tuluna da ruwa, ku zuba a kan hadayar da kuma a kan itacen.” Suka zuba.
il arrangea le bois, coupa le taureau par morceaux et le plaça sur le bois.
34 Ya ce, “Ku sāke yin haka,” sai suka sāke yin haka. Ya umarta, “Ku yi haka sau na uku,” suka kuma yi haka sau na uku.
Et il dit: « Remplissez d'eau quatre cruches, et versez-les sur l'holocauste et sur le bois. » Il dit: « Faites-le une seconde fois »; et ils le firent une seconde fois. Il dit: « Faites le une troisième fois »; et ils le firent une troisième fois.
35 Ruwan ya gangara kewaye da bagaden har ma ya cika wuriyar.
L'eau coula autour de l'autel, et il fit remplir aussi d'eau le fossé.
36 A lokacin hadaya, sai annabi Iliya ya zo gaba ya yi addu’a, ya ce, “Ya Ubangiji Allah na Ibrahim, na Isra’ila da kuma na Yaƙub, bari a sani a yau cewa kai Allah ne a cikin Isra’ila, a kuma san cewa ni bawanka ne, na kuma yi dukan waɗannan abubuwa bisa umarninka.
A l'heure où l'on offre l'oblation du soir, Elie, le prophète, s'avança et dit: « Yahweh, Dieu d'Abraham, d'Isaac et d'Israël, que l'on sache aujourd'hui que vous êtes Dieu en Israël, que je suis votre serviteur et que j'ai fait toutes ces choses sur votre parole.
37 Ka amsa mini, ya Ubangiji, ka amsa mini, saboda waɗannan mutane su san cewa kai, ya Ubangiji, kai ne Allah, su kuma san cewa kana sāke juye zukatansu zuwa gare ka.”
Exaucez-moi, Yahweh, exaucez-moi! Afin que ce peuple reconnaisse que vous, Yahweh, êtes Dieu, et que c'est vous qui ramenez leur cœur en arrière. »
38 Sai wutar Ubangiji ya fāɗo, ya cinye hadayar, itacen, duwatsun da kuma ƙasar, ya lashe ruwan da yake cikin wuriyar.
Alors le feu de Yahweh tomba, et il consuma l'holocauste, le bois, les pierres et la terre, et absorba l'eau qui était dans le fossé.
39 Sa’ad da mutane suka ga wannan, sai suka rusuna, suka sunkuyar da kai suka ce, “Ubangiji, shi ne Allah! Ubangiji, shi ne Allah!”
Quand tout le peuple vit cela, ils tombèrent sur leur visage et ils dirent: « C'est Yahweh qui est Dieu! C'est Yahweh qui est Dieu! »
40 Sa’an nan Iliya ya umarce su, ya ce, “Ku kama annabawan Ba’al, kada ku bar waninsu yă tsere!” Suka kama su, Iliya kuwa ya sa aka gangara da su zuwa Kwarin Kishon, aka yayyanka su a can.
Et Elie leur dit: « Saisissez les prophètes de Baal; que pas un d'eux n'échappe! » Ils les saisirent, et Elie les fit descendre au torrent de Cison, où il les tua.
41 Sai Iliya ya ce wa Ahab, “Ka haura gida, ka ci, ka sha, gama ina jin motsin ruwan sama mai yawa.”
Elie dit à Achab: « Monte, mange et bois; car j'entends le bruissement de la pluie. »
42 Sai Ahab ya ruga don yă ci, yă sha, amma Iliya ya hau kan ƙwanƙolin Karmel, ya rusuna ƙasa, ya sa fuska a tsakanin gwiwarsa.
Achab monta pour manger et pour boire; mais Elie monta au sommet du Carmel et, se penchant vers la terre, il mit son visage entre ses genoux,
43 Ya ce wa bawansa, “Tafi ka dubi wajen teku.” Sai bawan ya haura ya duba. Ya ce, “Ba kome a can.” Sau bakwai Iliya ya ce, “Koma.”
et il dit à son serviteur: « Monte, regarde du côté de la mer. » Le serviteur monta et, ayant regardé, il dit: « Il n'y a rien. » Et Elie dit: « Retourne sept fois. »
44 Sau na bakwai, bawan ya ce, “Wani girgije ƙarami kamar hannun mutum yana tasowa daga teku.” Sai Iliya ya ce, “Je ka faɗa wa Ahab, ‘Shirya keken yaƙinka, ka gangara kafin ruwan sama yă tare ka.’”
A la septième fois, il dit: « Voici un petit nuage, comme la paume de la main d'un homme, qui s'élève de la mer. » Et Elie dit: « Va dire à Achab: Attelle et descends, afin que la pluie ne te surprenne pas. »
45 Ana cikin haka, sarari ya ƙara duhunta da girgije, iska ta taso, sai ruwan sama kamar da bakin kwarya ya sauko, Ahab kuwa ya hau zuwa Yezireyel.
En peu de temps, le ciel fut assombri par les nuages et le vent, et il tomba une forte pluie; et Achab, monté sur son char, s'en retourna à Jezrahel.
46 Ikon Ubangiji ya sauko a kan Iliya, ya sha ɗamara, ya ruga a guje a gaban Ahab har zuwa Yezireyel.
Et la main de Yahweh fut sur Elie; il se ceignit les reins et courut devant Achab, jusqu'à l'entrée de Jezrahel.

< 1 Sarakuna 18 >