< 1 Sarakuna 17 >

1 To, Iliya mutumin Tishbe, daga Tishbe a Gileyad, ya ce wa Ahab, “Muddin Ubangiji, Allah na Isra’ila wanda nake bauta wa yana a raye, ba za a yi raɓa ko ruwan sama a’yan shekaru masu zuwa ba, sai ko na faɗa haka.”
Then said Elijah the Tishbite, who was of the inhabitants of Gil'ad, unto Achab, As the Lord the God of Israel liveth, before whom I have stood, there shall not be in these years dew or rain, except according to my word.
2 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Iliya, ta ce,
And the word of the Lord came unto him, saying,
3 “Ka bar nan, ka nufi wajajen gabas, ka ɓuya a Rafin Kerit, gabas da Urdun.
Go away from here, and turn thyself eastward, and hide thyself by the brook Kerith, which is to the east of the Jordan.
4 Za ka sha daga rafin, zan kuma umarci hankaki su ciyar da kai a can.”
And it shall be, that out of the brook shalt thou drink; and the ravens have I ordained to sustain thee there.
5 Saboda haka sai Iliya ya yi abin da Ubangiji ya faɗa masa. Ya tafi Rafin Kerit, gabas da Urdun, ya zauna a can.
And he went and did according to the word of the Lord; and he went and remained by the brook Kerith, that is to the east of the Jordan.
6 Hankaki suka riƙa kawo masa abinci da nama, safe da yamma, ya kuma sha daga rafin.
And the ravens brought him bread and flesh in the morning, and bread and flesh in the evening: and out of the brook he used to drink.
7 Ana nan sai rafin ya bushe saboda ba a yi ruwan sama a ƙasar ba.
And it came to pass after a while that the brook dried up; because there had been no rain in the land.
8 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Iliya cewa,
And the word of the Lord came unto him, saying,
9 “Je ka, nan take, zuwa Zarefat na Sidon, ka zauna a can. Na umarci wata gwauruwa a can tă ciyar da kai.”
Arise, go unto Zarephath, which belongeth to Zidon, and remain there: behold, I have ordained there a widow-woman to sustain thee.
10 Saboda haka sai ya tafi Zarefat. Sa’ad da ya isa ƙofar gari, sai ga wata gwauruwa tana tattara’yan itace. Sai ya kira ta, ya ce, “Ki kawo mini ɗan ruwa a tulu don in sha.”
So he arose and went to Zarephath; and when he came to the gate of the city, behold, there was there a widow-woman gathering sticks of wood: and he called her, and said, Fetch me, I pray thee, a little water in a vessel, that I may drink.
11 Da ta kama hanya za tă tafi tă kawo, sai ya sāke kiranta ya ce, “Ina roƙonki, ki kuma kawo mini ɗan abinci.”
And as she went to fetch it, he called to her, and said, Bring me, I pray thee, a morsel of bread in thy hand.
12 Sai ta ce masa, “Na rantse da Ubangiji Allahnka, ba ni da wani abinci, sai dai ɗan gari hannu guda a tulu, da kuma ɗan mai a kwalaba. Ina tattara’yan itacen nan ne don in kai gida in yi abinci wa kaina da ɗana, don mu ci, mu mutu.”
And she said, As the Lord thy God liveth, I have nothing baked, but a handful of meal in a jar, and a little oil in a cruise: and, behold, I am gathering a couple of sticks, that I may go in and prepare it for me and my son; and when we have eaten it, we shall have to die.
13 Iliya ya ce mata, “Kada ki ji tsoro. Ki tafi gida, ki yi yadda kika ce. Amma da farko ki yi mini’yar wainar burodi daga abin da kike da shi ki kawo mini, sa’an nan ki yi wani abu wa kanki da kuma ɗanki.
And Elijah said unto her, Fear not; go and do as thou hast said; but make me thereof a little cake at first, and bring it out unto me, and for thee and for thy son shalt thou prepare [something] afterward.
14 Gama abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Tulun garin ba zai ƙare ba, kwalabar man kuma ba zai bushe ba sai ranar da Ubangiji ya bayar da ruwan sama a ƙasar.’”
For thus hath said the Lord the God of Israel, The jar of meal shall not fail, neither shall the cruise of oil diminish, until the day that the Lord giveth rain upon the face of the earth.
15 Sai ta tafi, ta yi yadda Iliya ya faɗa mata. Saboda haka aka kasance da abinci kowace rana wa Iliya da kuma don macen da iyalinta.
And she went and did according to the word of Elijah: and she, and he, and her household, did eat [many] days.
16 Gama tulun garin bai ƙare ba, kwalabar man kuma bai bushe ba, kamar yadda Ubangiji ya faɗa wa Iliya.
The jar of meal failed not, nor did the cruise of oil diminish, according to the word of the Lord, which he had spoken through means of Elijah.
17 Ana nan sai ɗan matan, wato, gwauruwan nan ya fara ciwo. Ciwon ya ƙara muni, daga ƙarshe sai ya daina numfashi.
And it came to pass after these events, that the son of the woman, the mistress of the house, fell sick; and his sickness became very severe, until that at length there was no breath left in him.
18 Sai ta ce wa Iliya, “Mutumin Allah, yaya haka? Ka zo ne domin ka nuna wa Allah zunubaina, ka kuma jawo mutuwar ɗana?”
And she said unto Elijah, What have I to do with thee, O man of God? thou art come unto me to call my sin to remembrance, and to slay my son!
19 Iliya ya ce, “Ki miƙa mini ɗanki.” Sai ya ɗauke shi daga hannuwanta, ya kai shi ɗakin sama inda yake zama, ya kwantar da shi a gadonsa.
And he said unto her, Give me thy son. And he took him out of her bosom, and carried him up into the upper chamber, in which he abode, and he laid him upon his own bed.
20 Sa’an nan ya yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Allahna, don me ka kawo wannan masifa a kan gwauruwan nan? Kai ka ce in zauna tare da ita, ga shi yanzu ɗanta ya mutu.”
And he called unto the Lord, and said, O Lord my God, hast thou also brought evil upon the widow with whom I sojourn, by slaying her son?
21 Sai ya kwanta, ya miƙe kansa a kan yaron sau uku, ya kuma yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Allahna, ka mai da ran yaron nan!”
And he stretched himself out over the child three times, and called unto the Lord, and said, O Lord my God, let, I pray thee, the soul of this child return again within him.
22 Ubangiji kuwa ya ji kukan Iliya, sai ran yaron ya dawo masa, ya kuma rayu.
And the Lord listened to the voice of Elijah: and the soul of the child returned into him, and he revived.
23 Iliya ya ɗauki yaron ya sauko da shi daga ɗakin sama zuwa cikin gida. Ya ba da shi ga mahaifiyarsa, ya ce, “Duba, ɗanki yana da rai!”
And Elijah took the child, and brought him down out of the upper chamber into the house, and gave him unto his mother; and Elijah said, See, thy son liveth.
24 Sai matar ta ce wa Iliya, “Yanzu na san cewa kai mutumin Allah ne, Ubangiji kuma yana magana ta wurinka.”
And the woman said to Elijah, Now by this do I know, that thou art a man of God, and the word of the Lord in thy mouth is truth.

< 1 Sarakuna 17 >