< 1 Sarakuna 15 >

1 A shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yerobowam ɗan Nebat, Abiyam ya zama sarkin Yahuda,
La dix-huitième année du roi Jéroboam, fils de Nabat, Abiam devint roi de Juda,
2 ya kuma yi mulki a Urushalima shekara uku. Sunan mahaifiyarsa Ma’aka ne,’yar Abisalom.
et il régna trois ans à Jérusalem. Sa mère se nommait Maacha, fille d’Abessalom.
3 Shi ma ya aikata dukan irin zunubai da tsohonsa ya yi. Zuciyarsa ba tă bi Ubangiji Allahnsa, kamar yadda zuciyar Dawuda kakansa ta yi ba.
Il marcha dans tous les péchés de son père qu’il avait commis avant lui, et son cœur n’était pas tout entier à Yahweh, comme l’avait été le cœur de David, son père.
4 Duk da haka, saboda Dawuda Ubangiji Allahnsa ya ba shi fitila a Urushalima ta wurin ta da wani da ya gāje shi, ta wurinsa kuma Urushalima ta yi ƙarfi.
Mais, à cause de David, Yahweh, son Dieu, lui donna une lampe à Jérusalem en établissant son fils après lui et en laissant subsister Jérusalem.
5 Gama Dawuda ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, bai kuma fasa kiyaye wani daga umarnan Ubangiji ba dukan kwanakinsa, sai dai a batun Uriya mutumin Hitti.
Car David avait fait ce qui est droit aux yeux de Yahweh, et il ne s’était pas détourné pendant toute sa vie de tous les commandements qu’il en avait reçus, excepté dans l’affaire d’Urie le Hittite.
6 Aka yi yaƙi tsakanin Rehobowam da Yerobowam a duk kwanakin Abiya.
Il y eut guerre entre Roboam et Jéroboam tant qu’il vécut.
7 Game da sauran ayyukan mulkin Abiyam kuwa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. Aka yi yaƙi tsakanin Abiyam da Yerobowam.
Le reste des actes d’Abiam, et tout ce qu’il a fait, cela n’est-il pas écrit dans le livre des Chroniques des rois de Juda. Il y eut guerre entre Abiam et Jéroboam.
8 Sai Abiyam ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Asa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
Abiam se coucha avec ses pères, et on l’enterrera dans la ville de David. Asa, son fils, régna à sa place.
9 A shekara ta ashirin ta Yerobowam sarkin Isra’ila, Asa ya zama sarkin Yahuda,
La vingtième année de Jéroboam, roi d’Israël, Asa devint roi de Juda,
10 ya yi mulki a Urushalima shekara arba’in da ɗaya. Sunan mahaifiya mahaifiyarsa, Ma’aka ne’yar Abisalom.
et il régna quarante et un ans à Jérusalem. Sa mère s’appelait Maacha, fille d’Abessalom.
11 Asa ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar yadda kakansa Dawuda ya yi.
Asa fit ce qui est droit aux yeux de Yahweh, comme David, son père.
12 Ya kori dukan maza karuwai na masujadai daga ƙasar, ya kuma yi waje da dukan gumakan da mahaifinsa ya yi.
Il fit disparaître du pays les prostitués et enleva toutes les idoles que ses pères avaient faites.
13 Ya tuɓe mahaifiya mahaifiyarsa Ma’aka daga matsayinta na mahaifiyar sarauniya, gama ta gina ƙazantaccen ginshiƙin Ashera. Asa ya yanke ginshiƙin, ya kuma ƙone shi a Kwarin Kidron.
Et même il ôta la dignité de reine-mère à Maacha, sa mère, parce qu’elle avait fait une idole abominable pour Astarté. Asa abattit son idole abominable et la brûla au torrent de Cédron.
14 Ko da yake bai cire masujadai da suke kan tuddai ba, zuciyar Asa ta kasance da aminci ɗungum ga Ubangiji dukan kwanakinsa.
Mais les hauts lieux ne disparurent point, quoique le cœur d’Asa fut parfaitement à Yahweh pendant toute sa vie.
15 Ya kawo azurfa da zinariya da kayayyakin da shi da mahaifinsa suka keɓe a haikalin Ubangiji.
Il mit dans la maison de Yahweh les choses consacrées par son père et les choses consacrées par lui-même, de l’argent, de l’or et des vases.
16 Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
Il y eut guerre entre Asa et Baasa, roi d’Israël, pendant toute leur vie.
17 Ba’asha sarkin Isra’ila ya haura, ya yi yaƙi da Yahuda, ya kuma gina Rama don yă hana wani daga fita ko shiga yankin Asa, sarkin Yahuda.
Baasa, roi d’Israël, monta contre Juda, et il bâtit Rama, pour empêcher les gens d’Asa, roi de Juda, de sortir et d’entrer.
18 Sai Asa ya ɗauki dukan azurfa da kuma zinariyar da suka rage a ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma nasa fadan, ya ba da su ga wani shugabansa, ya kuma aika da su zuwa ga Ben-Hadad ɗan Tabrimmon, ɗan Heziyon, sarkin Aram, wanda yake mulki a Damaskus.
Asa prit tout l’argent et l’or qui étaient restés dans les trésors de la maison de Yahweh et les trésors de la maison du roi, et les mit entre les mains de ses serviteurs; et le roi Asa envoya ces derniers vers Ben-Hadad, fils de Tabremon, fils de Hézion, roi de Syrie, qui habitait à Damas, pour dire:
19 Ya ce, “Bari yarjejjeniya ta kasance tsakanina da kai, kamar yadda ta kasance tsakanin mahaifina da mahaifinka. Duba, ina aika maka kyautai na azurfa da na zinariya. Yanzu fa sai ka janye yarjejjeniyarka da Ba’asha sarkin Isra’ila, don yă janye daga gare ni.”
« Qu’il y ait une alliance entre moi et toi, comme il y en avait une entre mon père et ton père. Je t’envoie un présent en argent et en or. Va, romps ton alliance avec Baasa, roi d’Israël, afin qu’il s’éloigne de moi. »
20 Ben-Hadad ya yarda da maganar Sarki Asa, ya kuma aika shugabannin sojojin mayaƙansa ya yi yaƙi da garuruwan Isra’ila. Ya kame Iyon, Dan, Abel-Bet-Ma’aka da dukan Kinneret, haɗe da Naftali.
Ben-Hadad écouta le roi Asa; il envoya les chefs de son armée contre les villes d’Israël, et il battit Ahion, Dan, Abel-Beth-Maacha, et tout Cenéroth avec tout le pays de Nephthali.
21 Da Ba’asha ya ji haka, sai ya daina ginin Rama, ya janye zuwa Tirza.
Baasa, l’ayant appris, cessa de bâtir Rama, et resta à Thersa.
22 Sai Sarki Asa ya ba da umarni ga dukan Yahuda, kuma babu wanda aka ware, kowa yă taimaka a kwashe duwatsu da katakan da Ba’asha yake amfani da su daga Rama. Da duwatsu da katakan ne Sarki Asa ya gina Geba a Benyamin da kuma Mizfa.
Le roi Asa fit convoquer tout Juda, sans exempter personne; et ils emportèrent les pierres et le bois avec lesquels Baasa construisait Rama, et le roi Asa bâtit avec eux Gabaa de Benjamin et Maspha.
23 Game da sauran ayyukan mulkin Asa, dukan nasarorinsa, dukan abin da ya yi, da kuma biranen da ya gina, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. A tsufansa, sai ƙafafunsa suka kamu da cuta.
Le reste de tous les actes d’Asa, tous ses exploits, et tout ce qu’il a fait, et les villes qu’il a bâties, cela n’est-il pas écrit dans le livre des Chroniques des rois de Juda? Toutefois, au temps de sa vieillesse, il eut les pieds malades.
24 Sai Asa ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a birnin kakansa Dawuda. Sai Yehoshafat ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Asa se coucha avec ses pères et il fut enterré avec ses pères dans la ville de David, son père; et Josaphat, son fils, régna à sa place.
25 Nadab ɗan Yerobowam ya zama sarkin Isra’ila a shekara ta biyu ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki a bisa Isra’ila shekara biyu.
Nadab, fils de Jéroboam, devint roi d’Israël la seconde année d’Asa, roi de Juda, et il régna deux ans sur Israël.
26 Ya yi mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin mahaifinsa da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.
Il fit ce qui est mal aux yeux de Yahweh, et il marcha dans la voie de son père et dans les péchés de son père qu’il avait fait commettre à Israël.
27 Ba’asha ɗan Ahiya na gidan Issakar ya yi maƙarƙashiya gāba da shi, ya buge shi a Gibbeton, a wani garin Filistiyawa, yayinda Nadab da dukan Isra’ila suke wa garin kwanto.
Baasa, fils d’Ahias, de la maison d’Issachar, conspira contre lui; et Baasa le frappa à Gebbéthon, qui appartenait aux Philistins, car Nadab et tout Israël faisaient le siège de Gebbéthon.
28 Ba’asha ya kashe Nadab a shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma gāje shi a matsayin sarki.
Baasa le mit à mort la troisième année d’Asa, roi de Juda, et il régna à sa place.
29 Nan da nan da ya fara mulki, sai ya kashe dukan iyalin Yerobowam. Bai bar wa Yerobowam wani da rai ba, amma ya hallaka su duka, bisa ga maganar Ubangiji da ya ba wa bawansa Ahiya, mutumin Shilo.
Lorsqu’il fut devenu roi, il frappa toute la maison de Jéroboam; il n’épargna de la maison de Jéroboam aucune âme vivante, sans l’exterminer, selon la parole que Yahweh avait dite par l’organe de son serviteur Ahias de Silo,
30 Wannan abu ya faru saboda zunuban da Yerobowam ya yi, ya kuma sa Isra’ila ya yi, kuma saboda ya tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya yi fushi.
à cause des péchés de Jéroboam qu’il avait commis, et qu’il avait fait commettre à Israël, irritant ainsi Yahweh, le Dieu d’Israël.
31 Game da sauran ayyukan mulkin Nadab da kuma dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Le reste des actes de Nadab, et tout ce qu’il a fait, cela n’est-il pas écrit dans le livre des Chroniques des rois d’Israël?
32 Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
Il y eut guerre entre Asa et Baasa, roi d’Israël, pendant toute leur vie.
33 A shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, Ba’asha ɗan Ahiya ya zama sarkin dukan Isra’ila a Tirza, ya kuma yi sarauta shekara ashirin da huɗu.
La troisième année d’Asa, roi de Juda, Baasa, fils d’Ahias, devint roi sur tout Israël à Thersa, et il régna vingt-quatre ans.
34 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin Yerobowam da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.
Il fit ce qui est mal aux yeux de Yahweh, et il marcha dans la voie de Jéroboam et dans les péchés que celui-ci avait fait commettre à Israël.

< 1 Sarakuna 15 >