< 1 Korintiyawa 7 >

1 To, game da zancen da kuka rubuto. Yana da kyau mutum yă zauna ba aure.
S strany pak toho, o čemž jste mi psali, dobréť by bylo člověku ženy se nedotýkati.
2 Amma da yake fasikanci ya yi yawa, ya kamata kowane mutum yă kasance da matarsa, kowace mace kuma da mijinta.
Ale z příčiny smilstva, jeden každý manželku svou měj, a jedna každá měj muže svého.
3 Ya kamata miji yă cika hakkinsa na aure ga matarsa. Haka kuma matar ta yi ga mijinta.
Muž k ženě povinnou přívětivost prokazuj, podobně též i žena k muži.
4 Jikin matar ba nata ne kaɗai ba, amma na mijinta ne ma. Haka ma jikin mijin, ba na shi ne kaɗai ba, amma na matarsa ne ma.
Žena svého vlastního těla v moci nemá, ale muž; též podobně i muž těla svého vlastního v moci nemá, ale žena.
5 Kada ku ƙi kwana da juna sai ko kun yarda a junanku kuma na ɗan lokaci, don ku himmantu ga addu’a. Sa’an nan ku sāke haɗuwa don kada Shaiɗan yă jarrabce ku saboda rashin ƙamewarku.
Neoklamávejte jeden druhého, leč by to bylo z společného svolení na čas, abyste se uprázdnili ku postu a k modlitbě; a zase spolu se sejděte, aby vás nepokoušel satan pro nezdrželivost vaši.
6 Wannan fa shawara ce nake ba ku, ba umarni ba.
Ale totoť pravím podlé dopuštění, ne podlé rozkazu.
7 Da ma a ce dukan maza kamar ni suke mana. Sai dai kowa da irin baiwar da Allah ya yi masa; wani yana da wannan baiwa, wani kuwa wancan.
Nebo chtěl bych, aby všickni lidé tak byli jako já, ale jeden každý svůj vlastní dar od Boha má, jeden tak a jiný jinak.
8 To, ga marasa aure da gwauraye kuwa ina cewa yana da kyau su zauna haka ba aure, yadda nake.
Pravím pak neženatým a vdovám: Dobré jest jim, zůstali-li by tak jako já.
9 Sai dai in ba za su iya ƙame kansu ba, to, su yi aure, don yă fi kyau a yi aure, da sha’awa ta sha kan mutum.
Pakliť se nemohou zdržeti, nechažť v stav manželský vstoupí; nebo lépe jest v stav manželský vstoupiti nežli páliti se.
10 Ga waɗanda suke da aure kuwa ina ba da wannan umarni (ba ni ba, amma Ubangiji) cewa kada mace ta rabu da mijinta.
Manželům pak přikazuji ne já, ale Pán, řka: Manželko od muže neodcházej.
11 In kuwa ta rabu da shi, sai ta kasance ba aure, ko kuma ta sāke shiryawa da mijinta. Kada miji kuma yă saki matarsa.
Pakliť by odešla, zůstaniž nevdaná, aneb smiř se s mužem. Tolikéž muži nepropouštěj ženy.
12 Ga sauran kuwa (ni ne fa na ce ba Ubangiji ba), in wani ɗan’uwa yana da mata wadda ba mai bi ba ce, kuma tana so ta zauna tare da shi, kada yă sake ta.
Jiným pak pravím já, a ne Pán: Má-li který bratr manželku nevěřící, a ta povoluje býti s ním, nepropouštějž jí.
13 In kuma mace tana da miji wanda ba mai bi ba ne, kuma yana so yă zauna tare da ita, kada tă kashe auren.
A má-li která žena muže nevěřícího, a on chce býti s ní, nepropouštěj ho.
14 Don miji marar ba da gaskiya an tsarkake shi ta wurin matarsa. Mace marar ba da gaskiya kuma an tsarkake ta ta wurin mijinta. In ba haka ba’ya’yanku ba za su zama da tsarki ba, amma kamar yadda yake, su masu tsarki ne.
Posvěcenť jest zajisté nevěřící muž pro ženu, a žena nevěřící posvěcena jest pro muže; sic jinak děti vaši nečistí by byli, ale nyní svatí jsou.
15 Amma in marar bi ɗin ya raba auren, a ƙyale shi. A irin wannan hali, babu tilas a kan wani, ko wata mai bi. Allah ya kira mu ga zaman lafiya ne.
Pakliť nevěřící odjíti chce, nechť jde. Neníť manem bratr neb sestra v takových věcech, ale ku pokoji povolal nás Bůh.
16 Ke mace, kin sani ne, ko ke ce za ki ceci mijinki? Kai miji, ka sani ne, ko kai ne za ka ceci matarka?
A kterak ty víš, ženo, získáš-li muže svého? Aneb co ty víš, muži, získáš-li ženu?
17 Duk da haka, sai kowa yă kasance a rayuwar da Ubangiji ya sa shi da kuma wanda Allah ya kira shi. Umarnin da na kafa a dukan ikkilisiyoyi ke nan.
Ale jakž jednomu každému odměřil Bůh, a jakž jednoho každého povolal Pán, tak choď. A takť ve všech církvech řídím.
18 In an riga an yi wa mutum kaciya sa’ad da aka kira shi, to, kada yă zama marar kaciya. In an kira mutum sa’ad da yake marar kaciya, to, kada a yi masa kaciya.
Obřezaný někdo povolán jest? Neuvodiž na sebe neobřízky. V neobřízce někdo povolán jest? Neobřezuj se.
19 Kaciya ba wani abu ba ne, rashin kaciya kuma ba wani abu ba ne. Kiyaye umarnin Allah shi ne muhimmin abu.
Obřízka nic není, též neobřízka nic není, ale zachovávání přikázaní Božích.
20 Ya kamata kowa yă kasance a matsayin da yake ciki sa’ad da Allah ya kira shi.
Jeden každý v tom povolání, v němž povolán jest, zůstávej.
21 Kai bawa ne sa’ad da aka kira ka? Kada wannan yă dame ka, sai dai in kana iya samun’yanci, sai ka yi amfani da wannan dama.
Služebníkem povolán jsi? Nedbej na to. Pakli bys mohl býti svobodný, raději toho užívej.
22 Gama wanda yake bawa sa’ad da Ubangiji ya kira shi,’yantacce ne na Ubangiji; haka ma, wanda yake’yantacce sa’ad da aka kira shi, bawa ne na Kiristi.
Nebo kdož jest v Pánu povolán služebníkem, osvobozený jest Páně. Též podobně kdož jest povolán svobodný, služebník jest Kristův.
23 Da tsada fa aka saye ku, kada ku zama bayin mutane.
Za mzdu koupeni jste, nebuďtež služebníci lidští.
24 ’Yan’uwa, a duk matsayin da mutum yake sa’ad da aka kira shi, sai yă kasance haka a sabuwar dangantakarsa da Allah.
Jeden každý jakž povolán jest, bratří, v tom zůstávej před Bohem.
25 To, game da budurwai. Ba ni da wani umarni daga Ubangiji, sai dai na yanke hukunci a matsayi wanda yake amintacce ta wurin jinƙan Ubangiji.
O pannách pak přikázaní Páně nemám, ale však radu dávám, jako ten, jemuž z milosrdenství svého Pán dal věrným býti.
26 Saboda ƙuncin rayuwar da ake ciki, ina gani ya fi kyau ku kasance yadda kuke.
Za toť pak mám, že jest to dobré pro nastávající potřebu, totiž že jest dobré člověku tak býti.
27 In kuna da aure, kada ku nemi kashe auren. In ba ku da aure, kada ku nemi yin aure.
Přivázáns k ženě? Nehledej rozvázání. Jsi prost od ženy? Nehledej ženy.
28 Amma idan ka riga ka yi aure, to, ba laifi, ba zunubi ba ne, kuma idan yarinya ta yi aure, ba tă yi laifi ba. Sai dai waɗanda suka yi aure za su fuskanci damuwoyi masu yawa a cikin rayuwa, ni kuwa ina so in fisshe su daga wannan.
Pakli bys se i oženil, nezhřešils, a vdala-li by se panna, nezhřešila; ale trápení těla míti budou takoví; jáť pak vám odpouštím.
29 ’Yan’uwa, abin da nake nufi shi ne, lokaci ya rage kaɗan. Daga yanzu, waɗanda suke da mata ya kamata su yi rayuwa kamar ba su da su;
Ale totoť pravím, bratří, poněvadž čas ostatní jest ukrácený, aby i ti, kteříž mají ženy, byli, jako by jich neměli,
30 waɗanda suke kuka kuma kamar ba kuka suke yi ba, waɗanda suke farin ciki kuwa kamar ba farin ciki suke yi ba. Waɗanda suka sayi abu su yi kamar ba nasu ba ne;
A kteříž plačí, jako by neplakali, a kteříž radují se, jako by se neradovali, a kteříž kupují, jako by nevládli,
31 masu amfani da kayan duniya kuwa, kada su duƙufa a cikinsu. Gama duniyan nan a yadda take mai shuɗewa ce.
A kteříž užívají tohoto světa, jako by neužívali. Neboť pomíjí způsob tohoto světa.
32 Zan so ku’yantu daga damuwa. Mutum marar aure ya damu ne da al’amuran Ubangiji, yadda zai gamshi Ubangiji.
Chciť pak, abyste vy bez pečování byli. Nebo kdo ženy nemá, pečuje o to, což jest Páně, kterak by se líbil Pánu.
33 Amma mutumin da yake da aure yakan damu ne da al’amuran wannan duniya, yadda zai gamshi matarsa
Ale kdo se oženil, pečuje o věci tohoto světa, jak by se líbil ženě.
34 hankalinsa a rabe yake. Mace marar aure ko kuwa budurwa ta damu ne da al’amuran Ubangiji. Nufinta shi ne ta ba da kanta ga Ubangiji cikin jiki da ruhu. Amma mace da take da aure ta damu ne da al’amuran wannan duniya, yadda za tă gamshi mijinta.
Rozdílnéť jsou žena a panna. Nevdaná pečuje o to, což jest Páně, aby byla svatá i tělem i duchem, ale vdaná pečuje o věci tohoto světa, kterak by se líbila muži.
35 Na faɗa haka don amfaninku ne, ba don in ƙuntata muku ba. Sai dai don ku yi rayuwa a hanyar da ta dace da nufin ku himmantu ga bautar Ubangiji ba da raba hankali ba.
Totoť pak k vašemu dobrému pravím, ne abych na vás osídlo uvrhl, ale abyste slušně a případně Pána se přídrželi, bez všeliké roztržitosti.
36 In mutum ya ga cewa ba ya nuna halin da ya kamata ga budurwar da ya yi alkawarin aure da ita, in kuma shekarunta suna wucewa, shi kuma ya ga ya kamata yă yi aure, to, sai yă yi. Ba zunubi ba ne. Ya kamata su yi aure.
Pakli kdo za neslušnou věc své panně pokládá pomíjení času k vdání, a tak by se státi mělo, učiň, jakžkoli chce, nezhřeší. Nechažť ji vdá.
37 Amma mutumin da ya riga ya yanke shawara a ransa, wanda kuma ba lalle ba ne amma yana iya shan kan nufinsa, kuma ya riga ya zartar a zuciyarsa ba zai auri budurwar ba, wannan mutum ma ya yi abin da ya dace.
Ale kdož se pevně ustavil v srdci, a není mu toho nouze, ale v moci má svou vlastní vůli, a to uložil v srdci svém, aby choval pannu svou, dobře činí.
38 Don haka, wanda ya auri budurwar ya yi daidai, amma wanda bai aure ta ba ya ma fi.
A tak ten, kdož vdává, dobře činí, ale kdo nevdává, lépe činí.
39 Mace tana haɗe da mijinta muddin yana da rai. Amma in mijinta ya mutu, tana da’yanci ta auri wanda take so. Amma fa, sai mai bin Ubangiji.
Žena přivázána jest zákonem dotud, dokudž její muž živ jest. Pakli by umřel muž její, svobodná jest; můž se vdáti, za kohož chce, toliko v Pánu.
40 A nawa ra’ayi, za tă fi jin daɗi in ta zauna haka, a ganina kuwa ina ba ku shawara ce daga Ruhun Allah da na ce haka.
Ale blahoslavenější jest, zůstala-li by tak, podlé mého soudu. Mámť pak za to, žeť i já mám Ducha Božího.

< 1 Korintiyawa 7 >