< 1 Tarihi 4 >

1 Zuriyoyin Yahuda su ne, Ferez, Hezron, Karmi, Hur da Shobal.
The sonnes of Iudah were Pharez, Hezron, and Carmi, and Hur, and Shobal.
2 Reyahiya ɗan Shobal shi ne mahaifin Yahat, Yahat shi ne mahaifin Ahumai da Lahad. Waɗannan su ne gidajen Zoratiyawa.
And Reaiah the sonne of Shobal begat Iahath, and Iahath begate Ahumai, and Lahad: these are the families of the Zoreathites.
3 Waɗannan su ne’ya’yan Etam. Yezireyel, Ishma da Idbash.’Yar’uwarsu ita ce Hazzelelfoni.
And these were of the father of Etam, Izreel, and Ishma and Idbash: and the name of their sister was Hazelelponi.
4 Fenuwel shi ne mahaifin Gedor, kuma Ezer shi ne mahaifin Husha. Waɗannan su ne zuriyar Hur, ɗan farin Efrata da mahaifin Betlehem.
And Penuel was the father of Gedor, and Ezer the father of Hushah: these are the sonnes of Hur the eldest sonne of Ephratah, the father of Beth-lehem.
5 Asshur mahaifin Tekowa yana da mata biyu, Hela da Na’ara.
But Asher the father of Tekoa had two wiues, Heleah, and Naarah.
6 Na’ara ta haifi Ahuzzam, Hefer, Temeni da Hawahashtari. Waɗannan su ne zuriyar Na’ara.
And Naarah bare him Ahuzam, and Hepher, and Temeni and Haashtari: these were the sonnes of Naarah.
7 ’Ya’yan Hela maza su ne, Zeret, Zohar, Etnan,
And the sonnes of Heleah were Zereth, Iezohar and Ethnan.
8 da Koz. Koz ne mahaifin Anub da Hazzobeba, shi ne kuma kakan iyalin da suka fito daga zuriyar Aharhel ɗan Harum.
Also Coz begate Anub, and Zobebah, and the families of Aharhel the sonne of Harum.
9 Yabez ya fi’yan’uwansa martaba. Mahaifiyarsa ta sa masa suna Yabez, tana cewa, “Na haife shi da azaba.”
But Iabez was more honourable then his brethren: and his mother called his name Iabez, saying, Because I bare him in sorowe.
10 Yabez ya yi kuka ga Allah na Isra’ila ya ce, “Ka yi mini albarka ka fadada yankina! Bari hannunka yă kasance tare da ni, yă kuma kiyaye ni daga abin da zai cuce ni, don kada in shiga wahala.” Sai Allah ya ji roƙonsa.
And Iabez called on the God of Israel, saying, If thou wilt blesse me in deede, and enlarge my coastes, and if thine hand be with me, and thou wilt cause me to be deliuered from euill, that I be not hurt. And God graunted the thing that he asked.
11 Kelub, ɗan’uwan Shuha, shi ne mahaifin Mehir, wanda shi ne mahaifin Eshton.
And Chelub the brother of Shuah begate Mehir, which was the father of Eshton.
12 Eshton shi ne mahaifin Bet-Rafa, Faseya da Tehinna wanda ya haifi Ir Nahash. Waɗannan su ne mutanen Reka.
And Eshton begate Beth-rapha, and Paseah, and Tehinnah the father of the citie of Nahash: these are the men of Rechah.
13 ’Ya’yan Kenaz maza su ne, Otniyel da Serahiya.’Ya’yan Otniyel maza su ne, Hatat da Meyonotai.
And the sonnes of Kenaz were Othniel and Zeraiah, and the sonne of Othniel, Hathath.
14 Meyonotai shi ne mahaifin Ofra. Serahiya shi ne mahaifin Yowab, mahaifin Ge-Harashim. An kira shi haka domin mutanensa masu sana’ar hannu ne.
And Meonothai begate Ophrah. And Seraiah begate Ioab the father of the valley of craftesmen: for they were craftesmen.
15 ’Ya’yan Kaleb ɗan Yefunne maza su ne, Iru, Ela da Na’am. Ɗan Ela shi ne, Kenaz.
And the sonnes of Caleb the sonne of Iephunneh were Iru, Elah, and Naam. And the sonne of Elah was Kenaz.
16 ’Ya’yan Yahallelel su ne, Zif, Zifa, Tiriya da Asarel.
And the sonnes of Iehaleel were Ziph, and Ziphah, Tiria, and Asareel.
17 ’Ya’yan Ezra maza su ne, Yeter, Mered, Efer da Yalon. Ɗaya daga cikin matan Mered ta haifi Miriyam, Shammai da Ishba wanda ya haifi Eshtemowa.
And the sonnes of Ezrah were Iether and Mered, and Epher, and Ialon, and he begate Miriam, and Shammai, and Ishbah the father of Eshtemoa.
18 (Matarsa mutuniyar Yahuda kuwa ta haifi Yared mahaifin Gedor, Heber mahaifin Soko, da kuma Yekutiyel mahaifin Zanowa.) Waɗannan su ne’ya’yan Bitiya’yar Fir’auna, wadda Mered ya aura.
Also his wife Iehudiiah bare Iered the father of Gedor, and Heber the father of Socho, and Iekuthiel the father of Zanoah: and these are the sonnes of Bithiah ye daughter of Pharaoh which Mered tooke.
19 ’Ya’yan matar Hodiya,’yar’uwar Naham su ne, suka haifi Keyila Bagarme, da Eshtemowa mutumin Ma’aka.
And the sonnes of the wife of Hodiah, the sister of Naham the father of Keilah were the Garmites, and Eshtemoa the Maachathite.
20 ’Ya’yan Shimon maza su ne, Amnon, Rinna, Ben-Hanan da Tilon. Zuriyar Ishi su ne, Zohet da Ben-Zohet.
And the sonnes of Shimon were Amnon and Rinnah, Ben-hanam and Tilon. And the sonnes of Ishi were Zoheth, and Benzoheth.
21 ’Ya’yan Shela ɗan Yahuda maza su ne, Er mahaifin Leka, La’ada mahaifin Maresha da kuma gidajen masu aikin lilin a Bet-Ashbeya,
The sonnes of Shelah, the sonne of Iudah were Er the father of Lecah, and Laadah the father of Mareshah, and the families of the householdes of them that wrought fine linnen in the house of Ashbea.
22 da Yokim, mutanen Kozeba, da Yowash da Saraf wanda ya yi mulkin Mowab da kuma Yashubi Lehem (Waɗannan rubutattun tarihi ne na tun dā.)
And Iokim and the men of Chozeba and Ioash, and Saraph, which had the dominion in Moab, and Iashubi Lehem. These also are auncient things.
23 Su ne maginan tukwane waɗanda suka zauna a Netayim da Gedera; sun zauna a can suka kuma yi wa sarki aiki.
These were potters, and dwelt among plants and hedges: there they dwelt with the king for his worke.
24 Zuriyar Simeyon su ne, Nemuwel, Yamin, Yarib, Zera da Shawulu;
The sonnes of Simeon were Nemuel, and Iamin, Iarib, Zerah, and Shaul,
25 Shawulu ya haifi Shallum, Shallum ya haifi Mibsam. Mibsam ya haifi Mishma.
Whose sonne was Shallum, and his sonne, Mibsam, and his sonne Mishma.
26 Zuriyar Mishma su ne, Hammuwel ɗansa, wanda ya haifi Zakkur, shi Zakkur kuma ya haifi Shimeyi.
And the sonnes of Mishma, Hamuel was his sonne, Zacchur his sonne, and Shimei his sonne.
27 Shimeyi yana da’ya’ya maza goma sha shida da’ya’ya mata shida, amma’yan’uwansa ba su da’ya’ya da yawa; saboda haka gidansu gaba ɗaya ba tă zama mai mutane da yawa kamar mutanen Yahuda ba.
And Shimei had sixteene sonnes, and sixe daughters, but his brethren had not many children, neither was all their familie like to the children of Iudah in multitude.
28 Sun zauna a Beyersheba, Molada, Hazar Shuwal,
And they dwelt at Beer-sheba, and at Moladah, and at Hazar Shual,
29 Bilha, Ezem, Tolad
And at Bilhah, and at Ezem, and at Tolad,
30 Betuwel, Horma, Ziklag,
And at Bethuel, and at Hormah, and at Ziklag,
31 Bet-Markabot, Hazar-Susim, Bet-Biri da Sha’arayim. Waɗannan su ne garuruwansu har lokacin mulkin Dawuda.
And at Beth-marcaboth, and at Hazar Susim, at Beth-birei, and at Shaaraim, these were their cities vnto the reigne of Dauid.
32 Ƙauyukan da suke kewayensu su ne Etam, Ayin, Rimmon, Token da Ashan, garuruwa biyar;
And their townes were Etam, and Ain, Rimmon, and Tochen, and Ashan, fiue cities.
33 da kuma dukan ƙauyuka kewaye da waɗannan garuruwa har zuwa Ba’al. Waɗannan ne wuraren zamansu. Suka kuma ajiye tarihin zuriya.
And all their townes that were rounde about these cities vnto Baal, These are their habitations and the declaration of their genealogie,
34 Zuriyar Simeyon ta ƙunshi Meshobab, da Yamlek, da Yosha ɗan Amaziya.
And Meshobab, and Iamlech, and Ioshah the sonne of Amashiah,
35 Akwai Yowel, da Yehu ɗan Yoshibiya. Yoshibiya ɗan Seraya ne. Serahiya kuma ɗan Asiyel ne.
And Ioel and Iehu the sonne of Ioshibiah, the sonne of Seraiah, the sonne of Asiel,
36 Akwai Eliyohenai da Ya’akoba, da Yeshohahiya, da Asahiya, da Adiyel, da Yesimiyel, da Benahiya.
And Elionai, and Iaakobah, and Ieshohaiah, and Asaiah, and Adiel, and Iesimiel, and Benaiah,
37 Akwai Ziza ɗan Shifi. Shifi ɗan Allon ne. Allon ɗan Yedahiya ne. Yedahiya ɗan Shimri ne. Shimri kuma ɗan Shemahiya ne.
And Ziza the sonne of Shiphei, the sonne of Allon, the sonne of Iedaiah, the sonne of Shimri, the sonne of Shemaiah.
38 Mutanen da aka jera sunayensu a bisa, shugabannin gidajensu ne. Iyalansu sun ƙaru sosai,
These were famous princes in their families, and increased greatly their fathers houses.
39 suka tafi bayan garin Gedor wajajen gabashin kwari suna neman makiyaya domin garkunansu.
And they went to the entring in of Gedor, euen vnto the East side of the valley, to seeke pasture for their sheepe.
40 Suka sami makiyaya mai ciyawa mai kyau, ƙasar kuma tana da fāɗi, da salama, kuma zaman lafiya. A dā waɗansu mutanen Ham sun zauna a can.
And they found fat pasture and good, and a wide land, both quiet and fruitfull: for they of Ham had dwelt there before.
41 Mutanen da aka jera sunayensu sun zo ne a zamanin Hezekiya sarkin Yahuda. Suka yaƙi mutanen Ham a wuraren zamansu, haka kuma suka yi da Meyunawa da suke can, suka hallaka su ƙaƙaf, yadda yake har yă zuwa yau. Sa’an nan suka zauna a wurin, gama akwai makiyaya domin garkunansu.
And these described by name, came in the dayes of Hezekiah king of Iudah, and smote their tents, and the inhabitants that were found there, and destroyed them vtterly vnto this day, and dwelt in their roume, because there was pasture there for their sheepe.
42 Mutum ɗari biyar na waɗannan mutane Simeyon, waɗanda Felatiya, Neyariya, Refahiya da Uzziyel,’ya’yan Ishi maza suka jagorance, sun mamaye ƙasar tudu ta Seyir.
And besides these, fiue hundreth men of the sonnes of Simeon went to mount Seir, and Pelatiah, and Neariah, and Rophaiah, and Vzziel the sonnes of Ishi were their captaines,
43 Suka karkashe raguwar Amalekawan da suka tsere, suka kuma zauna a can har yă zuwa yau.
And they smote the rest of Amalek that had escaped, and they dwelt there vnto this day.

< 1 Tarihi 4 >