< 1 Tarihi 24 >

1 Waɗannan su ne sassan’ya’yan Haruna maza.’Ya’yan Haruna maza su ne Nadab, Abihu, Eleyazar da Itamar.
Porro filiis Aaron hæ partitiones erant: Filii Aaron: Nadab, et Abiu, et Eleazar, et Ithamar.
2 Amma Nadab da Abihu sun mutu kafin mahaifinsu, ba su kuma haifi’ya’ya maza ba; saboda haka Eleyazar da Itamar suka yi hidimar firistoci.
Mortui sunt autem Nadab, et Abiu ante patrem suum absque liberis: sacerdotioque functus est Eleazar, et Ithamar.
3 Tare da taimakon Zadok zuriyar Eleyazar da Ahimelek wani zuriyar Itamar. Dawuda ya karkasa su zuwa ɓangarori don aikinsu bisa ga hidima.
Et divisit eos David, id est Sadoc de filiis Eleazari, et Ahimelech de filiis Ithamar, secundum vices suas et ministerium.
4 Akwai ɗumbun shugabanni a cikin zuriyar Eleyazar fiye da zuriyar Itamar, aka kuma karkasa su haka, kawuna goma sha shida daga zuriyar Eleyazar da kuma kawuna iyalai takwas daga zuriyar Itamar.
Inventique sunt multo plures filii Eleazar in principibus viris, quam filii Ithamar. Divisit autem eis, hoc est filiis Eleazar principes per familias sedecim: et filiis Ithamar per familias et domos suas octo.
5 Aka karkasa su babu sonkai ta wurin jifa ƙuri’a, gama akwai manyan ma’aikatan wuri mai tsarki da manyan ma’aikatan Allah a cikin zuriyar Eleyazar da Itamar.
Porro divisit utrasque inter se familias sortibus: erant enim principes sanctuarii, et principes Dei, tam de filiis Eleazar, quam de filiis Ithamar.
6 Shemahiya ɗan Netanel, wani Balawe ne marubuci, ya rubuta sunayensu a gaban sarki da kuma a gaban manyan ma’aikata. Zadok firist, Ahimelek ɗan Abiyatar da kuma kawunan iyalan firistoci da na Lawiyawa, iyali guda daga Eleyazar, guda kuma daga Itamar.
Descripsitque eos Semeias filius Nathanael scriba Levites, coram rege et principibus, et Sadoc sacerdote, et Ahimelech filio Abiathar, principibus quoque familiarum sacerdotalium et Leviticarum: unam domum, quæ ceteris præerat, Eleazar: et alteram domum, quæ sub se habebat ceteros, Ithamar.
7 Ƙuri’a ta farko ta faɗa a kan Yehoyarib, na biyu a kan Yedahiya,
Exivit autem sors prima Ioiarib, secunda Iedei,
8 na uku a kan Harim, na huɗu a kan Seyorim,
tertia Harim, quarta Seorim,
9 na biyar a kan Malkiya, na shida a kan Miyamin,
quinta Melchia, sexta Maiman,
10 na bakwai a kan Hakkoz, na takwas a kan Abiya,
septima Accos, octava Abia,
11 na tara a kan Yeshuwa, na goma a kan Shekaniya,
nona Iesua, decima Sechenia,
12 na goma sha ɗaya a kan Eliyashib, na goma sha biyu a kan Yakim,
undecima Eliasib, duodecima Iacim,
13 na goma sha uku a kan Huffa, na goma sha huɗu a kan Yeshebeyab,
tertiadecima Hoppha, decimaquarta Isbaab,
14 na goma sha biyar a kan Bilga, na goma sha shida a kan Immer,
decimaquinta Belga, decimasexta Emmer,
15 na goma sha shida a kan Hezir, na goma sha takwas a kan Haffizzez,
decimaseptima Hezir, decimaoctava Aphses,
16 na goma sha tara a kan Fetahahiya, na ashirin a kan Ezekiyel,
decimanona Pheteia, vigesima Hezechiel,
17 na ashirin da ɗaya wa Yakin, na ashirin da biyu a kan Gamul,
vigesimaprima Iachin, vigesimasecunda Gamul,
18 na ashirin da uku wa Delahiya da kuma na ashirin da huɗu a kan Ma’aziya.
vigesimatertia Dalaiau, vigesimaquarta Maaziau.
19 Ga tsarin aikinsu na hidima sa’ad da suka shiga haikalin Ubangiji, bisa ga ƙa’idar da kakansu Haruna ya kafa, yadda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya umarce shi.
Hæ vices eorum secundum ministeria sua, ut ingrediantur domum Domini, et iuxta ritum suum sub manu Aaron patris eorum: sicut præceperat Dominus Deus Israel.
20 Game da sauran zuriyar Lawi kuwa, Daga’ya’yan Amram maza. Shubayel; daga’ya’yan Shubayel maza. Yedehiya.
Porro filiorum Levi, qui reliqui fuerant, de filiis Amram erat Subael, et de filiis Subael, Iehedeia.
21 Game da Rehabiya kuwa, daga’ya’yansa maza. Isshiya shi ne na fari.
De filiis quoque Rohobiæ princeps Iesias.
22 Daga mutanen Izhar, Shelomot; daga’ya’yan Shelomot maza, Yahat.
Isaari vero filius Salemoth, filiusque Salemoth Iahath:
23 ’Ya’yan Hebron maza su ne, Yeriya na fari, Amariya na biyu, Yahaziyel na uku da Yekameyam na huɗu.
filiusque eius Ieriau primus, Amarias secundus, Iahaziel tertius, Iecmaan quartus.
24 Ɗan Uzziyel shi ne, Mika; daga’ya’yan Mika maza, Shamir.
Filius Oziel, Micha: filius Micha, Samir.
25 Ɗan’uwan Mika shi ne, Isshiya; daga’ya’yan Isshiya maza, Zakariya.
Frater Micha, Iesia: filiusque Iesiæ, Zacharias.
26 ’Ya’yan Merari su ne, Mali da Mushi. Ɗan Ya’aziya shi ne, Beno.
Filii Merari: Moholi et Musi. Filius Oziau: Benno.
27 ’Ya’yan Merari su ne, daga Ya’aziya, Beno, Shoham, Zakkur da Ibri.
Filius quoque Merari: Oziau et Soam et Zachur et Hebri.
28 Daga Mali, Eleyazar, wanda ba shi da’ya’ya maza.
Porro Moholi filius: Eleazar, qui non habebat liberos.
29 Daga Kish, ɗan Kish shi ne, Yerameyel.
Filius vero Cis, Ierameel.
30 Kuma’ya’yan Mushi maza su ne, Mali, Eder da Yerimot. Waɗannan su ne Lawiyawa bisa ga iyalansu.
Filii Musi: Moholi, Eder, et Ierimoth. isti filii Levi secundum domos familiarum suarum.
31 Suka kuma jifa ƙuri’a, kamar dai yadda’yan’uwansu zuriyar Haruna suka yi, a gaban Sarki Dawuda da gaban Zadok, Ahimelek, da kuma a gaban kawunan iyalan firistoci da na Lawiyawa. Aka yi da iyalan wa daidai da iyalan ƙane.
Miseruntque et ipsi sortes contra fratres suos filios Aaron coram David rege, et Sadoc, et Ahimelech, et principibus familiarum Sacerdotalium et Leviticarum, tam maiores, quam minores. omnes sors æqualiter dividebat.

< 1 Tarihi 24 >