< 1 Tarihi 24 >

1 Waɗannan su ne sassan’ya’yan Haruna maza.’Ya’yan Haruna maza su ne Nadab, Abihu, Eleyazar da Itamar.
Now these were the divisions of the sons of Aaron. The sons of Aaron: Nadab, and Abihu, and Eleazar, and Ithamar.
2 Amma Nadab da Abihu sun mutu kafin mahaifinsu, ba su kuma haifi’ya’ya maza ba; saboda haka Eleyazar da Itamar suka yi hidimar firistoci.
But Nadab and Abihu died before their father, and without children. And so Eleazar and Ithamar exercised the priestly office.
3 Tare da taimakon Zadok zuriyar Eleyazar da Ahimelek wani zuriyar Itamar. Dawuda ya karkasa su zuwa ɓangarori don aikinsu bisa ga hidima.
And David distributed them, that is, Zadok of the sons of Eleazar, and Ahimelech of the sons of Ithamar, according to their courses and ministry.
4 Akwai ɗumbun shugabanni a cikin zuriyar Eleyazar fiye da zuriyar Itamar, aka kuma karkasa su haka, kawuna goma sha shida daga zuriyar Eleyazar da kuma kawuna iyalai takwas daga zuriyar Itamar.
And there were found many more of the sons of Eleazar among the leading men, than of the sons of Ithamar. Therefore, he divided them so that there were, of the sons of Eleazar, sixteen leaders by their families, and of the sons of Ithamar eight by their families and houses.
5 Aka karkasa su babu sonkai ta wurin jifa ƙuri’a, gama akwai manyan ma’aikatan wuri mai tsarki da manyan ma’aikatan Allah a cikin zuriyar Eleyazar da Itamar.
Then he divided among them, in both families, by lot. For there were leaders of the sanctuary and leaders of God, as much from the sons of Eleazar as from the sons of Ithamar.
6 Shemahiya ɗan Netanel, wani Balawe ne marubuci, ya rubuta sunayensu a gaban sarki da kuma a gaban manyan ma’aikata. Zadok firist, Ahimelek ɗan Abiyatar da kuma kawunan iyalan firistoci da na Lawiyawa, iyali guda daga Eleyazar, guda kuma daga Itamar.
And the scribe Shemaiah, the son of Nethanel, a Levite, wrote these down before the king and the leaders, with Zadok, the priest, and Ahimelech, the son of Abiathar, and also the leaders of the priestly and Levitical families. And there was one house, which was preeminent over the others, that of Eleazar; and there was another house, which had the others under it, that of Ithamar.
7 Ƙuri’a ta farko ta faɗa a kan Yehoyarib, na biyu a kan Yedahiya,
Now the first lot went forth to Jehoiarib, the second to Jedaiah,
8 na uku a kan Harim, na huɗu a kan Seyorim,
the third to Harim, the fourth to Seorim,
9 na biyar a kan Malkiya, na shida a kan Miyamin,
the fifth to Malchijah, the sixth to Mijamin,
10 na bakwai a kan Hakkoz, na takwas a kan Abiya,
the seventh to Hakkoz, the eighth to Abijah,
11 na tara a kan Yeshuwa, na goma a kan Shekaniya,
the ninth to Jeshua, the tenth to Shecaniah,
12 na goma sha ɗaya a kan Eliyashib, na goma sha biyu a kan Yakim,
the eleventh to Eliashib, the twelfth to Jakim,
13 na goma sha uku a kan Huffa, na goma sha huɗu a kan Yeshebeyab,
the thirteenth to Huppah, the fourteenth to Jeshebeab,
14 na goma sha biyar a kan Bilga, na goma sha shida a kan Immer,
the fifteenth to Bilgah, the sixteenth to Immer,
15 na goma sha shida a kan Hezir, na goma sha takwas a kan Haffizzez,
the seventeenth to Hezir, the eighteenth to Happizzez,
16 na goma sha tara a kan Fetahahiya, na ashirin a kan Ezekiyel,
the nineteenth to Pethahiah, the twentieth to Jehezkel,
17 na ashirin da ɗaya wa Yakin, na ashirin da biyu a kan Gamul,
the twenty-first to Jachin, the twenty-second to Gamul,
18 na ashirin da uku wa Delahiya da kuma na ashirin da huɗu a kan Ma’aziya.
the twenty-third to Delaiah, the twenty-fourth to Maaziah.
19 Ga tsarin aikinsu na hidima sa’ad da suka shiga haikalin Ubangiji, bisa ga ƙa’idar da kakansu Haruna ya kafa, yadda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya umarce shi.
These were their courses according to their ministries, so that they would enter into the house of the Lord in accord with their practice, under the hand of Aaron, their father, just as the Lord, the God of Israel, had instructed.
20 Game da sauran zuriyar Lawi kuwa, Daga’ya’yan Amram maza. Shubayel; daga’ya’yan Shubayel maza. Yedehiya.
Now of the sons of Levi who were remaining, there were Shubael, from the sons of Amram, and Jehdeiah, from the sons of Shubael.
21 Game da Rehabiya kuwa, daga’ya’yansa maza. Isshiya shi ne na fari.
Also, there were Isshiah, the leader from the sons of Rehabiah,
22 Daga mutanen Izhar, Shelomot; daga’ya’yan Shelomot maza, Yahat.
and truly Shelomoth, the son of Izhar, and Jahath, the son of Shelomoth,
23 ’Ya’yan Hebron maza su ne, Yeriya na fari, Amariya na biyu, Yahaziyel na uku da Yekameyam na huɗu.
and his son, Jeriah the first, Amariah the second, Jahaziel the third, Jekameam the fourth.
24 Ɗan Uzziyel shi ne, Mika; daga’ya’yan Mika maza, Shamir.
The son of Uzziel was Micah. The son of Micah was Shamir.
25 Ɗan’uwan Mika shi ne, Isshiya; daga’ya’yan Isshiya maza, Zakariya.
The brother of Micah was Isshiah. And the son of Isshiah was Zechariah.
26 ’Ya’yan Merari su ne, Mali da Mushi. Ɗan Ya’aziya shi ne, Beno.
The sons of Merari were Mahli and Mushi. The son of Uzziah was Beno.
27 ’Ya’yan Merari su ne, daga Ya’aziya, Beno, Shoham, Zakkur da Ibri.
Also, the son of Merari: Uzziah, and Shoham, and Zaccur, and Hebri.
28 Daga Mali, Eleyazar, wanda ba shi da’ya’ya maza.
In addition, the son of Mahli was Eleazar, who had no children.
29 Daga Kish, ɗan Kish shi ne, Yerameyel.
Truly, the son of Kish was Jerahmeel.
30 Kuma’ya’yan Mushi maza su ne, Mali, Eder da Yerimot. Waɗannan su ne Lawiyawa bisa ga iyalansu.
The sons of Mushi were Mahli, Eder, and Jerimoth. These were the sons of Levi according to the houses of their families.
31 Suka kuma jifa ƙuri’a, kamar dai yadda’yan’uwansu zuriyar Haruna suka yi, a gaban Sarki Dawuda da gaban Zadok, Ahimelek, da kuma a gaban kawunan iyalan firistoci da na Lawiyawa. Aka yi da iyalan wa daidai da iyalan ƙane.
And they also cast lots concerning their brothers, the sons of Aaron, before David the king, and Zadok, and Ahimelech, and the leaders of the priestly and Levitical families, as much concerning the elder as the younger. The lot divided all things equitably.

< 1 Tarihi 24 >