< 1 Tarihi 18 >

1 Ana nan sai Dawuda ya ci Filistiyawa ya kuma rinjaye su, ya ƙwace Gat da ƙauyukan kewayenta daga mulkin Filistiyawa.
And it comes to pass after this, that David strikes the Philistines, and humbles them, and takes Gath and its small towns out of the hand of the Philistines;
2 Dawuda ya kuma ci Mowabawa, suka zama bayinsa suka kuma biya haraji.
and he strikes Moab, and the Moabites are servants to David, bringing a present.
3 Ban da haka, Dawuda ya yaƙi Hadadezer sarkin Zoba, har can Hamat, sa’ad da ya je don yă kafa mulkinsa a wajen Kogin Yuferites.
And David strikes Hadarezer king of Zobah, at Hamath, in his going to establish his power by the Euphrates River,
4 Dawuda ya kame keken yaƙinsa dubu ɗaya, da mahayan kekunan yaƙi dubu bakwai da sojojin kafa guda dubu ashirin. Ya yayyanke dukan agaran dawakansa, amma ya bar dawakai da suka isa jan kekunan yaƙi ɗari.
and David captures from him one thousand chariots, and seven thousand horsemen, and twenty thousand footmen, and David utterly destroys all the chariots, and leaves of them [only] one hundred chariots.
5 Da Arameyawan Damaskus suka zo su taimaki Hadadezer sarkin Zoba, sai Dawuda ya bugi dubu ashirin da biyunsu.
And Aram of Damascus comes to give help to Hadarezer king of Zobah, and David strikes twenty-two thousand men in Aram,
6 Ya sa ƙungiyoyin sojoji a masarautar Arameyawan Damaskus. Arameyawan kuwa suka zama bayinsa, suka kuma kawo haraji. Ubangiji ya ba Dawuda nasara a ko’ina da ya tafi.
and David puts [garrisons] in Aram of Damascus, and the Arameans are for servants to David, carrying a present, and YHWH gives salvation to David wherever he has gone.
7 Dawuda ya kwashe garkuwoyin zinariyan da shugabannin sojojin Hadadezer suke riƙe, ya kawo su Urushalima.
And David takes the shields of gold that have been on the servants of Hadarezer, and brings them to Jerusalem;
8 Daga Teba da Kun, garuruwan da suke ƙarƙashin Hadadezer, Dawuda ya kwashe tagulla da yawa sosai, wanda Solomon ya yi amfani don yă yi Tekun tagulla, ginshiƙai da kuma kayayyakin tagulla dabam-dabam.
and from Tibhath, and from Chun, cities of Hadarezer, David has taken very much bronze; with it Solomon has made the bronze sea, and the pillars, and the vessels of bronze.
9 Sa’ad da Towu sarkin Hamat ya ji cewa Dawuda ya ci mayaƙan Hadadezer sarkin Zoba gaba ɗaya,
And Tou king of Hamath hears that David has struck the whole force of Hadarezer king of Zobah,
10 sai ya aiki ɗansa Hadoram zuwa wurin Sarki Dawuda yă gaishe shi yă kuma yi masa barka da nasara a yaƙi a kan Hadadezer, wanda yake yaƙi da Towu. Hadoram ya kawo kowane irin kayayyakin zinariya da na azurfa da na tagulla.
and he sends his son Hadoram to King David, to ask of him of peace, and to bless him, because that he has fought against Hadarezer and strikes him (for Hadarezer had been a man of wars with Tou); and [with him were] all kinds of vessels, of gold, and silver, and bronze;
11 Sarki Dawuda ya miƙa waɗannan kayayyakin ga Ubangiji, kamar yadda ya yi da azurfa da kuma zinariyan da ya kwaso daga dukan waɗannan al’ummai. Edom da Mowab, Ammonawa da Filistiyawa, da kuma Amalek.
King David has also sanctified them to YHWH with the silver and the gold that he has taken from all the nations, from Edom, and from Moab, and from the sons of Ammon, and from the Philistines, and from Amalek.
12 Abishai ɗan Zeruhiya ya bugi mutanen Edom dubu goma sha takwas a Kwarin Gishiri.
And Abishai son of Zeruiah has struck Edom in the Valley of Salt—eighteen thousand,
13 Ya sa ƙungiyoyin sojoji a Edom, dukan mutanen Edom kuwa suka zama bayin Dawuda. Ubangiji ya ba Dawuda nasara a ko’ina da ya tafi.
and he puts garrisons in Edom, and all the Edomites are servants to David; and YHWH saves David wherever he has gone.
14 Dawuda ya yi mulki a bisa dukan Isra’ila, yana yin abin da yake daidai da kuma gaskiya saboda dukan mutanensa.
And David reigns over all Israel, and he is doing judgment and righteousness to all his people,
15 Yowab ɗan Zeruhiya shi ne shugaban mayaƙa; Yehoshafat ɗan Ahilud shi ne marubuci;
and Joab son of Zeruiah [is] over the host, and Jehoshaphat son of Ahilud [is] remembrancer,
16 Zadok ɗan Ahitub da Abimelek ɗan Abiyatar su ne firistoci; Shafsha shi ne magatakarda;
and Zadok son of Ahitub and Abimelech son of Abiathar [are] priests, and Shavsha [is] scribe,
17 Benahiya ɗan Yehohiyada shi ne shugaban Keretawa da Feletiyawa;’ya’yan Dawuda maza su ne manyan ma’aikata a gefen sarki.
and Benaiah son of Jehoiada [is] over the Cherethite and the Pelethite, and the chief sons of David [are] at the hand of the king.

< 1 Tarihi 18 >