< 1 Tarihi 16 >

1 Suka fa kawo akwatin alkawarin Allah, suka sa a cikin tentin da Dawuda ya kafa dominsa, suka kuma miƙa hadayun ƙonawa da hadayu na salama a gaban Allah.
Trazendo pois a arca de Deus, a pozeram no meio da tenda que David lhe tinha armado; e offereceram holocaustos e sacrificios pacificos perante Deus.
2 Bayan Dawuda ya gama miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama, sai ya albarkaci mutane a cikin sunan Ubangiji.
E, acabando David de offerecer os holocaustos e sacrificios pacificos, abençoou o povo em nome do Senhor.
3 Sa’an nan ya ba da dunƙulen burodi da wainar dabino da kuma kauɗar zabibi ga kowane mutumin Isra’ila namiji da ta mace.
E repartiu a todos em Israel, tanto a homens como a mulheres, a cada um um pão, e um bom pedaço de carne, e um frasco de vinho.
4 Ya sa Lawiyawa su yi hidima a gaban akwatin alkawarin Ubangiji, su ɗaukaka, su gode, su kuma yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila.
E poz perante a arca do Senhor alguns dos levitas por ministros; e isto para recordarem, e louvarem, e celebrarem ao Senhor Deus d'Israel.
5 Asaf shi ne babba, sai Zakariya na biye, sa’an nan Ya’aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Mattitiya, Eliyab, Benahiya, Obed-Edom da Yehiyel. Su ne za su kaɗa molaye, da garayu, Asaf kuwa zai buga ganguna,
Era Asaph o chefe, e Zacharias o segundo depois d'elle: Jeiel, e Semiramoth, e Jehiel, e Mattithias, e Eliab, e Benaias, e Obed-edom, e Jeiel, com alaudes e com harpas; e Asaph se fazia ouvir com cymbalos;
6 Benahiya da Yahaziyel firistoci za su busa ƙahoni kullum a gaban akwatin alkawarin Allah.
Tambem Benaias, e Jahaziel, os sacerdotes, continuamente com trombetas, perante a arca do concerto de Deus.
7 A wannan rana, da farko, Dawuda ya sa Asaf da’yan’uwansa su rera wannan zabura ta yabo ga Ubangiji.
Então n'aquelle mesmo dia entregou David em primeiro logar o Psalmo seguinte, para louvarem ao Senhor, pelo ministerio de Asaph e de seus irmãos:
8 Ku yi godiya ga Ubangiji, ku yi shelar sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
Louvae ao Senhor, invocae o seu nome, fazei conhecidos entre os povos os seus feitos.
9 Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan ayyukan banmamakinsa.
Cantae-lhe, psalmodiae-lhe, attentamente fallae de todas as suas maravilhas.
10 Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
Gloriae-vos no seu sancto nome; alegre-se o coração dos que buscam ao Senhor.
11 Ku dogara ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
Buscae ao Senhor, e a sua força; buscae a sua face continuamente.
12 Ku tuna ayyukan banmamakin da ya aikata, mu’ujizansa da kuma hukuntai da ya yanke,
Lembrae-vos das suas maravilhas que tem feito, de seus prodigios, e dos juizos da sua bocca.
13 Ya ku zuriyar Isra’ila bayinsa, Ya ku’ya’yan Yaƙub maza, zaɓaɓɓunsa.
Vós, semente d'Israel, seus servos, vós, filhos de Jacob, seus eleitos.
14 Shi ne Ubangiji Allahnmu; hukuntansa suna a cikin dukan duniya.
Elle é o Senhor nosso Deus; em toda a terra estão os seus juizos.
15 Yakan tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
Lembrae-vos perpetuamente do seu concerto e da palavra que prescreveu para mil gerações;
16 alkawarin da ya yi wa Ibrahim rantsuwar da ya yi ga Ishaku.
Do concerto que contratou com Abrahão, e do seu juramento a Isaac;
17 Ya tabbatar da shi ga Yaƙub kamar ƙa’ida, ga Isra’ila kamar madawwamin alkawari.
O qual tambem a Jacob ratificou por estatuto, e a Israel por concerto eterno,
18 “Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana kamar rabon da za ka gāda.”
Dizendo: A ti te darei a terra de Canaan, quinhão da vossa herança.
19 Sa’ad da suke kima, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
Sendo vós em pequeno numero, poucos homens, e estrangeiros n'ella.
20 suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga wannan mulki zuwa wancan.
E andaram de nação em nação, e d'um reino para outro povo.
21 Bai bar wani ya zalunce su ba; saboda su ya tsawata wa sarakuna.
A ninguem permittiu que os opprimisse, e por amor d'elles reprehendeu reis, dizendo:
22 “Kada ku taɓa shafaffuna; kada ku yi wa annabawana lahani.”
Não toqueis os meus ungidos, e aos meus prophetas não façaes mal.
23 Ku rera ga Ubangiji, ku duniya duka; ku yi shelar cetonsa kowace rana.
Cantae ao Senhor em toda a terra; annunciae de dia em dia a sua salvação.
24 Ku furta ɗaukakarsa a cikin al’ummai, ayyukansa masu al’ajabai a cikin mutane.
Contae entre as nações a sua gloria, entre todos os povos as suas maravilhas.
25 Gama Ubangiji mai girma ne ya kuma cancanci yabo; dole a ji tsoronsa fiye da dukan alloli.
Porque grande é o Senhor, e muito para louvar, e mais tremendo é do que todos os deuses.
26 Gama dukan allolin al’ummai gumaka ne, amma Ubangiji ya yi sammai.
Porque todos os deuses das nações são vaidades; porém o Senhor fez os céus.
27 Daraja da ɗaukaka suna a gabansa; ƙarfi da farin ciki suna a wurin zamansa.
Magestade e esplendor ha diante d'elle, força e alegria no seu logar.
28 Ku yabi Ubangiji, ku iyalan al’ummai, ku yabi ɗaukaka da ƙarfin Ubangiji,
Dae ao Senhor, ó familias das nações, dae ao Senhor gloria e força.
29 ku ba wa Ubangiji ɗaukakar da ta dace da sunansa. Ku kawo hadaya ku kuma zo gabansa; ku yi wa Ubangiji sujada cikin darajar tsarkinsa.
Dae ao Senhor a gloria de seu nome; trazei presentes, e vinde perante Elle: adorae ao Senhor na belleza da sua sanctidade.
30 Ku yi rawar jiki a gabansa, ya ku duniya duka! Duniya ta kahu sosai; ba za tă jijjigu ba.
Trema perante Elle, trema toda a terra; pois o mundo se affirmará, para que se não abale.
31 Bari sammai su yi farin ciki, bari duniya tă yi murna; bari su ce a cikin al’ummai, “Ubangiji yana mulki!”
Alegrem-se os céus, e regozije-se a terra; e diga-se entre as nações: O Senhor reina.
32 Bari teku da kome da yake cikinsa su yi ruri; bari gonaki da kome a cikinsu su yi farin ciki!
Brama o mar com a sua plenitude; exulte o campo com tudo o que ha n'elle.
33 Sa’an nan itatuwan jeji za su rera, za su rera don farin ciki a gaban Ubangiji, gama ya zo don yă hukunta duniya.
Então jubilarão as arvores dos bosques perante o Senhor; porquanto vem a julgar a terra.
34 Ku yi godiya ga Ubangiji, gama shi nagari ne; ƙaunarsa madawwamiya ce.
Louvae ao Senhor, porque é bom; pois a sua benignidade dura perpetuamente.
35 Ku yi kuka, ku ce, “Cece mu, ya Allah Mai Cetonmu; tara mu ka kuma cece mu daga al’ummai, don mu yi godiya ga sunanka mai tsarki, don mu ɗaukaka a cikin yabonka.”
E dizei: Salva-nos, ó Deus da nossa salvação, e ajunta-nos, e livra-nos das nações; para que louvemos o teu sancto nome, e nos gloriemos do teu louvor.
36 Yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Sai dukan mutane suka ce, “Amin.” Suka kuma “Yabi Ubangiji.”
Louvado seja o Senhor Deus de Israel, de seculo em seculo. E todo o povo disse: Amen! e louvou ao Senhor.
37 Dawuda ya bar Asaf da’yan’uwansa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji don su yi hidima a can kullum, bisa ga tsari na kowace rana.
Então deixou ali, diante da arca do concerto do Senhor, a Asaph e a seus irmãos, para ministrarem continuamente perante a arca, segundo se ordenara para cada dia.
38 Ya kuma bar Obed-Edom da’yan’uwansa sittin da takwas don su yi hidima tare. Obed-Edom ɗan Yedutun da Hosa kuma, su ne matsaran ƙofofi.
E mais a Obed-edom, com seus irmãos, sessenta e oito: a este Obed-edom, filho de Jeduthun, e a Hosa, ordenou por porteiros.
39 Dawuda ya bar Zadok firist da’yan’uwansa firistoci a gaban tabanakul na Ubangiji a tudun da yake a Gibeyon
E mais a Zadok, o sacerdote, e a seus irmãos, os sacerdotes, diante do tabernaculo do Senhor, no alto que está em Gibeon,
40 don su miƙa hadayun ƙonawa ga Ubangiji a kan bagaden hadaya ta ƙonawa kullum, da safe da kuma yamma, bisa ga kome da yake a rubutacce a cikin Dokar Ubangiji, da ya ba wa Isra’ila.
Para offerecerem ao Senhor os holocaustos sobre o altar dos holocaustos continuamente, pela manhã e á tarde: e isto segundo tudo o que está escripto na lei do Senhor que tinha prescripto a Israel.
41 Tare da su akwai Heman da Yedutun da sauran waɗannan zaɓaɓɓun da aka rubuta sunansu don yin godiya ga Ubangiji, “gama ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
E com elles a Heman, e a Jeduthun, e aos mais escolhidos, que foram apontados pelos seus nomes, para louvarem ao Senhor, porque a sua benignidade dura perpetuamente.
42 Heman da Yedutun su ne da hakkin busa ƙahoni da kaɗa kuge da sauran kayan bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe, waɗanda ake amfani da su lokacin da ake rera waƙoƙi masu tsarki.’Ya’yan Yedutun maza, su aka ba wa aikin tsaron ƙofa.
Com elles pois estavam Heman e Jeduthun, com trombetas e cymbalos, para os que se faziam ouvir, e com instrumentos de musica de Deus: porém os filhos de Jeduthun estavam á porta.
43 Sa’an nan dukan mutanen suka tashi, kowa ya koma gidansa, Dawuda ya koma gida yă sa wa iyalinsa albarka.
Então se foi todo o povo, cada um para a sua casa: e tornou David, para abençoar a sua casa.

< 1 Tarihi 16 >