< 1 Tarihi 16 >
1 Suka fa kawo akwatin alkawarin Allah, suka sa a cikin tentin da Dawuda ya kafa dominsa, suka kuma miƙa hadayun ƙonawa da hadayu na salama a gaban Allah.
Après qu’on eut fait entrer l’arche de Dieu, et qu’on l’eut déposée au milieu de la tente que David avait dressée pour elle, on offrit devant Dieu des holocaustes et des sacrifices pacifiques.
2 Bayan Dawuda ya gama miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama, sai ya albarkaci mutane a cikin sunan Ubangiji.
Quand David eut achevé d’offrir les holocaustes et les sacrifices pacifiques, il bénit le peuple au nom de Yahweh.
3 Sa’an nan ya ba da dunƙulen burodi da wainar dabino da kuma kauɗar zabibi ga kowane mutumin Isra’ila namiji da ta mace.
Puis il distribua à tous ceux d’Israël, hommes et femmes, à chacun un pain, une portion de viande et un gâteau de raisins.
4 Ya sa Lawiyawa su yi hidima a gaban akwatin alkawarin Ubangiji, su ɗaukaka, su gode, su kuma yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Il établit devant l’arche de Yahweh des lévites pour faire le service, en invoquant, en célébrant et en louant Yahweh, le Dieu d’Israël.
5 Asaf shi ne babba, sai Zakariya na biye, sa’an nan Ya’aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Mattitiya, Eliyab, Benahiya, Obed-Edom da Yehiyel. Su ne za su kaɗa molaye, da garayu, Asaf kuwa zai buga ganguna,
C’étaient: Asaph, le chef; Zacharie, le second; puis Jahiel, Sémiramoth, Jéhiel, Mathathias, Eliab, Banaïas, Obédédom et Jéhiel, avec des cithares et des harpes pour instruments; et Asaph faisait retentir les cymbales;
6 Benahiya da Yahaziyel firistoci za su busa ƙahoni kullum a gaban akwatin alkawarin Allah.
les prêtres Banaïas et Jaziel sonnaient continuellement de la trompette devant l’arche de l’alliance de Dieu.
7 A wannan rana, da farko, Dawuda ya sa Asaf da’yan’uwansa su rera wannan zabura ta yabo ga Ubangiji.
Ce fut en ce jour que David établit pour la première fois qu’on célébrerait Yahweh par l’organe d’Asaph et de ses frères:
8 Ku yi godiya ga Ubangiji, ku yi shelar sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
Louez Yahweh, invoquez son nom, faites connaître ses œuvres parmi les peuples.
9 Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan ayyukan banmamakinsa.
Chantez en son honneur, chantez des psaumes en son honneur, racontez toutes ses merveilles.
10 Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
Glorifiez-vous dans son saint nom; que se réjouisse le cœur de ceux qui cherchent Yahweh!
11 Ku dogara ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
Recherchez Yahweh et sa force; cherchez continuellement sa face.
12 Ku tuna ayyukan banmamakin da ya aikata, mu’ujizansa da kuma hukuntai da ya yanke,
Souvenez-vous des prodiges qu’il a faits, de ses miracles et des jugements de sa bouche,
13 Ya ku zuriyar Isra’ila bayinsa, Ya ku’ya’yan Yaƙub maza, zaɓaɓɓunsa.
race d’Israël, son serviteur, enfants de Jacob, ses élus.
14 Shi ne Ubangiji Allahnmu; hukuntansa suna a cikin dukan duniya.
Lui, Yahweh, est notre Dieu; ses jugements s’exercent sur toute la terre.
15 Yakan tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
Souvenez-vous à jamais de son alliance. — la parole qu’il a dite pour mille générations.
16 alkawarin da ya yi wa Ibrahim rantsuwar da ya yi ga Ishaku.
De l’alliance qu’il a conclue avec Abraham, et de son serment à Isaac,
17 Ya tabbatar da shi ga Yaƙub kamar ƙa’ida, ga Isra’ila kamar madawwamin alkawari.
qu’il a érigé pour Jacob en loi, pour Israël en alliance éternelle,
18 “Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana kamar rabon da za ka gāda.”
disant: « À toi je donnerai le pays de Chanaan, comme la part de votre héritage. »
19 Sa’ad da suke kima, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
Alors que vous étiez faciles à compter, en petit nombre et étrangers dans le pays,
20 suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga wannan mulki zuwa wancan.
qu’ils erraient d’une nation à l’autre, et d’un royaume vers un autre peuple,
21 Bai bar wani ya zalunce su ba; saboda su ya tsawata wa sarakuna.
Il ne permit à personne de les opprimer, et il châtia des rois à cause d’eux;
22 “Kada ku taɓa shafaffuna; kada ku yi wa annabawana lahani.”
« Ne touchez pas à mes oints, et ne faites pas de mal à mes prophètes! »
23 Ku rera ga Ubangiji, ku duniya duka; ku yi shelar cetonsa kowace rana.
Chantez à Yahweh, habitants de toute la terre; annoncez de jour en jour son salut.
24 Ku furta ɗaukakarsa a cikin al’ummai, ayyukansa masu al’ajabai a cikin mutane.
Racontez parmi les nations sa gloire, parmi tous les peuples ses merveilles.
25 Gama Ubangiji mai girma ne ya kuma cancanci yabo; dole a ji tsoronsa fiye da dukan alloli.
Car Yahweh est grand et très digne de louange, il est redoutable par-dessus tous les dieux;
26 Gama dukan allolin al’ummai gumaka ne, amma Ubangiji ya yi sammai.
car tous les dieux des peuples sont des idoles. Et Yahweh a fait les cieux;
27 Daraja da ɗaukaka suna a gabansa; ƙarfi da farin ciki suna a wurin zamansa.
la majesté et la splendeur sont devant sa face; la force et la joie sont dans sa demeure.
28 Ku yabi Ubangiji, ku iyalan al’ummai, ku yabi ɗaukaka da ƙarfin Ubangiji,
Rendez à Yahweh, familles des peuples, rendez à Yahweh gloire et puissance,
29 ku ba wa Ubangiji ɗaukakar da ta dace da sunansa. Ku kawo hadaya ku kuma zo gabansa; ku yi wa Ubangiji sujada cikin darajar tsarkinsa.
rendez à Yahweh gloire pour son nom. Apportez des offrandes et venez en sa présence; adorez Yahweh dans de saints ornements,
30 Ku yi rawar jiki a gabansa, ya ku duniya duka! Duniya ta kahu sosai; ba za tă jijjigu ba.
tremblez devant lui, habitants de toute la terre. Et le monde affermi ne chancellera point.
31 Bari sammai su yi farin ciki, bari duniya tă yi murna; bari su ce a cikin al’ummai, “Ubangiji yana mulki!”
Que les cieux se réjouissent et que la terre soit dans l’allégresse! Qu’on dise parmi les nations: « Yahweh est roi! »
32 Bari teku da kome da yake cikinsa su yi ruri; bari gonaki da kome a cikinsu su yi farin ciki!
Que la mer retentisse avec ce qu’elle contient! Que les champs tressaillent avec tout ce qu’ils renferment!
33 Sa’an nan itatuwan jeji za su rera, za su rera don farin ciki a gaban Ubangiji, gama ya zo don yă hukunta duniya.
Que les arbres de la forêt poussent des cris joyeux, devant Yahweh, car il vient pour juger la terre!
34 Ku yi godiya ga Ubangiji, gama shi nagari ne; ƙaunarsa madawwamiya ce.
Célébrez Yahweh, car il est bon, car sa miséricorde dure à jamais.
35 Ku yi kuka, ku ce, “Cece mu, ya Allah Mai Cetonmu; tara mu ka kuma cece mu daga al’ummai, don mu yi godiya ga sunanka mai tsarki, don mu ɗaukaka a cikin yabonka.”
Dites: « Sauve-nous, Dieu de notre salut; rassemble-nous et retire-nous du milieu des nations, afin que nous célébrions ton saint nom, et que nous mettions notre gloire en ta louange. »
36 Yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Sai dukan mutane suka ce, “Amin.” Suka kuma “Yabi Ubangiji.”
Béni soit Yahweh, le Dieu d’Israël, d’éternité en éternité! Et tout le peuple dit: « Amen! « et: « Louez Yahweh. »
37 Dawuda ya bar Asaf da’yan’uwansa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji don su yi hidima a can kullum, bisa ga tsari na kowace rana.
David laissa là, devant l’arche de l’alliance de Yahweh, Asaph et ses frères pour faire continuellement le service devant l’arche, selon la tâche de chaque jour;
38 Ya kuma bar Obed-Edom da’yan’uwansa sittin da takwas don su yi hidima tare. Obed-Edom ɗan Yedutun da Hosa kuma, su ne matsaran ƙofofi.
de même Obédédom avec ses frères, au nombre de soixante-huit, Obédédom, fils d’Idithun, et Hosa, comme portiers;
39 Dawuda ya bar Zadok firist da’yan’uwansa firistoci a gaban tabanakul na Ubangiji a tudun da yake a Gibeyon
de même, le prêtre Sadoc et les prêtres, ses frères, devant la Demeure de Yahweh sur le haut lieu qui était à Gabaon,
40 don su miƙa hadayun ƙonawa ga Ubangiji a kan bagaden hadaya ta ƙonawa kullum, da safe da kuma yamma, bisa ga kome da yake a rubutacce a cikin Dokar Ubangiji, da ya ba wa Isra’ila.
pour qu’ils offrissent des holocaustes à Yahweh continuellement, matin et soir, sur l’autel des holocaustes, et pour qu’ils accomplissent tout ce qui est écrit dans la loi de Yahweh qu’il a imposée à Israël.
41 Tare da su akwai Heman da Yedutun da sauran waɗannan zaɓaɓɓun da aka rubuta sunansu don yin godiya ga Ubangiji, “gama ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Auprès d’eux étaient Héman et Idithun, et le reste de ceux qui avaient été choisis et désignés par leurs noms, pour « louer Yahweh, car sa miséricorde dure à jamais! »
42 Heman da Yedutun su ne da hakkin busa ƙahoni da kaɗa kuge da sauran kayan bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe, waɗanda ake amfani da su lokacin da ake rera waƙoƙi masu tsarki.’Ya’yan Yedutun maza, su aka ba wa aikin tsaron ƙofa.
Avec eux, savoir, avec Héman et Idithun, étaient des trompettes et des cymbales pour ceux qui devaient les faire retentir, et des instruments pour les cantiques de Dieu. Les fils d’Idithun étaient pour la porte.
43 Sa’an nan dukan mutanen suka tashi, kowa ya koma gidansa, Dawuda ya koma gida yă sa wa iyalinsa albarka.
Tout le peuple s’en alla chacun dans sa maison; et David s’en retourna pour bénir sa maison.