< 1 Tarihi 16 >

1 Suka fa kawo akwatin alkawarin Allah, suka sa a cikin tentin da Dawuda ya kafa dominsa, suka kuma miƙa hadayun ƙonawa da hadayu na salama a gaban Allah.
So they brought in the Arke of God, and set it in the middes of the Tabernacle that Dauid had pitched for it, and they offred burnt offrings and peace offrings before God.
2 Bayan Dawuda ya gama miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama, sai ya albarkaci mutane a cikin sunan Ubangiji.
And when Dauid had made an ende of offering the burnt offering and the peace offerings, hee blessed the people in the Name of the Lord.
3 Sa’an nan ya ba da dunƙulen burodi da wainar dabino da kuma kauɗar zabibi ga kowane mutumin Isra’ila namiji da ta mace.
And he dealt to euery one of Israel both man and woman, to euery one a cake of breade, and a piece of flesh, and a bottel of wine.
4 Ya sa Lawiyawa su yi hidima a gaban akwatin alkawarin Ubangiji, su ɗaukaka, su gode, su kuma yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila.
And he appointed certaine of the Leuites to minister before the Arke of the Lord, and to rehearse and to thanke and prayse the Lord God of Israel:
5 Asaf shi ne babba, sai Zakariya na biye, sa’an nan Ya’aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Mattitiya, Eliyab, Benahiya, Obed-Edom da Yehiyel. Su ne za su kaɗa molaye, da garayu, Asaf kuwa zai buga ganguna,
Asaph the chiefe, and next to him Zechariah, Ieiel, and Shemiramoth, and Iehiel, and Mattithiah, and Eliab, and Benaiah, and Obed Edom, euen Ieiel with instruments, violes and harpes, and Asaph to make a sound with cymbales,
6 Benahiya da Yahaziyel firistoci za su busa ƙahoni kullum a gaban akwatin alkawarin Allah.
And Benaiah and Iahaziel Priestes, with trumpets continually before the Arke of the couenant of God.
7 A wannan rana, da farko, Dawuda ya sa Asaf da’yan’uwansa su rera wannan zabura ta yabo ga Ubangiji.
Then at that time Dauid did appoint at the beginning to giue thankes to the Lord by the hand of Asaph and his brethren.
8 Ku yi godiya ga Ubangiji, ku yi shelar sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
Praise the Lord and call vpon his Name: declare his workes among the people.
9 Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan ayyukan banmamakinsa.
Sing vnto him, sing praise vnto him, and talke of all his wonderfull workes.
10 Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
Reioyce in his holy Name: let the hearts of them that seeke the Lord reioyce.
11 Ku dogara ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
Seeke the Lord and his strength: seeke his face continually.
12 Ku tuna ayyukan banmamakin da ya aikata, mu’ujizansa da kuma hukuntai da ya yanke,
Remember his marueilous workes that he hath done, his wonders, and the iudgements of his mouth,
13 Ya ku zuriyar Isra’ila bayinsa, Ya ku’ya’yan Yaƙub maza, zaɓaɓɓunsa.
O seede of Israel his seruant, O the children of Iaakob his chosen.
14 Shi ne Ubangiji Allahnmu; hukuntansa suna a cikin dukan duniya.
He is the Lord our God: his iudgements are throughout all the earth.
15 Yakan tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
Remember his couenant for euer, and the worde, which hee commanded to a thousand generations:
16 alkawarin da ya yi wa Ibrahim rantsuwar da ya yi ga Ishaku.
Which he made with Abraham, and his othe to Izhak:
17 Ya tabbatar da shi ga Yaƙub kamar ƙa’ida, ga Isra’ila kamar madawwamin alkawari.
And hath confirmed it to Iaakob for a Law, and to Israel for an euerlasting couenant,
18 “Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana kamar rabon da za ka gāda.”
Saying, To thee will I giue the land of Canaan, the lot of your inheritance.
19 Sa’ad da suke kima, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
When ye were fewe in number, yea, a very fewe, and strangers therein,
20 suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga wannan mulki zuwa wancan.
And walked about from nation to nation, and from one kingdome to another people,
21 Bai bar wani ya zalunce su ba; saboda su ya tsawata wa sarakuna.
He suffered no man to do them wrong, but rebuked Kings for their sakes, saying,
22 “Kada ku taɓa shafaffuna; kada ku yi wa annabawana lahani.”
Touch not mine anoynted, and doe my Prophets no harme.
23 Ku rera ga Ubangiji, ku duniya duka; ku yi shelar cetonsa kowace rana.
Sing vnto the Lord all the earth: declare his saluation from day to day.
24 Ku furta ɗaukakarsa a cikin al’ummai, ayyukansa masu al’ajabai a cikin mutane.
Declare his glory among the nations, and his wonderful workes among all people.
25 Gama Ubangiji mai girma ne ya kuma cancanci yabo; dole a ji tsoronsa fiye da dukan alloli.
For the Lord is great and much to be praised, and hee is to bee feared aboue all gods.
26 Gama dukan allolin al’ummai gumaka ne, amma Ubangiji ya yi sammai.
For all the gods of the people are idoles, but the Lord made the heauens.
27 Daraja da ɗaukaka suna a gabansa; ƙarfi da farin ciki suna a wurin zamansa.
Prayse and glory are before him: power and beautie are in his place.
28 Ku yabi Ubangiji, ku iyalan al’ummai, ku yabi ɗaukaka da ƙarfin Ubangiji,
Giue vnto the Lord, ye families of the people: giue vnto the Lord glory and power.
29 ku ba wa Ubangiji ɗaukakar da ta dace da sunansa. Ku kawo hadaya ku kuma zo gabansa; ku yi wa Ubangiji sujada cikin darajar tsarkinsa.
Giue vnto the Lord ye glory of his Name: bring an offring and come before him, and worship the Lord in the glorious Sanctuarie.
30 Ku yi rawar jiki a gabansa, ya ku duniya duka! Duniya ta kahu sosai; ba za tă jijjigu ba.
Tremble ye before him, al the earth: surely the world shalbe stable and not moue.
31 Bari sammai su yi farin ciki, bari duniya tă yi murna; bari su ce a cikin al’ummai, “Ubangiji yana mulki!”
Let the heauens reioyce, and let the earth be glad, and let them say among the nations, The Lord reigneth.
32 Bari teku da kome da yake cikinsa su yi ruri; bari gonaki da kome a cikinsu su yi farin ciki!
Let the sea roare, and all that therein is: Let the field be ioyfull and all that is in it.
33 Sa’an nan itatuwan jeji za su rera, za su rera don farin ciki a gaban Ubangiji, gama ya zo don yă hukunta duniya.
Let the trees of the wood then reioyce at the presence of the Lord: for he commeth to iudge the earth.
34 Ku yi godiya ga Ubangiji, gama shi nagari ne; ƙaunarsa madawwamiya ce.
Prayse the Lord, for hee is good, for his mercie endureth for euer.
35 Ku yi kuka, ku ce, “Cece mu, ya Allah Mai Cetonmu; tara mu ka kuma cece mu daga al’ummai, don mu yi godiya ga sunanka mai tsarki, don mu ɗaukaka a cikin yabonka.”
And say ye, Saue vs, O God, our saluation, and gather vs, and deliuer vs from the heathen, that we may prayse thine holy Name, and glorie in thy praise.
36 Yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Sai dukan mutane suka ce, “Amin.” Suka kuma “Yabi Ubangiji.”
Blessed be the Lord God of Israel for euer and euer: and let all people say, So be it, and praise the Lord.
37 Dawuda ya bar Asaf da’yan’uwansa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji don su yi hidima a can kullum, bisa ga tsari na kowace rana.
Then he left there before the Arke of the Lordes couenant Asaph and his brethren to minister continually before the Arke, that which was to be done euery day:
38 Ya kuma bar Obed-Edom da’yan’uwansa sittin da takwas don su yi hidima tare. Obed-Edom ɗan Yedutun da Hosa kuma, su ne matsaran ƙofofi.
And Obed Edom and his brethren, three score and eight: and Obed Edom the sonne of Ieduthun, and Hosah were porters.
39 Dawuda ya bar Zadok firist da’yan’uwansa firistoci a gaban tabanakul na Ubangiji a tudun da yake a Gibeyon
And Zadok the Priest and his brethren the Priestes were before the Tabernacle of ye Lord, in the hie place that was at Gibeon,
40 don su miƙa hadayun ƙonawa ga Ubangiji a kan bagaden hadaya ta ƙonawa kullum, da safe da kuma yamma, bisa ga kome da yake a rubutacce a cikin Dokar Ubangiji, da ya ba wa Isra’ila.
To offer burnt offrings vnto the Lord, vpon the burnt offring altar continually, in the morning and in the euening, euen according vnto all that is written in the law of the Lord, which hee commanded Israel.
41 Tare da su akwai Heman da Yedutun da sauran waɗannan zaɓaɓɓun da aka rubuta sunansu don yin godiya ga Ubangiji, “gama ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
And with them were Heman, and Ieduthun, and the rest that were chosen (which were appointed by names) to praise the Lord, because his mercie endureth for euer.
42 Heman da Yedutun su ne da hakkin busa ƙahoni da kaɗa kuge da sauran kayan bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe, waɗanda ake amfani da su lokacin da ake rera waƙoƙi masu tsarki.’Ya’yan Yedutun maza, su aka ba wa aikin tsaron ƙofa.
Euen with them were Heman and Ioduthun, to make a sound with the cornets and with the cymbales, with excellent instruments of musicke: and the sonnes of Ieduthun were at the gate.
43 Sa’an nan dukan mutanen suka tashi, kowa ya koma gidansa, Dawuda ya koma gida yă sa wa iyalinsa albarka.
And all the people departed, euerie man to his house: and Dauid returned to blesse his house.

< 1 Tarihi 16 >