< 1 Tarihi 12 >
1 Waɗannan su ne mutanen da suka zo wurin Dawuda a Ziklag, yayinda aka kore shi daga gaban Shawulu ɗan Kish (suna cikin jarumawan da suka taimake shi a yaƙi;
Voici ceux qui vinrent auprès de David, à Ciklag, lorsqu’il se cachait encore pour échapper à Saül, fils de Kich. Ils faisaient partie des vaillants guerriers, ses compagnons de lutte,
2 suna da baka suna kuma iya harba kibiya, ko majajjawa da hannun dama ko na hagu; su’yan’uwan Shawulu ne daga kabilar Benyamin):
maniaient l’arc, lançaient des pierres de la main droite et de la gauche, et des flèches avec leurs arcs. Parmi les parents de Saül, issus de Benjamin, il y avait:
3 Ahiyezer babbansu da Yowash’ya’yan Shema’a maza daga Gibeya; Yeziyel da Felet’ya’yan Azmawet; Beraka, Yehu daga Anatot,
le chef Ahiézer et Joas, fils de Hachemaa, de Ghibea; Yeziël et Pélet, fils de Azmavet; Berakha, Yêhou, d’Anatot;
4 da Ishmahiya daga Gibeyon, wani jarumi a cikin Talatin nan, wanda shi ne shugaban Talatin; Irmiya, Yahaziyel, Yohanan, Yozabad daga Gedera,
Yichmaïa, de Gabaon, vaillant parmi les Trente, et chef des Trente; Jérémie, Yahaziël, Johanan, Yozabad, de Ghedêra;
5 Eluzai, Yerimot, Beyaliya, Shemariya da Shefatiya daga Haruf;
Elouzaï, Yerimot, Bealia, Chemariahou, Chefatiahou, de Harouf;
6 Elkana, Isshiya, Azarel, Yoyezer da Yashobeyam daga Kora;
Elkana, Yichiahou, Azarêl, Yoézer, Yachobam, les Korahites;
7 da Yoyela da Zebadiya’ya’yan Yeroham maza daga Gedor.
Yoêla, Zebadia, fils de Yeroham, de Ghedor.
8 Sai waɗansu mutanen Gad suka koma suna goyon bayan Dawuda suka kuma haɗa kai da shi a kagararsa a hamada. Su ƙwararrun mayaƙa ne, a shirye don yaƙi, kuma suna iya riƙe garkuwa da māshi. Fuskokinsu kamar fuskoki zakoki, kuma suna da sauri kamar bareyi a kan duwatsu.
Des Gadites se détachèrent pour passer à David, dans la forteresse du désert, vaillants héros, hommes de guerre, maniant le bouclier et la lance, ayant une apparence de lions et semblables à des chamois sur les montagnes pour la rapidité.
9 Ezer shi ne babba, Obadiya shi ne mai binsa a shugabanci, Eliyab na uku,
Le chef était Ezer, le second Obadia, le troisième Elïab,
10 Mismanna na huɗu, Irmiya na biyar,
le quatrième Michmanna, le cinquième Jérémie,
11 Attai na shida, Eliyel na bakwai,
le sixième Attaï, le septième Eliël,
12 Yohanan na takwas, Elzabad na tara,
le huitième Johanan, le neuvième Elzabad,
13 Irmiya na goma da kuma Makbannai na goma sha ɗaya.
le dixième Yirmeyahou, et le onzième Makhbannaï.
14 Waɗannan mutanen Gad shugabannin mayaƙa ne; ƙarami a cikinsu zai iya ƙara da mutum ɗari, kuma babba a cikin zai iya ƙara da dubu.
Tels étaient les Gadites, chefs d’armée: le plus petit en valait cent, le plus grand, mille.
15 Su ne suka haye Urdun a wata na farko sa’ad da kogin ya yi ambaliya, suka kuma kori duk mai rai a kwarin, na wajen gabas da na wajen yamma.
Ce sont eux qui passèrent le Jourdain dans le premier mois, quand il coule à pleins bords, et qui mirent en fuite tous les habitants de la vallée à l’Ouest et à l’Est.
16 Sauran mutanen Benyamin da waɗansu mutanen Yahuda su ma suka zo wurin Dawuda a kagararsa.
Des Benjaminites et des Judéens rejoignirent aussi David dans la forteresse.
17 Sai Dawuda ya fita don yă tarye su, ya kuma ce musu, “In kun zo wurina da salama, don ku taimake ni, to, ina a shirye in bar ku ku haɗa kai tare da ni. Amma in kun zo don ku bashe ni ga abokan gābana sa’ad da hannuwana ba su da laifi a rikici, bari Allah na kakanninmu yă duba yă kuma shari’anta ku.”
David sortit à leur rencontre et leur adressa ces paroles: "Si c’est avec des intentions pacifiques que vous êtes venus à moi, pour m’aider, je serai de cœur avec vous; si c’est pour me livrer traîtreusement à mes ennemis, sans que j’aie commis de faute, que le Dieu de nos ancêtres voie et juge!"
18 Sai Ruhu ya sauko a kan Amasai, shugaban Talatin nan, sai ya ce, “Mu naka ne, ya Dawuda! Muna tare da kai, ya ɗan Yesse! Nasara, nasara gare ka, nasara kuma ga waɗanda suke taimakonka. Gama Allahnka zai taimake ka.” Saboda haka Dawuda ya karɓe su ya kuma mai da su shugabannin ƙungiyoyin maharansa.
Alors une inspiration s’empara d’Amassaï, chef des Trente: "A toi, David, dit-il, et avec toi, fils de Jessé, paix; oui, paix à toi, et paix à tes auxiliaires, car ton Dieu t’assiste!" David alors les accueillit et les plaça à la tête des troupes.
19 Waɗansu mutanen Manasse suka haɗa kai da Dawuda sa’ad da ya tafi tare da Filistiyawa don yă yaƙi Shawulu (Shi da mutanensa ba su taimaki Filistiyawa ba domin bayan shawarwari, shugabanninsu suka salame shi. Sun ce, “Za mu biya da kawunanmu in ya koma ga maigidansa Shawulu.”)
Des gens de Manassé se rallièrent aussi à David, lorsqu’il vint avec les Philistins combattre Saül; mais ils n’aidèrent pas les Philistins, car les chefs de ceux-ci, après s’être concertés, l’avaient renvoyé, en disant: "C’Est au prix de nos têtes qu’il se rallierait à son maître Saül."
20 Da Dawuda ya tafi Ziklag, waɗannan mutanen Manasse ne suka haɗa kai da shi. Adna, Yozabad, Yediyayel, Mika’ilu, Yozabad, Elihu da Zilletai, shugabannin ƙungiyoyi na dubu a cikin Manasse.
Lorsqu’il alla à Ciklag, se joignirent à son parti, d’entre les gens de Manassé, Adna, Yozabad, Yedïaêl, Mikhaël, Yozabad, Elihou, et Cilletaï, chefs de mille en Manassé.
21 Suka taimaki Dawuda a kan ƙungiyoyin hari, gama dukansu jarumawa ne sosai, kuma su shugabanni ne a cikin mayaƙansa.
Ils furent un grand appui pour David à la tête des troupes, car ils étaient tous de vaillants guerriers, et ils devinrent des chefs d’armée.
22 Kowace rana mutane suka riƙa zuwa don su taimaki Dawuda, sai da ya kasance da runduna mai girma, kamar mayaƙan Allah.
Journellement, en effet, on venait à David pour l’assister, au point qu’il eut un camp grand comme celui de Dieu.
23 Ga yawan mutanen shiryayyu don yaƙi waɗanda suka zo wurin Dawuda a Hebron don su mai da mulkin Shawulu gare shi, yadda Ubangiji ya faɗa.
Et voici le décompte des chefs des hommes, équipés pour faire campagne, qui vinrent rejoindre David à Hébron, pour lui transférer la royauté de Saül, selon la parole de l’Eternel.
24 Mutanen Yahuda, masu riƙe garkuwa da māshi, su 6,800 shiryayyu don yaƙi;
Des Judéens, portant le bouclier et la lance: six mille huit cents hommes équipés pour l’armée.
25 mutanen Simeyon, jarumawa shiryayyu don yaƙi, su 7,100;
Des Siméonites, vaillants hommes d’armes: sept mille cent.
26 mutanen Lawi, su 4,600,
Des Lévites: quatre mille six cents.
27 haɗe da Yehohiyada, shugaban iyalin Haruna tare da mutane 3,700,
Joïada était le chef des Aaronides; il avait avec lui trois mille sept cents hommes.
28 da Zadok, matashi jarumi sosai, tare da shugabanni su 22 daga iyalinsa;
Çadok, quoique encore jeune, était un vaillant soldat. La maison de son père comptait vingt-deux capitaines.
29 mutanen Benyamin,’yan’uwan Shawulu, su 3,000, yawanci waɗanda suke biyayya ga gidan Shawulu sai lokacin;
Des Benjaminites, frères de Saül: trois mille. Jusque-là, la plupart avaient gardé leur foi à la maison de Saül.
30 mutanen Efraim, jarumawa, sanannu cikin gidajensu, su 20 800;
Des Ephraïmites: vingt mille huit cents, vaillants guerriers, possédant une grande renommée, répartis selon leurs familles.
31 mutanen rabin kabilar Manasse, sanannu da sunaye suka zo suka mai da Dawuda sarki, su 18,000;
De la demi-tribu de Manassé: dix-huit mille, désignés nominativement pour aller conférer la royauté à David.
32 mutanen Issakar, masu fahimtar lokuta suka kuma san abin da ya kamata Isra’ila ya yi, manya 200, tare da danginsu a ƙarƙashin shugabancinsu;
Des gens d’Issachar, experts en la connaissance des temps pour décider la conduite à tenir par Israël, il vint deux cents chefs, auxquels obéissaient tous leurs frères.
33 mutanen Zebulun, ƙwararru sojoji shiryayyu don yaƙi da kowane irin makami, suka zo don su taimaki Dawuda da zuciya ɗaya, su 50,000;
Des gens de Zabulon, allant à la guerre et menant le combat avec toute sorte d’armes de guerre: cinquante mille; ils gardaient leurs rangs d’un cœur ferme.
34 mutanen Naftali su 1,000 shugabanni, tare da mutane 37,000 masu riƙe garkuwa da masu;
Des gens de Nephtali: mille chefs, commandant à trente-sept mille hommes, armés de boucliers et de lances.
35 mutanen Dan, shiryayyu don yaƙi, su 28,600;
Des gens de Dan, dressés au combat: vingt-huit mille six cents.
36 mutanen Asher, ƙwararrun sojoji shiryayyu don yaƙi, su 40,000;
Des gens d’Aser allant à la guerre et prenant part aux combats: quarante mille.
37 kuma daga gabashin Urdun, mutanen Ruben, Gad da kuma rabin kabilar Manasse, masu kayan yaƙi iri-iri, su 120,000.
De la Transjordanie, en fait de Rubénites, de Gadites et de gens de la demi-tribu de Manassé, cent vingt mille hommes, armés de toute sorte d’armes de guerre.
38 Dukan waɗannan mayaƙa ne waɗanda suka ba da kansu da yardar rai su yi hidima. Suka zo Hebron da cikakken niyya don su naɗa Dawuda sarki a bisa dukan Isra’ila. Duka sauran Isra’ilawa su ma suka goyi baya a naɗa Dawuda sarki.
Tous ces guerriers, habitués des combats, vinrent avec enthousiasme à Hébron pour proclamer David roi sur tout Israël. Pareillement, tous les autres Israélites étaient unanimes à acclamer David.
39 Mutanen suka yi kwana uku a can tare da Dawuda, suna ci suna sha, gama iyalansu sun yi musu tanadi.
Ils restèrent là avec David, trois jours durant, mangeant et buvant, approvisionnés par leurs frères.
40 Haka ma, maƙwabtansu daga nesa har Issakar, Zebulun da Naftali suka zo suka kawo abinci a kan jakuna, raƙuma, alfadarai da shanu. Akwai tanadin mai yawa na gari, kauɗar ɓaure, nonnan busassun’ya’yan inabi, ruwan inabi, mai, shanu da tumaki. Duk an yi haka don a nuna farin ciki ƙwarai a cikin dukan ƙasar Isra’ila.
De plus, ceux qui demeuraient dans le voisinage, jusqu’à Issachar, Zabulon et Nephtali, leur apportaient des vivres à dos d’ânes, de chameaux, de mulets et de bœufs: aliments de farine, figues, raisins secs, vin, huile, viande de menu et de gros bétail en abondance, car c’était fête en Israël.