< 1 Tarihi 11 >

1 Dukan Isra’ila fa suka taru wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu jiki da jininka ne.
Tout Israël s’assembla et vint auprès de David à Hébron, pour lui dire: "Nous sommes ta chair et ton sang.
2 A dā, ko a lokacin da Shawulu yake sarki, ai, kai ne kake shugabantar Isra’ila a yaƙe-yaƙe. Kuma Ubangiji Allahnka ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayin mutanena Isra’ila, za ka kuma zama mai mulkinsu.’”
Déjà hier, déjà avant-hier, alors que Saül était roi, c’est toi qui dirigeais toutes les expéditions d’Israël. C’Est toi, t’avait dit l’Eternel, ton Dieu, qui gouverneras Israël, mon peuple, toi qui seras son chef."
3 Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, suka yi yarjejjeniya da shi a gaban Ubangiji, suka kuwa shafe Dawuda ya zama sarki a bisa Isra’ila, yadda Ubangiji ya yi alkawari ta wurin Sama’ila.
Tous les Anciens d’Israël vinrent donc trouver le roi à Hébron; le roi David fit un pacte avec eux à Hébron devant l’Eternel, et ils le sacrèrent comme roi d’Israël, selon la parole de l’Eternel à Samuel.
4 Dawuda tare da dukan Isra’ilawa suka taka zuwa Urushalima (wato, Yebus). Yebusiyawan da suke zama a wurin
David et tous les Israélites marchèrent sur Jérusalem, qui s’appelait Jébus. Là étaient les Jébuséens, qui occupaient le pays.
5 suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba.” Duk da haka, Dawuda ya ci kagarar Sihiyona, Birnin Dawuda.
Mais ceux-ci dirent à David: "Tu n’entreras pas ici." Toutefois, David s’empara de la forteresse de Sion, qui est la Cité de David.
6 Dawuda ya ce, “Duk wanda ya jagoranci yaƙi a kan Yebusiyawa zai zama babban shugaban mayaƙa.” Yowab ɗan Zeruhiya ya fara haurawa, ta haka ya zama shugaba.
David avait dit: "Celui qui battra les Jébuséens en premier deviendra chef et prince." Ce fut Joab, fils de Cerouya, qui monta le premier, et il devint chef.
7 Dawuda zauna a kagarar, ta haka aka kira ta Birnin Dawuda.
David s’établit dans la forteresse, qu’on nomma pour cette raison Cité de David.
8 Sai ya gina birni kewaye da shi, daga madogaran gini zuwa katangar da take kewaye, yayinda Yowab ya maido da sauran birnin.
Il ajouta des constructions à la ronde, sur le pourtour du Millo. Quant à Joab, il restaura le reste de la ville.
9 Dawuda kuwa ya ƙara ƙarfi, domin Ubangiji Maɗaukaki yana tare da shi.
David alla grandissant de plus en plus, assisté par l’Eternel-Cebaot.
10 Waɗannan su ne manyan jarumawan Dawuda, su ne, tare da dukan Isra’ila, suka ba wa mulkinsa goyon baya mai ƙarfi da ya kai bisa dukan ƙasar, yadda Ubangiji ya yi alkawari.
Voici les chefs des vaillants guerriers de David, qui l’aidèrent, avec tout Israël, à conquérir le trône et le firent régner selon la parole de l’Eternel, adressée à Israël.
11 Ga jerin sunayen jarumawan Dawuda. Yashobeyam wani ɗan Hakmoni, shi ne babban shugaba; ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe a ƙarawa guda kawai.
Et voici la liste des vaillants guerriers de David: Yachobam, fils de Hakhmoni, chef de la garde. C’Est lui qui, en une seule rencontre, brandit la lance, faisant trois cents cadavres.
12 Biye da shi, shi ne Eleyazar ɗan Dodo mutumin Aho, ɗaya daga cikin jarumawa uku.
Après lui, Eléazar, fils de Dodo, l’Ahohite, l’un des trois héros,
13 Yana tare da Dawuda a Fas Dammim sa’ad da Filistiyawa suka taru can don yaƙi. A wani wuri inda akwai gona cike da sha’ir, sojoji suka gudu daga Filistiyawa.
assista David à Pass-Dammim. Là s’étaient assemblés les Philistins pour la bataille. Il s’y trouvait une pièce de terre pleine d’orge, et le peuple fuyait devant les Philistins.
14 Sai shi da Dawuda suka shiga gonar sha’ir ɗin, suka tsaya ciki don su tsare ta. Suka ragargaza Filistiyawa, Ubangiji kuma ya kawo babban nasara.
Mais lui prit position au milieu du champ, le défendit et battit les Philistins; le Seigneur opéra ainsi une grande délivrance.
15 Wata rana uku cikin manyan mutanen nan talatin suka gangara wurin Dawuda zuwa dutse a kogon Adullam, yayinda ƙungiyar Filistiyawa suke sansani a Kwarin Refayim.
Trois des trente chefs descendirent sur le roc auprès de David, du côté de la caverne d’Adoullam; un corps de Philistins se trouvait campé dans la vallée de Rephaïm.
16 A lokacin Dawuda yana cikin mafaka, sojojin Filistiyawa kuma suna a Betlehem.
David était alors dans la forteresse, et les Philistins avaient une garnison à Bethléem.
17 Dawuda ya ji marmarin ruwan sha sai ya ce, “Kash, a ce wani zai sami mini ruwan sha daga rijiya kusa da ƙofar Betlehem mana!”
David eut un désir et dit: "Ah! si on pouvait me faire boire de l’eau de la citerne qui est à la porte de Bethléem!"
18 Sai Ukun suka kutsa kai cikin sansanin Filistiyawa, suka ja ruwa daga rijiyar da take kusa da ƙofar Betlehem suka ɗauko shi suka kawo wa Dawuda. Amma ya ƙi yă sha; a maimako, sai ya zubar da shi a gaban Ubangiji.
Les trois guerriers s’ouvrirent un passage par le camp des Philistins, puisèrent de l’eau à la citerne qui est à la porte de Bethléem et l’apportèrent à David; mais celui-ci ne voulut pas la boire et en fit une libation à l’Eternel,
19 Ya ce, “Allah yă sawwaƙe in yi haka, ya kamata in sha jinin waɗannan mutanen da suka yi kasai da rayukansu?” Domin sun yi kasai da rayukansu don su dawo da shi, Dawuda bai sha shi ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
en disant: "Mon Dieu me préserve de faire pareille chose! Boirais-je le sang de ces hommes qui ont risqué leur vie, car ils l’ont apportée au péril de leur vie!" Il refusa donc de boire. Voilà ce que firent ces trois guerriers.
20 Abishai ɗan’uwan Yowab shi ma babba ne cikin Ukun nan. Ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe, ya kuma zama sananne kamar Ukun.
Puis Abchaï, frère de Joab, le chef des trois: il brandit un jour sa lance sur trois cents ennemis qu’il immola, et se fit un nom parmi les Trois.
21 Aka ninka girmama shi bisa Ukun, sai ya zama shugaba, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
Il fut plus estimé que les Trente, de la deuxième série, car il devint leur chef, cependant il n’arriva pas jusqu’aux Trois.
22 Benahiya ɗan Yehohiyada shi ma wani barden yaƙi ne daga Kabzeyel, wanda ya yi manyan abubuwa. Ya bugi gwanayen Mowab biyu. Ya kuma gangara zuwa cikin rami a ranar da aka yi dusar ƙanƙara ya kashe zaki.
Puis Benaïa, fils de Joïada, d’un vaillant aux nombreux exploits, originaire de Kabceël; ce fut lui qui triompha des deux Arïel de Moab; ce fut lui aussi qui descendit et tua un lion dans une fosse par un jour de neige.
23 Ya kuma kashe wani mutumin Masar mai tsayi ƙafa bakwai da rabi. Ko da yake mutumin Masar yana da māshi kamar sandan masaƙa a hannunsa, Benahiya ya yaƙe shi da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannun mutumin Masar ya kuma kashe shi da māshin nan nasa.
Il tua aussi un Egyptien, homme de grande taille, haut de cinq coudées, et, dans la main de l’Egyptien, il y avait une lance, grande comme une ensouple de tisserand; il descendit vers lui avec un bâton, arracha la lance de la main de l’Egyptien et le tua avec sa lance.
24 Irin abubuwan da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma sananne ne kamar waɗannan jarumawa uku.
Voilà ce que fit Benaïahou, fils de Joïada, renommé parmi les trois héros.
25 Aka ɗauka shi da bangirma fiye da Talatin nan, amma ba a haɗa shi cikin Ukun ba. Dawuda kuwa ya sa shi yă lura da masu tsaron lafiyarsa.
Il fut plus estimé que les Trente, mais il n’arriva pas jusqu’aux Trois. David l’admit dans son conseil.
26 Jarumawan nan su ne, Asahel ɗan’uwan Yowab, Elhanan ɗan Dodo daga Betlehem,
Puis d’autres héroïques guerriers: Assahel, frère de Joab; Elhanân, fils de Dodo, de Bethléem;
27 Shammot mutumin Haror, Helez mutumin Felon,
Chammot, le Harorite, Hêleç, le Pelonite;
28 Ira ɗan Ikkesh daga Tekowa, Abiyezer daga Anatot,
Ira, fils d’Ikkech, de Tekoa; Abiézer, d’Anatot;
29 Sibbekai mutumin Husha, Ilai mutumin Aho,
Sibbekhaï, le Houchatite; Ilaï, l’Ahohite;
30 Maharai mutumin Netofa, Heled ɗan Ba’ana mutumin Netofa,
Maharaï, de Netofa; Hêled, fils de Baana, de Netofa;
31 Ittai ɗan Ribai daga Gibeya a Benyamin, Benahiya mutumin Firaton,
Itaï, fils de Ribaï, de Ghibea des Benjaminites; Benaïa, de Piratôn
32 Hurai daga kogunan Ga’ash, Abiyel mutumin Arba,
Houraï, de Nahalê-Gaach; Abiël, l’Arbatite;
33 Azmawet mutumin Harum, Eliyaba mutumin Sha’albo,
Azmaveth, le Baharoumite; Elyahba, le Chaalbonite;
34 ’ya’yan Hashem mutumin Gizon maza, Yonatan ɗan Shageye mutumin Harar,
des fils de Hachêm le Ghizonite; Jonathan, fils de Chaghê, le Hararite;
35 Ahiyam ɗan Sakar mutumin Harar, Elifal ɗan Ur,
Ahïâm, fils de Sakhar, le Hararite; Elifal, fils d’Our;
36 Hefer mutumin Mekerat, Ahiya mutumin Felon,
Hêfer, le Mekhératite; Ahiya, le Pelonite;
37 Hezro mutumin Karmel, Na’arai ɗan Ezbai,
Heçro, le Carmélite; Naaraï, fils d’Ezbaï;
38 Yowel ɗan’uwan Natan, Mibhar ɗan Hagiri,
Joël, frère de Nathan; Mibhar, fils du Hagrite;
39 Zelek mutumin Ammon Naharai Baroti, mai ɗaukar kayan yaƙin Yowab ɗan Zeruhiya,
Célek, l’Ammonite; Nahraï, le Bêrotite, écuyer de Joab, fils de Cerouya;
40 Ira mutumin Itra, Gareb mutumin Itra,
Ira, le Yithrite; Garêb, le Yithrite;
41 Uriya mutumin Hitti Zabad ɗan Alai,
Urie, le Héthéen; Zabad, fils d’Ahlaï;
42 Adina ɗan Shiza mutumin Ruben, wanda shi ne babba na mutanen Ruben, kuma talatin suna tare da shi,
Adina, fils de Chiza, le Rubénite, chef rubénite, commandant à trente;
43 Hanan ɗan Ma’aka, Yoshafat mutumin Mit,
Hanân, fils de Maakha; Josaphat, le Mitnite;
44 Uzziya mutumin Ashtarot, Shama da Yehiyel’ya’yan Hotam mutumin Arower maza,
Ouzzia, l’Achteratite; Chama et Yeïêl, fils de Hotam, d’Aroër;
45 Yediyayel ɗan Shimri, ɗan’uwansa Yoha mutumin Tiz,
Yedïaêl, fils de Chimri; Yoha, son frère, le Tiçite;
46 Eliyel mutumin Ma’aha, Yeribai da Yoshawiya’ya’yan Elna’am maza, Itma mutumin Mowab,
Eliël, de Mahavïm; Yeribaï et Yochavia, fils d’Elnaam; Yitma, le Moabite;
47 Eliyel, Obed da Ya’asiyel mutumin Mezob.
Eliël, Obed et Yaassïêl, de Meçobaïa.

< 1 Tarihi 11 >