< Psalm 48 >

1 Ein Psalmlied der Kinder Korah. Groß ist der HERR und hochberühmt in der Stadt unsers Gottes, auf seinem heiligen Berge.
Waƙa ce. Zabura ta’ya’yan Kora maza. Ubangiji mai girma ne, kuma mafificin yabo, a birnin Allahnmu, dutsensa mai tsarki.
2 Schön ragt empor der Berg Zion, des sich das ganze Land tröstet; an der Seite gegen Mitternacht liegt die Stadt des großen Königs.
Kyakkyawa ce cikin tsayinta, abin farin cikin dukan duniya. Kamar ƙwanƙoli mafi tsayi na Zafon ne Dutsen Sihiyona, birnin Babban Sarki.
3 Gott ist in ihren Palästen bekannt, daß er der Schutz sei.
Allah yana cikin fadodinta; ya nuna kansa mafaka ce gare ta.
4 Denn siehe, Könige waren versammelt und sind miteinander vorübergezogen.
Sa’ad da sarakuna suka haɗa rundunoni, sa’ad da suka yi gaba tare,
5 Sie haben sich verwundert, da sie solches sahen; sie haben sich entsetzt und sind davon gestürzt.
sun gan ta suka kuwa yi mamaki; suka gudu don tsoro.
6 Zittern ist sie daselbst angekommen, Angst wie eine Gebärerin.
Rawar jiki ya kama su a can, zafi kamar na mace mai naƙuda.
7 Du zerbrichst die Schiffe im Meer durch den Ostwind.
Ka hallaka su kamar jiragen ruwan Tarshish da iskar gabas ta wargaje.
8 Wie wir gehört haben, so sehen wir's an der Stadt des HERRN Zebaoth, an der Stadt unsers Gottes; Gott erhält sie ewiglich. (Sela)
Yadda muka ji, haka muka gani a cikin birnin Ubangiji Maɗaukaki, a cikin birnin Allahnmu. Allah ya sa ta zauna lafiya har abada. (Sela)
9 Gott, wir gedenken deiner Güte in deinem Tempel.
Cikin haikalinka, ya Allah, mun yi tunani a kan ƙaunarka marar ƙarewa.
10 Gott, wie dein Name, so ist auch dein Ruhm bis an der Welt Enden; deine Rechte ist voll Gerechtigkeit.
Kamar sunanka, ya Allah, yabonka ya kai iyakokin duniya; hannunka na dama ya cika da adalci.
11 Es freue sich der Berg Zion, und die Töchter Juda's seien fröhlich um deiner Gerichte willen.
Dutsen Sihiyona ya yi farin ciki, ƙauyukan Yahuda suna murna saboda hukuntanka.
12 Machet euch um Zion und umfanget sie, zählet ihre Türme;
Yi tafiya cikin Sihiyona, ku kewaye ta, ku ƙirga hasumiyoyinta,
13 achtet mit Fleiß auf ihre Mauern, durchwandelt ihre Paläste, auf daß ihr davon verkündiget den Nachkommen,
ku lura da katangarta da kyau, ku dubi fadodinta, don ku faɗe su ga tsara mai zuwa.
14 daß dieser Gott sei unser Gott immer und ewiglich. Er führt uns wie die Jugend.
Gama wannan Allah shi ne Allahnmu har abada abadin; zai zama jagorarmu har zuwa ƙarshe.

< Psalm 48 >