< Psalm 55 >
1 Eine Unterweisung Davids, vorzusingen auf Saitenspielen. Gott, höre mein Gebet und verbirg dich nicht vor meinem Flehen.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Ka ji addu’ata, ya Allah, kada ka ƙyale roƙona;
2 Merke auf mich und erhöre mich, wie ich so kläglich zage und heule,
ka ji ni ka kuma amsa mini. Tunanina yana damuna na kuma gaji tilis
3 daß der Feind so schreiet, und der Gottlose dränget; denn sie wollen mir einen Tück beweisen und sind mir heftig gram.
hankalina ya tashi saboda yawan surutan masu ƙina, saboda danniyar mugaye. Gama sukan jawo mini wahala, suna jin haushina suna ƙina.
4 Mein Herz ängstet sich in meinem Leibe, und des Todes Furcht ist auf mich gefallen.
Zuciyata tana wahala a cikina; tsorace-tsoracen mutuwa sun sha kaina.
5 Furcht und Zittern ist mich ankommen, und Grauen hat mich überfallen.
Tsoro da rawan jiki sun kama ni; razana ta sha kaina.
6 Ich sprach: O, hätte ich Flügel wie Tauben, daß ich flöge und etwa bliebe!
Na ce, “Kash, da a ce ina da fikafikan kurciya mana! Ai, da na yi firiya na tafi na huta,
7 Siehe, so wollt ich mich ferne weg machen und in der Wüste bleiben. (Sela)
da na tafi can da nisa na zauna a hamada; (Sela)
8 Ich wollt eilen, daß ich entrönne vor dem Sturmwind und Wetter.
da na hanzarta na tafi wurin mafakata, nesa da muguwar iska da hadiri.”
9 Mache ihre Zunge uneins, HERR, und laß sie untergehen; denn ich sehe Frevel und Hader in der Stadt.
Ka rikitar da mugaye, ya Ubangiji, ka birkitar da maganarsu, gama na ga rikici da faɗa a cikin birni.
10 Solches gehet Tag und Nacht um und um in ihren Mauern; es ist Mühe und Arbeit drinnen.
Dare da rana suna yawo a kan katanga; mugun hali da zargi suna a cikinta.
11 Schadentun regieret drinnen, Lügen und Trügen läßt nicht von ihrer Gasse.
Rundunar hallaka suna aiki a cikin birni; barazana da ƙarairayi ba sa taɓa barin titunanta.
12 Wenn mich doch mein Feind schändete, wollt ich's leiden, und wenn mir mein Hasser pochte, wollt ich mich vor ihm verbergen;
Da a ce abokin gāba ne ke zagina, da na jure da shi; da a ce maƙiyi yana tā da kansa a kaina, da na ɓoye daga gare shi.
13 du aber bist mein Geselle, mein Pfleger und mein Verwandter,
Amma kai ne, mutum kamar ni, abokina, abokina na kurkusa,
14 die wir freundlich miteinander waren unter uns; wir wandelten im Hause Gottes zu Haufen.
wanda na taɓa jin daɗin zumunci da shi sosai yayinda muke tafiya tare a taron jama’a a gidan Allah.
15 Der Tod übereile sie, und müssen lebendig in die Hölle fahren; denn es ist eitel Bosheit unter ihrem Haufen. (Sheol )
Bari mutuwa ta ɗauki abokan gābana ba labari; bari su gangara da rai zuwa cikin kabari, gama mugunta tana samun masauƙi a cikinsu. (Sheol )
16 Ich aber will zu Gott rufen, und der HERR wird mir helfen.
Amma na kira ga Allah, Ubangiji kuwa ya cece ni.
17 Des Abends, Morgens und Mittags will ich klagen und heulen, so wird er meine Stimme hören.
Safe, rana da yamma ina kuka da nishi, yakan kuwa ji muryata.
18 Er erlöset meine Seele von denen, die an mich wollen, und schaffet ihr Ruhe; denn ihrer ist viel wider mich.
Yakan fisshe ni lafiya daga yaƙin da ake yi da ni, ko da yake da yawa suna gāba da ni.
19 Gott wird hören und sie demütigen, der allwege bleibt. (Sela) Denn sie werden nicht anders und fürchten Gott nicht.
Allah, yana mulki har abada, zai ji su yă kuma azabtar da su, (Sela) mutanen da ba sa taɓa canja hanyoyinsu kuma ba sa tsoron Allah.
20 Denn sie legen ihre Hände an seine Friedsamen und entheiligen seinen Bund.
Abokina ya kai wa abokansa hari; ya tā da alkawarinsa.
21 Ihr Mund ist glätter denn Butter und haben doch Krieg im Sinn; ihre Worte sind gelinder denn Öl und sind doch bloße Schwerter.
Maganarsa tana da laushi kamar man zaitun, duk da haka yaƙi yana a cikin zuciyarsa; kalmominsa sun fi mai sulɓi, duk da haka takuba ne zārarru.
22 Wirf dein Anliegen auf den HERRN! Der wird dich versorgen und wird den Gerechten nicht ewiglich in Unruhe lassen.
Ku kawo damuwoyinku ga Ubangiji zai kuwa riƙe ku; ba zai taɓa barin mai adalci yă fāɗi ba.
Amma kai, ya Allah, za ka kawar da mugaye zuwa cikin ramin lalacewa; masu kisa da mutane masu ruɗu ba za su kai rabin kwanakin rayuwarsu ba. Amma ni dai, na dogara gare ka.