< Psalm 106 >

1 Halleluja! Danket dem HERRN; denn er ist freundlich, und seine Güte währet ewiglich.
Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 Wer kann die großen Taten des HERRN ausreden und alle seine löblichen Werke preisen?
Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
3 Wohl denen, die das Gebot halten und tun immerdar recht!
Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
4 HERR, gedenke mein nach der Gnade, die du deinem Volk verheißen hast; beweise uns deine Hilfe,
Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
5 daß wir sehen mögen die Wohlfahrt deiner Auserwählten und uns freuen, daß es deinem Volk wohlgehet, und uns rühmen mit deinem Erbteil.
don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
6 Wir haben gesündiget samt unsern Vätern; wir haben mißgehandelt und sind gottlos gewesen.
Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
7 Unsere Väter in Ägypten wollten deine Wunder nicht verstehen; sie gedachten nicht an deine große Güte und waren ungehorsam am Meer, nämlich am Schilfmeer.
Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
8 Er half ihnen aber um seines Namens willen, daß er seine Macht beweisete.
Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
9 Und er schalt das Schilfmeer, da ward's trocken; und führete sie durch die Tiefe wie in einer Wüste;
Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
10 und half ihnen von der Hand des, der, sie hassete, und erlösete sie von der Hand des Feindes
Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
11 Und die Wasser ersäuften ihre Widersacher, daß nicht einer überblieb.
Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
12 Da glaubten sie an seine Worte und sangen sein Lob.
Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
13 Aber sie vergaßen bald seiner Werke; sie warteten nicht seines Rats.
Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
14 Und sie wurden lüstern in der Wüste und versuchten Gott in der Einöde.
A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
15 Er aber gab ihnen ihre Bitte und sandte ihnen genug, bis ihnen davor ekelte.
Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
16 Und sie empörten sich wider Mose im Lager, wider Aaron, den Heiligen des HERRN.
A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
17 Die Erde tat sich auf und verschlang Dathan und deckte zu die Rotte Abirams.
Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
18 Und Feuer ward unter ihrer Rotte angezündet; die Flamme verbrannte die Gottlosen.
Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
19 Sie machten ein Kalb in Horeb und beteten an das gegossene Bild;
A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
20 und verwandelten ihre Ehre in ein Gleichnis eines Ochsen, der Gras isset.
Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
21 Sie vergaßen Gottes, ihres Heilandes, der so große Dinge in Ägypten getan hatte,
Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
22 Wunder im Lande Hams und schreckliche Werke am Schilfmeer.
mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
23 Und er sprach, er wollte sie vertilgen, wo nicht Mose, sein Auserwählter, den Riß aufgehalten hätte, seinen Grimm abzuwenden, auf daß er sie nicht gar verderbete.
Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
24 Und sie verachteten das liebe Land; sie glaubten seinem Wort nicht
Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
25 und murreten in ihren Hütten; sie gehorchten der Stimme des HERRN nicht.
Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
26 Und er hub auf seine Hand wider sie, daß er sie niederschlüge in der Wüste
Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
27 und würfe ihren Samen unter die Heiden und streuete sie in die Länder.
ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
28 Und sie hingen sich an den Baal Peor und aßen von den Opfern der toten Götzen
Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
29 und erzürneten ihn mit ihrem Tun; da riß auch die Plage unter sie.
suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
30 Da trat zu Pinehas und schlichtete die Sache; da ward der Plage gesteuert,
Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
31 und ward ihm gerechnet zur Gerechtigkeit für und für ewiglich.
An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
32 Und sie erzürneten ihn am Haderwasser; und sie zerplagten den Mose übel.
A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
33 Denn sie betrübten ihm sein Herz, daß ihm etliche Worte entfuhren.
saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
34 Auch vertilgten sie die Völker nicht, wie sie doch der HERR geheißen hatte,
Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
35 sondern sie mengeten sich unter die Heiden und lernten derselben Werke
amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
36 und dieneten ihren Götzen, die gerieten ihnen zum Ärgernis.
Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
37 Und sie opferten ihre Söhne und ihre Töchter den Teufeln
Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
38 und vergossen unschuldig Blut, das Blut ihrer Söhne und ihrer Töchter, die sie opferten den Götzen Kanaans, daß das Land mit Blutschulden befleckt ward;
Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
39 und verunreinigten sich mit ihren Werken und hureten mit ihrem Tun.
Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
40 Da ergrimmete der Zorn des HERRN über sein Volk und gewann einen Greuel an seinem Erbe
Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
41 und gab sie in die Hand der Heiden, daß über sie herrscheten, die ihnen gram waren.
Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
42 Und ihre Feinde ängsteten sie; und wurden gedemütiget unter ihre Hände.
Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
43 Er errettete sie oftmals; aber sie erzürneten ihn mit ihrem Vornehmen und wurden wenig um ihrer Missetat willen.
Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
44 Und er sah ihre Not an, da er ihre Klage hörete,
Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
45 und gedachte an seinen Bund, mit ihnen gemacht. Und reuete ihn nach seiner großen Güte
saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
46 und ließ sie zur Barmherzigkeit kommen vor allen, die sie gefangen hatten.
Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
47 Hilf uns, HERR, unser Gott, und bringe uns zusammen aus den Heiden, daß wir danken deinem heiligen Namen und rühmen dein Lob!
Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
48 Gelobet sei der HERR, der Gott Israels, von Ewigkeit zu Ewigkeit, und alles Volk spreche: Amen, Halleluja!
Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.

< Psalm 106 >