< Psalm 115 >

1 Nicht uns, nicht uns, nein, Deinem Namen gib die Ehre, Herr, und Deiner Huld und Deiner Treue!
Ba gare mu ba, ya Ubangiji, ba gare mu ba amma ga sunanka yă sami ɗaukaka, saboda ƙaunarka da amincinka.
2 Was sollten schon die Heiden sagen: "Wo ist ihr Gott?"
Me ya sa al’ummai suke cewa, “Ina Allahnsu?”
3 Im Himmel ist er, unser Gott, der alles, was er will, vollbringt. -
Allahnmu yana a sama; yana yin duk abin da ya ga dama.
4 Doch ihre Götzen sind von Gold und Silber, ein Werk von Menschenhänden.
Amma gumakansu azurfa da zinariya ne, da hannuwan mutane suka yi.
5 Sie haben einen Mund und reden nicht; Sie haben Augen, doch sie sehen nicht.
Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
6 Nicht hören sie mit ihren Ohren; nicht riechen sie mit ihrer Nase.
suna da kunnuwa, amma ba sa ji, hanci, amma ba sa jin ƙanshi
7 Nicht tasten sie mit ihren Händen; nicht gehen sie mit ihren Füßen; sie bringen keinen Laut aus ihrer Kehle.
suna da hannuwa, amma ba sa iya taɓa kome, ƙafafu, amma ba sa iya tafiya; ba sa iya ce wani abu da maƙogwaronsu.
8 Wie sie, so werden ihre Schöpfer und alle, die auf sie vertrauen. -
Masu yinsu za su zama kamar su, haka kuma zai kasance da duk wanda ya dogara da su.
9 Hat aber Israel fest auf den Herrn gebaut, dann ist er ihm ein Schutz und Schild.
Ya gidan Isra’ila, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
10 Baut Aarons Haus fest auf den Herrn, dann ist er ihnen Schutz und Schild.
Ya gidan Haruna, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
11 Und bauen, die den Herren fürchten, auf den Herrn, dann ist er ihnen Schutz und Schild.
Ku da kuke tsoronsa, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
12 So segne unsern Fortbestand der Herr! Er segne das Haus Israel! Er segne Aarons Haus!
Ubangiji yakan tuna da mu zai kuma albarkace mu. Zai albarkace gidan Isra’ila, zai albarkace gidan Haruna,
13 Er segne, die den Herren fürchten, die Kleinen mit den Großen!
zai albarkace waɗanda suke tsoron Ubangiji, manya da ƙanana duka.
14 Der Herr vermehre euch, euch selbst und eure Kinder!
Bari Ubangiji yă sa ku ƙaru, da ku da’ya’yanku.
15 So seid gesegnet von dem Herrn, dem Schöpfer Himmels und der Erde! -
Bari Ubangiji yă albarkace ku, shi Mahalicci sama da ƙasa.
16 Der Himmel ist ein Himmel für den Herrn; die Erde nur gibt er den Menschenkindern.
Saman sammai na Ubangiji ne, amma ya ba da duniya ga mutum.
17 Die Toten loben nicht den Herrn, nicht die ins stille Reich Gesunkenen.
Ba matattu ba ne masu yabon Ubangiji, waɗanda suke gangara zuwa wurin da ake shiru;
18 Dagegen wollen wir den Herrn lobpreisen von nun an bis in Ewigkeit. Alleluja!
mu ne masu ɗaukaka Ubangiji, yanzu da har abada kuma. Yabi Ubangiji.

< Psalm 115 >