< Juges 4 >
1 Et les enfants d’Israël recommencèrent à faire le mal en la présence du Seigneur après la mort d’Aod,
Bayan rasuwar Ehud, Isra’ilawa suka sāke aikata mugayen ayyuka a gaban Ubangiji.
2 Et le Seigneur les livra aux mains de Jabin, roi de Chanaan, qui régna dans Asor; or, il avait pour général de son armée un homme du nom de Sisara; et lui-même habitait à Haroseth des nations.
Saboda haka Ubangiji ya sayar da su ga Yabin sarkin Kan’ana wanda yake mulki a Hazor. Shugaban mayaƙansa shi ne Sisera, wanda yake zaune a Haroshet Haggoyim.
3 Et les enfants d’Israël crièrent au Seigneur; car Jabin avait neuf cents chars armés de faux; et pendant vingt ans il les avait violemment opprimés.
Domin Yabin sarkin Kan’ana yana da kekunan yaƙin ƙarfe ɗari tara, ya ji wa Isra’ilawa ƙwarai har shekara ashirin, sai suka yi kuka ga Ubangiji, don taimako.
4 Or, c’était Debbora, prophétesse, femme de Lapidoth, laquelle jugeait le peuple en ce temps-là.
A lokacin Debora annabiya, matar Laffidot ce take bi da Isra’ila.
5 Et elle s’asseyait sous un palmier, qui était appelé de son nom, entre Rama et Béthel sur la montagne d’Ephraïm; et les enfants d’Israël montaient vers elle, pour tous les jugements.
Takan yi zaman shari’a a ƙarƙashin Dabinon Debora tsakanin Rama da Betel, a ƙasar tudu ta Efraim, Isra’ilawa kuwa sukan zo wurinta don tă yi musu shari’a.
6 Elle envoya et appela Barac, fils d’Abinoem de Cédés de Nephthali, et elle lui dit: Le Seigneur Dieu d’Israël te l’ordonne, va, et conduis l’armée sur la montagne de Thabor, et tu prendras avec toi dix mille combattants des enfants de Nephthali et des enfants de Zabulon:
Sai ta aika a kira mata Barak ɗan Abinowam daga Kedesh a Naftali, ta ce masa, “Ubangiji, Allah na Isra’ila ya umarce ka, ‘Je ka, ka ɗauki mutane Naftali da na Zebulun dubu goma tare da kai, ka yi jagoransu zuwa Dutse Tabor.
7 Or moi-même je t’amènerai à l’endroit du torrent de Cison, Sisara, prince de l’armée de Jabin, ses chars et toute sa multitude, et je les livrerai en ta main.
Zan jawo Sisera, shugaban mayaƙan Yabin, da keken yaƙinsa da mayaƙansa zuwa Kogin Kishon in ba da su a hannunku.’”
8 Et Barac lui répondit: Si vous venez avec moi, j’irai; si vous ne voulez pas venir avec moi, je n’irai pas.
Barak ya ce, “In kika tafi tare da ni, zan tafi; amma in ba ki zo tare da ni ba, ba zan tafi ba.”
9 Debbora lui repartit: J’irai assurément avec toi; mais pour cette fois la victoire ne te sera point attribuée, parce que c’est dans la main d’une femme que sera livré Sisara. C’est pourquoi Debbora se leva et s’en alla avec Barac à Cédés.
Debora ta ce, “To, shi ke nan, zan tafi tare da kai. Amma saboda yadda ka ɗauki wannan batun, darajar ba za tă zama taka ba, gama Ubangiji zai ba da Sisera a hannun mace.” Saboda haka Debora ta tafi tare da Barak zuwa Kedesh,
10 Barac, ayant mandé Zabulon et Nephthali, monta avec dix mille combattants, accompagné de Debbora.
a can Barak ya kira Zebulun da Naftali. Mutum dubu goma suka kuma bi shi, Debora kuma tana tare da shi.
11 Or Haber le Cinéen s’était retiré depuis longtemps de tous ses autres frères, les Cinéens, fils d’Hobab, parent de Moïse, et il avait tendu ses tabernacles jusqu’à la vallée qui est appelée Sennim, et qui était près de Cédés.
To, Heber Bakene ya riga ya bar Keniyawa, zuriyar Hobab, ɗan’uwan matar Musa, ya kafa tentinsa wajen babban itace a Za’anannim kusa da Kedesh.
12 Et l’on annonça à Sisara, que Barac, fils d’Abinoem, était monté sur la montagne de Thabor.
Sa’ad da aka gaya wa Sisera cewa Barak ɗan Abinowam ya haura zuwa dutsen Tabor,
13 Et il assembla ses neuf cents chars armés de faux, et toute son armée qui vint de Haroseth des nations au torrent de Cison.
sai Sisera ya tattara keken yaƙinsa na ƙarfe ɗari tara wuri ɗaya da dukan mutanen da suke tare da shi daga Haroshet Haggoyim zuwa Kogin Kishon.
14 Alors Debbora dit à Barac: Lève-toi; car c’est le jour auquel le Seigneur a livré Sisara en tes mains: voilà que lui-même est ton guide. C’est pourquoi Barac descendit de la montagne de Thabor, et dix mille combattants avec lui.
Sa’an nan Debora ta ce wa Barak, “Je ka! Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya ba da Sisera a hannunka. Ba Ubangiji ya riga ya sha gabanka?” Saboda haka Barak ya gangara zuwa Dutsen Tabor, da mutum dubu goma biye da shi.
15 Et le Seigneur épouvanta Sisara, tous ses chars et toute sa multitude, par le tranchant du glaive, à l’aspect de Barac; de telle sorte que Sisara s’élançant de son char, s’enfuit à pied,
Da matsowar Barak, Ubangiji ya murƙushe Sisera da dukan sarakunansa da mayaƙansa da takobi, Sisera kuwa ya gudu da ƙafa ya bar keken yaƙinsa.
16 Que Barac poursuivit les chars qui s’enfuyaient et l’armée, jusqu’à Haroseth des nations, et que toute la multitude des ennemis périt jusqu’à une entière extermination.
Amma Barak ya bi keken yaƙin da mayaƙan har Haroshet Haggoyim. Aka karkashe dukan mayaƙan Sisera ba ko ɗayan da ya tsira.
17 Mais Sisara fuyant parvint à la tente de Jahel, femme d’Haber le Cinéen. Car il y avait paix entre Jabin, roi d’Azor, et la maison d’Haber le Cinéen.
Amma Sisera, ya tsere da ƙafa zuwa tentin Yayel, matar Heber Bakene, domin suna da abokantaka da Yabin sarkin Hazor da kuma kabilar Heber Bakene.
18 Jahel étant donc sorti au devant à la rencontre de Sisara, lui dit: Entre chez moi, mon seigneur; entre, et ne crains point. Sisara entré dans son tabernacle, et couvert par elle, de son manteau,
Yayel ta fito ta taryi Sisera ta ce masa, “Ranka yă daɗe, ka shigo, ka shigo ciki. Kada ka ji tsoro.” Saboda haka ya shiga cikin tentinta, sai ta rufe shi da bargo.
19 Lui dit: Donnez-moi, je vous prie, un peu d’eau, parce que j’ai une grande soif. Jahel ouvrit l’outre du lait, lui donna à boire et le couvrit.
Sai ya ce, “Ina roƙonki, ki ba ni ruwa in sha, ina jin ƙishirwa.” Sai ta buɗe salkar madara, ta ba shi ya sha, sai ta kuma rufe shi.
20 Alors Sisara lui dit: Tenez-vous devant la porte de votre tabernacle; et lorsque quelqu’un viendra, vous interrogeant, et disant: Est-ce qu’il n’y a point ici quelqu’un? Vous répondrez: Il n’y a personne.
Ya ce mata, “Ki tsaya a ƙofar tenti, in wani ya zo ya tambaye ki, ‘Akwai wani a nan?’ Ki ce masa ‘a’a.’”
21 C’est pourquoi, Jahel, femme d’Haber prit le clou du tabernacle, prenant également le marteau; et étant entrée secrètement et en silence, elle posa le clou sur la tempe de sa tête, et après l’avoir frappé avec le marteau, elle lui enfonça dans le cerveau jusqu’à terre: et Sisara joignant le sommeil à la mort défaillit et mourut.
Amma Yayel, matar Heber, ta ɗauki turken tenti da guduma ta tafi wurinsa da sauri sa’ad da yake barci saboda gajiya. Ta kafa masa turken a gindin kunnensa ta haɗa shi da ƙasa, har ya mutu.
22 Et voilà que Barac, poursuivant Sisara, arrivait; et Jahel étant sortie à sa rencontre, lui dit: Viens, et je te montrerai l’homme que tu cherches. Lorsque celui-ci fut entré chez elle, il vit Sisara étendu mort, et le clou enfoncé dans sa tempe.
Sai ga Barak mai bin sawun Sisera, Yayel kuwa ta fito don marabtarsa, ta ce, “Shigo, zan nuna maka mutumin da kake nema.” Saboda haka ya shiga ciki tare da ita, sai ga Sisera kwance da turken a gindin kunnensa, matacce.
23 Dieu humilia donc en ce jour-là Jabin, roi de Chanaan, devant les enfants d’Israël,
A ranar Allah ya yi kaca-kaca da Yabin, sarkin Kan’ana a gaban Isra’ila.
24 Qui croissaient tous les jours, et qui d’une main forte opprimaient Jabin, roi de Chanaan, jusqu’à ce qu’ils l’eurent entièrement détruit.
Isra’ilawa kuwa suka ƙara ƙarfi gāba da Yabin, sarkin Kan’aniyawa, har suka hallaka shi.